< Çölde Sayim 21 >
1 Negev'de yaşayan Kenanlı Arat Kralı, İsrailliler'in Atarim yolundan geldiğini duyunca, onlara saldırarak bazılarını tutsak aldı.
Sa’ad da sarkin Arad, mutumin Kan’ana, wanda yake zaune a Negeb, da ya ji cewa Isra’ila yana zuwa ta hanyar Atarim, sai ya fito, yă yaƙi Isra’ilawa, yă kuma kama waɗansunsu.
2 Bunun üzerine İsrailliler, “Eğer bu halkı tümüyle elimize teslim edersen, kentlerini büsbütün yok edeceğiz” diyerek RAB'be adak adadılar.
Sai Isra’ila suka yi alkawari wa Ubangiji suka ce, “In ka ba da waɗannan mutane a hannunmu, za mu hallaka dukan garuruwansu ƙaf.”
3 RAB İsrailliler'in yalvarışını işitti ve Kenanlılar'ı ellerine teslim etti. İsrailliler onları da kentlerini de büsbütün yok ettiler. Oraya Horma adı verildi.
Ubangiji kuwa ya saurari kukan Isra’ila, ya kuma ba da Kan’aniyawa a gare su. Suka hallaka su da biranensu ƙaf; saboda haka aka sa wa wurin suna Horma.
4 Edom ülkesinin çevresinden geçmek için Kamış Denizi yoluyla Hor Dağı'ndan ayrıldılar. Ama yolda halk sabırsızlandı.
Suka kama hanya daga Dutsen Hor ta hanya zuwa Jan Teku, don su kauce wa Edom. Amma mutane suka rasa haƙuri a hanya;
5 Tanrı'dan ve Musa'dan yakınarak, “Çölde ölelim diye mi bizi Mısır'dan çıkardınız?” dediler, “Burada ne ekmek var, ne de su. Ayrıca bu iğrenç yiyecekten de tiksiniyoruz!”
suka yi wa Allah da Musa gunaguni, suka ce, “Me ya sa kuka fitar da mu daga Masar, kuka kawo mu mu mutu a wannan hamada? Babu abinci! Babu ruwa! Mu dai mun gaji da wannan abinci marar amfani!”
6 Bunun üzerine RAB halkın arasına zehirli yılanlar gönderdi. Yılanlar ısırınca İsrailliler'den birçok kişi öldü.
Sai Ubangiji ya aiko da macizai masu dafin a cikinsu, suka sassari mutane, Isra’ilawa masu yawa kuwa suka mutu.
7 Halk Musa'ya gelip, “RAB'den ve senden yakınmakla günah işledik. Yalvar da, RAB aramızdan yılanları kaldırsın” dedi. Bunun üzerine Musa halk için yalvardı.
Mutanen suka zo wurin Musa, suka ce, “Mun yi zunubi, da muka yi wa Ubangiji da kai gunaguni. Ka yi addu’a don Ubangiji yă ɗauke mana macizan nan.” Saboda haka Musa ya yi addu’a domin mutane.
8 RAB Musa'ya, “Bir yılan yap ve onu bir direğin üzerine koy. Isırılan herkes ona bakınca yaşayacaktır” dedi.
Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ƙera siffar maciji ka rataye shi a bisa doguwar sanda; kowa da maciji ya sare shi, idan ya dubi macijin nan da ka rataye, zai rayu.”
9 Böylece Musa tunç bir yılan yaparak direğin üzerine koydu. Yılan tarafından ısırılan kişiler tunç yılana bakınca yaşadı.
Saboda haka Musa ya ƙera macijin tagulla, ya kuma rataye shi bisa doguwar sanda. Sa’an nan duk wanda maciji ya sare shi, ya kuma dubi macijin tagullar, zai warke.
10 İsrail halkı yola koyulup Ovot'ta konakladı.
Isra’ilawa suka kama hanya, suka yi sansani a Obot.
11 Sonra Ovot'tan ayrılıp doğuda Moav'a bakan çölde, İye– Haavarim'de konakladı.
Sai suka tashi daga Obot, suka yi sansani a Iye Abarim a hamadar da take fuskantar Mowab, wajen fitowar rana.
12 Oradan da ayrılıp Zeret Vadisi'nde konakladı.
Daga nan kuma suka ci gaba, suka yi sansani a Kwarin Zered.
13 Oradan da ayrılıp Amorlular'ın sınırına dek uzanan çölde, Arnon Vadisi'nin karşı yakasında konakladılar. Arnon Moav'la Amorlular'ın ülkesi arasındaki Moav sınırıdır.
Suka tashi daga nan, suka sauka kusa da Arnon wanda yake a hamadar da ta miƙe zuwa iyakar Amoriyawa. Arnon shi ne iyakar Mowab, wanda yake tsakanin Mowab da Amoriyawa.
14 RAB'bin Savaşları Kitabı'nda şöyle yazılıdır: “... Sufa topraklarında Vahev Kenti, vadiler, Arnon Vadisi,
Shi ya sa Littafin Yaƙoƙin Ubangiji ya ce, “Waheb ta cikin yankin Sufa, da kwaruruka na tuddan Arnon,
15 Ar Kenti'ne dayanan ve Moav sınırı boyunca uzanan vadilerin yamaçları ...”
da gangaren kwaruruka, wanda ya nausa zuwa garin Ar, ya kuma dangana da kan iyakar Mowab.”
16 Oradan RAB'bin Musa'ya, “Halkı bir araya topla, onlara su vereceğim” dediği kuyuya, Beer'e doğru yol aldılar.
Daga can, suka gangara zuwa Beyer, wato, rijiyar da Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tattara mutane duka, zan kuwa ba su ruwa.”
17 O zaman İsrailliler şu ezgiyi söylediler: “Suların fışkırsın, ey kuyu! Ezgi okuyun ona.
Sai Isra’ilawa suka rera wannan waƙa, “Ki ɓuɓɓugo da ruwa, Ke rijiya! Rera waƙa game da ita,
18 O kuyu ki, onu önderlerle Halkın soyluları Asayla, değnekle kazdılar.” Bundan sonra çölden Mattana'ya,
game da rijiyar da’ya’yan sarki suka haƙa, rijiyar da manyan mutane masu sandunan sarauta suka nuna da sandunansu.” Sa’an nan suka tashi daga hamadar, suka tafi Mattana,
19 Mattana'dan Nahaliel'e, Nahaliel'den Bamot'a,
daga Mattana, suka tafi Nahaliyel, daga Nahaliyel, suka tafi Bamot,
20 Bamot'tan Moav topraklarındaki vadiye, çöle bakan Pisga Dağı'nın eteklerine gittiler.
daga Bamot kuma suka tafi kwarin da yake cikin Mowab inda ƙwanƙolin Fisga yake fuskantar hamada.
21 İsrailliler Amorlular'ın Kralı Sihon'a ulaklarla şu haberi gönderdi:
Isra’ila suka aiki manzanni wurin Sihon sarkin Amoriyawa su ce,
22 “İzin ver, ülkenden geçelim. Tarlalardan, bağlardan geçmeyeceğiz, hiçbir kuyudan su içmeyeceğiz. Sınırından geçinceye dek, Kral yolundan yolumuza devam edeceğiz.”
“Ka bari mu ratsa ta ƙasarka. Ba za mu shiga wata gona ba, ba za mu kuma shiga gonar inabi, ko mu sha ruwa daga wata rijiya ba. Za mu bi ta babbar hanyar sarki, har mu fita ƙasarka.”
23 Ne var ki Sihon, ülkesinden İsrailliler'in geçmesine izin vermedi. İsrailliler'le savaşmak üzere bütün halkını toplayıp çöle çıktı. Yahesa'ya varınca, İsrailliler'e saldırdı.
Amma Sihon bai bar Isra’ila su ratsa ta yankinsa ba. Sai ya tara dukan sojojinsa, suka fita zuwa cikin hamada, su yaƙi Isra’ila. Da ya kai Yahaz, sai ya yaƙi Isra’ila.
24 İsrailliler onu kılıçtan geçirip Arnon'dan Yabbuk'a, Ammonlular'ın sınırına dek uzanan topraklarını aldılar. Az Kenti Ammon sınırını oluşturuyordu.
Isra’ila fa suka kashe shi da takobi, suka ƙwace ƙasarsa, tun daga kogin Arnon har zuwa kogin Yabbok, zuwa kan iyakar Ammonawa kawai, gama sun yi wa iyakansu katanga.
25 İsrailliler Heşbon ve çevresindeki köylerle birlikte Amorlular'ın bütün kentlerini ele geçirerek orada yaşamaya başladılar.
Isra’ila suka ci dukan biranen Amoriyawa, suka kuma zauna a cikinsu, haɗe da babban birnin Heshbon da dukan ƙauyukanta.
26 Heşbon Amorlular'ın Kralı Sihon'un kentiydi. Sihon eski Moav Kralı'na karşı savaşmış, Arnon'a dek uzanan topraklarını elinden almıştı.
Sihon sarkin Amoriyawa ya yi mulkin Heshbon, bayan ya ci sarkin Mowab na dā da yaƙi, ya kuma ƙwace dukan ƙasarsa har zuwa arewancin kogin Arnon.
27 Bunun için ozanlar şöyle diyor: “Heşbon'a gelin, Sihon'un kenti yeniden kurulsun Ve sağlamlaştırılsın.
Shi ya sa Amoriyawa suka rubuta wannan waƙa game da Heshbon suka ce, “Ku zo mu sāke gina Heshbon, birnin Sihon.
28 Heşbon'dan ateş, Sihon'un kentinden alev çıktı; Moav'ın Ar Kenti'ni, Arnon tepelerinin efendilerini yakıp yok etti.
“Mayaƙansa sun fito kamar harshen wuta suka ƙone birnin Ar na Mowab suna hallaka’yan ƙasar tuddan Arnon.
29 Vay sana, ey Moav! İlah Kemoş'un halkı, yok oldun! Kemoş senin oğullarının Amorlular'ın Kralı Sihon'a kaçmasını, Kızlarının ona tutsak olmasını önleyemedi.
Kaitonki, Mowab! Gunkinki Kemosh ya yashe mutanenki; aka kuma kama su, aka kai su bauta wajen Sihon sarkin Amoriyawa.
30 Onları bozguna uğrattık; Heşbon Divon'a dek yıkıma uğradı. Medeva'ya uzanan Nofah'a dek onları yıkıma uğrattık.”
“Amma mun tumɓuke su, mun hallaka garuruwan Heshbon har zuwa Dibon. Mun ragargaza su har zuwa Nofa wanda ya miƙe zuwa Medeba.”
31 Böylece İsrail halkı Amorlular'ın ülkesinde yaşamaya başladı.
Ta haka Isra’ila suka zauna a ƙasar Amoriyawa.
32 Musa Yazer'i araştırmak için adamlar gönderdi. Sonra İsrailliler Yazer çevresindeki köyleri ele geçirerek orada yaşayan Ammonlular'ı kovdular.
Sai Musa ya aika’yan leƙen asiri zuwa Yazer. Daga baya, sai Isra’ilawa suka ci ƙauyukan da suke kewaye, suka kuma kori Amoriyawa da suke zaune a can.
33 Bundan sonra dönüp Başan'a doğru ilerlediler. Başan Kralı Og'la ordusu onlarla savaşmak için Edrei'de karşılarına çıktı.
Sai suka juya suka haura kan hanya ta zuwa Bashan, inda Og yake sarauta, ya kuwa fito tare da dukan sojojinsa suka yi yaƙi da Isra’ila a Edireyi.
34 RAB Musa'ya, “Ondan korkma!” dedi, “Çünkü onu da ordusuyla ülkesini de senin eline teslim ettim. Amorlular'ın Heşbon'da yaşayan Kralı Sihon'a yaptığının aynısını ona da yapacaksın.”
Ubangiji ya ce wa Musa, “Kada ka ji tsoronsa, gama na ba da shi a gare ka, da dukan sojojinsa da kuma ƙasarsa. Ka yi da shi yadda ka yi da Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon.”
35 Böylece İsrail halkı kimseyi sağ bırakmadan Og'la oğullarını ve ordusunu yok etti, ülkeyi ele geçirdi.
Ta haka suka kashe shi, tare da’ya’yansa maza da kuma dukan sojojinsa, ba wanda ya ragu. Suka kuma mamaye ƙasarsa.