< Süleyman'In Özdeyişleri 15 >
1 Yumuşak yanıt gazabı yatıştırır, Oysa yaralayıcı söz öfkeyi alevlendirir.
Amsa da tattausar harshe kan kwantar da fushi, amma magana da kakkausan harshe kan kuta fushi.
2 Bilgenin dili bilgiyi iyi kullanır, Akılsızın ağzındansa ahmaklık akar.
Harshen mai hikima kan yi zance mai kyau a kan sani, amma bakin wawa kan fitar da wauta.
3 RAB'bin gözü her yerde olanı görür, Kötüleri de iyileri de gözler.
Idanun Ubangiji suna a ko’ina, suna lura da masu aikata mugunta da masu aikata alheri.
4 Okşayıcı dil yaşam verir, Çarpık dilse ruhu yaralar.
Harshen da ya kawo warkarwa shi ne itacen rai, amma harshe mai ƙarya kan ragargaza zuciya.
5 Ahmak babasının uyarılarını küçümser, İhtiyatlı kişi azara kulak verir.
Wawa yakan ƙi kulawa da horon da mahaifinsa yake masa, amma duk wanda ya yarda da gyara kan nuna azanci.
6 Doğru kişinin evi büyük hazine gibidir, Kötünün geliriyse sıkıntı kaynağıdır.
Gidan adali yana da dukiya mai yawa, amma albashin mugaye kan kawo musu wahala.
7 Bilgelerin dudakları bilgi yayar, Ama akılsızların yüreği öyle değildir.
Leɓunan masu hikima sukan baza sani; ba haka zukatan wawaye suke ba.
8 RAB kötülerin kurbanından iğrenir, Ama doğruların duası O'nu hoşnut eder.
Ubangiji yana ƙyamar hadayar mugaye, amma addu’ar masu aikata gaskiya kan sa ya ji daɗi.
9 RAB kötü kişinin yolundan iğrenir, Doğruluğun ardından gideni sever.
Ubangiji yana ƙin hanyar mugaye amma yana ƙaunar waɗanda suke neman adalci.
10 Yoldan sapan şiddetle cezalandırılır Ve azarlanmaktan nefret eden ölüme gider.
Horo mai tsanani yana jiran duk wanda ya bar hanya; wanda ya ƙi gyara zai mutu.
11 RAB, ölüm ve yıkım diyarında olup biteni bilir, Nerde kaldı ki insanın yüreği! (Sheol )
Mutuwa da Hallaka suna nan a fili a gaban Ubangiji, balle fa zukatan mutane! (Sheol )
12 Alaycı kişi azarlanmaktan hoşlanmaz, Bilgelere gidip danışmaz.
Mai yin ba’a yakan ƙi gyara; ba zai nemi shawara mai hikima ba.
13 Mutlu yürek yüzü neşelendirir, Acılı yürek ruhu ezer.
Zuciya mai farin ciki kan sa fuska tă yi haske, amma ciwon zuciya kan ragargaza rai.
14 Akıllı yürek bilgi arar, Akılsızın ağzıysa ahmaklıkla beslenir.
Zuciya mai la’akari kan nemi sani, amma bakin wawa wauta ce ke ciyar da shi.
15 Mazlumun bütün günleri sıkıntı doludur, Mutlu bir yürekse sahibine sürekli ziyafettir.
Dukan kwanakin mutumin da ake danniya fama yake yi, amma zuciya mai farin ciki yana yin biki kullum.
16 Yoksul olup RAB'den korkmak, Zengin olup kaygı içinde yaşamaktan yeğdir.
Gara a kasance da kaɗan da tsoron Ubangiji da a kasance da arziki mai yawa game da wahala.
17 Sevgi dolu bir ortamdaki sebze yemeği, Nefret dolu bir ortamdaki besili danadan yeğdir.
Gara a ci abincin kayan ganye inda akwai ƙauna da a ci kiwotaccen saniya inda ƙiyayya take.
18 Huysuz kişi çekişme yaratır, Sabırlı kişi kavgayı yatıştırır.
Mutum mai zafin rai kan kawo faɗa, amma mutum mai haƙuri kan kwantar da faɗa.
19 Tembelin yolu dikenli çit gibidir, Doğrunun yoluysa ana caddeye benzer.
An tare hanyar rago da ƙayayyuwa, amma hanyar mai aikata gaskiya buɗaɗɗiyar hanya ce.
20 Bilge çocuk babasını sevindirir, Akılsız çocuksa annesini küçümser.
Ɗa mai hikima kan kawo farin ciki wa mahaifinsa, amma wawa yakan rena mahaifiyarsa.
21 Sağduyudan yoksun kişi ahmaklığıyla sevinir, Ama akıllı insan dürüst bir yaşam sürer.
Wauta kan sa mutum marar azanci ya yi farin ciki, amma mai basira kan kiyaye abin da yake yi daidai.
22 Karşılıklı danışılmazsa tasarılar boşa çıkar, Danışmanların çokluğuyla başarıya ulaşılır.
Shirye-shirye sukan lalace saboda rashin neman shawara, amma tare da mashawarta masu yawa za su yi nasara.
23 Uygun yanıt sahibini mutlu eder, Yerinde söylenen söz ne güzeldir!
Mutum yakan yi farin ciki a ba da amsar da take daidai, kuma ina misali a yi magana a lokacin da ya dace!
24 Sağduyulu kişi yukarıya, yaşama giden yoldadır, Bu da ölüler diyarına inmesini önler. (Sheol )
Hanyar rai na yin jagora ya haura wa masu hikima don ta kiyaye shi daga gangarawa zuwa kabari. (Sheol )
25 RAB kibirlinin evini yıkar, Dul kadının sınırını korur.
Ubangiji yakan rushe gidan mai girman kai amma yakan kiyaye iyakokin gwauruwa daidai.
26 RAB kötünün tasarılarından iğrenir, Temiz düşüncelerden hoşnut kalır.
Ubangiji yana ƙyamar tunanin mugaye, amma waɗanda suke da tunani masu tsabta yakan ji daɗinsu.
27 Kazanca düşkün kişi kendi evine sıkıntı verir, Rüşvetten nefret edense rahat yaşar.
Mutum mai haɗama kan kawo wahala ga iyalinsa, amma wanda yake ƙin cin hanci zai rayu.
28 Doğru kişinin aklı yanıtını iyi tartar, Kötünün ağzı kötülük saçar.
Zuciyar mai adalci takan auna amsoshinta, amma bakin mugu yakan fitar da mugunta.
29 RAB kötülerden uzak durur, Oysa doğruların duasını duyar.
Ubangiji yana nesa da mugaye amma yakan ji addu’ar adalai.
30 Gülen gözler yüreği sevindirir, İyi haber bedeni ferahlatır.
Fuska mai fara’a takan kawo farin ciki ga zuciya, kuma labari mai daɗi na kawo lafiya ga ƙasusuwa.
31 Yaşam veren uyarıları dinleyen, Bilgeler arasında konaklar.
Duk wanda ya mai da hankali sa’ad da ake tsawata masa ba zai kasance dabam a cikin masu hikima ba.
32 Terbiyeden kaçan kendine zarar verir, Azara kulak verense sağduyu kazanır.
Duk waɗanda suka ƙi horon sun rena kansu ke nan, amma duk waɗanda sun yarda da gyara sukan ƙara basira.
33 RAB korkusu bilgelik öğretir, Alçakgönüllülük de onurun önkoşuludur.
Tsoron Ubangiji yakan koya wa mutum hikima, kuma sauƙinkai kan zo kafin girmamawa.