< Nehemya 5 >
1 Bir süre sonra kadınlı erkekli halk Yahudi kardeşlerinden şiddetle yakınmaya başladı.
To, sai maza da matansu suka tā da fara gunaguni mai tsanani a kan’yan’uwansu Yahudawa.
2 Bazıları, “Biz kalabalığız” diyordu, “Oğullarımız, kızlarımız çok. Yaşamak için buğdaya ihtiyacımız var.”
Waɗansu suka ce, “Mu da’ya’yanmu maza da mata muna da yawa, muna bukatar hatsi domin mu ci mu rayu.”
3 Bazıları da, “Kıtlıkta buğday almak için tarlalarımızı, bağlarımızı, evlerimizi ipotek ediyoruz” diyordu.
Waɗansu kuwa suka ce, “Saboda yunwa mun jinginar da gonakinmu, da gonakin inabinmu, da gidajenmu don mu sami hatsi.”
4 Bazıları ise, “Krala vergi ödemek için tarlalarımızı, bağlarımızı karşılık gösterip borç para aldık” diyordu,
Har illa yau waɗansu suka ce, “Mun ci bashin kuɗi don mu biya haraji a kan gonakinmu, da gonakin inabinmu.
5 “Yahudi kardeşlerimizle aynı kanı taşımıyor muyuz? Bizim çocuklarımızın onlarınkinden ne farkı var? Oğullarımızı kızlarımızı köle olarak satmak zorunda kaldık. Kızlarımızdan bazıları cariye olarak satıldı bile. Çaresiz kaldık. Çünkü tarlalarımız, bağlarımız başkalarının elinde.”
Ga shi kuwa, mu da su dangin juna ne,’ya’yanmu da nasu kuma ɗaya ne, duk da haka an tilasta mu mu sa’ya’yanmu mata da maza su zama bayi. Har ma an riga an bautar waɗansu daga cikin’ya’yanmu mata, amma ba mu da iko mu ce kome, domin gonakinmu da gonakin inabinmu suna a hannun waɗansu mutane.”
6 Onların bu dertlerini, yakınmalarını duyunca çok öfkelendim.
Sa’ad da na ji kukansu da waɗannan koke-koke, na husata ƙwarai.
7 Düşününce soylularla yetkilileri suçlu buldum. Onlara, “Kardeşlerinizden faiz alıyorsunuz!” dedim. Onlara karşı herkesi bir araya topladım. Sonra şöyle dedim:
Na yi tunaninsu a zuciyata sa’an nan na zargi manyan gari da shugabanni. Na ce musu, “Kuna musguna wa’yan’uwanku ta wurin ba su rance da ruwa!” Saboda haka na kira babban taro gaba ɗaya don a magance wannan.
8 “Biz yabancılara satılan Yahudi kardeşlerimizi elimizden geldiğince geri almaya çalışırken siz kardeşlerinizi satıyorsunuz. Yine bize satılsınlar diye mi?” Sustular, söyleyecek söz bulamadılar.
Na ce, “Da dukan iyakar ƙoƙarinmu, mun fanshi’yan’uwanmu Yahudawan da aka sayar wa Al’ummai. Amma ga shi kuna sayar da’yan’uwanku ga Al’ummai, don kawai a sāke sayar mana da su!”
9 Sonra, “Yaptığınız doğru değil” dedim, “Düşmanlarımız olan öteki ulusların aşağılamalarından kaçınmak için Tanrı korkusuyla yaşamanız gerekmez mi?
Saboda haka na ci gaba na ce, “Abin da kuke yi a yanzu ba daidai ba ne. Bai kamata ku yi tafiya cikin tsoron Allahnmu don mu guji ba’ar Al’ummai abokan gābanmu ba?
10 Kardeşlerim, adamlarım ve ben ödünç olarak halka para ve buğday veriyoruz. Lütfen faiz almaktan vazgeçelim!
Ni ma da’yan’uwana da kuma mutanena muna ba wa mutane bashin kuɗi da kuma hatsi. Sai mu daina sha’anin ba da rance da ruwa!
11 Tarlalarını, bağlarını, zeytinliklerini, evlerini onlara hemen geri verin. Bir de faiz olarak aldığınız gümüşün, buğdayın, yeni şarabın, zeytinyağının yüzde birini verin.”
Yau sai ku mayar musu da gonakinsu, da gonakin inabinsu, da na zaitunsu, da gidajensu, da kashi ɗaya bisa ɗari na kuɗi, da na hatsi, da na ruwan inabi, da na mai, waɗanda kuka karɓa a wurinsu.”
12 “Veririz” dediler, “Artık onlardan hiçbir şey istemeyeceğiz. Ne diyorsan öyle yapacağız.” Kâhinleri çağırdım ve yetkililere kâhinlerin önünde verdikleri sözü tutacaklarına ilişkin ant içirdim.
Suka ce, “Za mu mayar musu, kuma ba za mu bukaci wani abu daga gare su ba. Za mu yi yadda ka faɗa.” Sai na tattara firistoci na kuma sa manyan gari da shugabanni su yi rantsuwa don su yi abin da suka yi alkawari.
13 Sonra eteğimi silktim ve dedim ki, “Kim verdiği sözü tutmazsa, Tanrı da onu böyle silksin; malını mülkünü elinden alsın; tamtakır bıraksın.” Herkes buna, “Amin” dedi ve RAB'be övgüler sundu. Ve sözlerini tuttular.
Na kuma kakkaɓe hannuna, na ce, “Duk wanda ya karya wannan alkawari, haka Allah zai kakkaɓe shi daga gidansa da aikinsa. Allah zai kakkaɓe shi, yă wofintar da shi!” Da jin wannan, sai dukan taron suka ce, “Amin,” suka kuma yabi Ubangiji. Mutane kuwa suka yi kamar yadda suka yi alkawari.
14 Yahuda'da valilik yaptığım on iki yıl boyunca, ilk atandığım günden son güne kadar, Artahşasta'nın krallığının yirminci yılından otuz ikinci yılına dek, ne ben, ne kardeşlerim valiliğe ayrılan yiyecek bütçesine dokunmadık.
Ban da haka ma, daga shekara ta ashirin ta Sarki Artazerzes, sa’ad da aka naɗa ni in zama gwamnansu a ƙasar Yahuda, har zuwa shekara ta talatin da biyu na mulkinsa, shekara sha biyu ke nan, ko ni, ko’yan’uwana, ba wanda ya ci abincin da akan ba wa gwamna.
15 Benden önce görev yapan valiler halka yük oldular. Onlardan kırk şekel gümüşün yanısıra yiyecek ve şarap da aldılar. Uşakları bile halkı ezdi. Ama ben Tanrı'dan korktuğum için böyle davranmadım.
Amma gwamnonin farko, waɗanda suka riga ni, sun ɗaura wa mutane kaya mai nauyi suka karɓi shekel arba’in na azurfa daga gare su haɗe da abinci da kuma ruwan inabi. Har bayin masu mulki ma sun nawaya wa mutane. Amma ni ban yi haka ba, saboda ina tsoron Allah.
16 Surların onarımını sürdürdüm. Adamlarımın hepsi işin başında durdu. Bir tarla bile satın almadık.
A maimakon haka, na miƙa kaina ga aiki a kan wannan katanga. Na tattara dukan mutanena a can don aikin; ba mu samar wa kanmu wata gona ba.
17 Çevremizdeki uluslardan bize gelenlerin dışında Yahudiler'den ve yetkililerden yüz elli kişi soframa otururdu.
Bugu da ƙari, Yahudawa da shugabanni ɗari da hamsin suna ci daga teburina, haka ma waɗanda suka zo wurinmu daga ƙasashen da suke kewaye.
18 Benim için her gün bir boğa, altı seçme koyun, tavuklar kesilir, on günde bir de her türden bolca şarap hazırlanırdı. Bütün bunlara karşın valiliğin yiyecek bütçesine dokunmadım. Çünkü halk ağır yük altındaydı.
Kowace rana akan shirya mini saniya ɗaya, zaɓaɓɓun tumaki shida da waɗansu kaji, kuma kowace kwana goma akan tanadar da ruwan inabi na kowane iri a yalwace. Duk da haka, ban taɓa nemi a ba ni abincin da akan ba wa gwamna ba, domin wahala ta yi wa jama’a yawa.
19 Ey Tanrım, bu halk uğruna yaptıklarım için beni iyilikle an.
Ka tuna da ni, ka yi mini alheri, ya Allah, saboda dukan abubuwan da na yi saboda waɗannan mutane.