< Malaki 3 >

1 “İşte habercimi gönderiyorum. Önümde yolu hazırlayacak. Aradığınız Rab ansızın tapınağına gelecek; görmeyi özlediğiniz antlaşma habercisi gelecek” diyor Her Şeye Egemen RAB.
“Duba, zan aika manzona, wanda zai shirya hanya a gabana. Sa’an nan a farat ɗaya Ubangiji wanda kuke nema zai zo haikalinsa. Manzon alkawari, wanda kuke sa zuciya kuwa zai zo,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
2 Ama onun geleceği güne kim dayanabilir? O belirince kim durabilir? Çünkü o maden arıtıcının ateşi, çamaşırcının kül suyu gibi olacak;
Amma wa zai jure wa ranar zuwansa? Wa zai iya tsaya sa’ad da ya bayyana? Gama zai zama kamar wuta mai tace ƙarfe, ko sabulu mai wanki.
3 gümüş eritip arıtan gibi davranacak: Levililer'i arındırıp altın, gümüş temizler gibi temizleyecek. Böylece RAB'be doğrulukla sunular sunacaklar.
Zai zama kamar mai tace azurfa da mai tsarkaketa; zai tsabtacce Lawiyawa, yă kuma tace su kamar zinariya da azurfa. Sa’an nan Ubangiji zai sami mutanen da za su kawo hadayu a cikin adalci.
4 Geçmiş günlerde, geçmiş yıllarda olduğu gibi, RAB Yahuda ve Yeruşalim'in sunacağı sunulardan hoşnut kalacak.
Hadayun Yahuda da na Urushalima za su zama yardajje ga Ubangiji, za su zama kamar a kwanakin da suka wuce, kamar a shekarun baya.
5 Her Şeye Egemen RAB, “Yargılamak için size yaklaşacağım” diyor, “Büyücülere, zina edenlere, yalan yere ant içenlere, işçinin, dulun, öksüzün, yabancının hakkını çiğneyenlere –benden korkmayanlara– karşı hemen tanık olacağım.”
“Ta haka zan zo kusa da ku don in yi hukunci. Zan hanzarta ba da shaida a kan masu yin sihiri, da mazinata da masu shaidar zur. Zan ba da shaida a kan waɗanda suke zaluntar ma’aikata a kan albashinsu, da waɗanda suke ƙwarar gwauraye da marayu, suna kuma hana baƙi samun adalci, ba sa ma tsorona,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
6 “Ben RAB'bim, değişmem. Siz bunun için yok olmadınız, ey Yakup soyu!
“Ni Ubangiji ba na canjawa. Shi ya sa ku zuriyar Yaƙub, ba a hallaka ku ƙaƙaf ba.
7 Atalarınızın günlerinden bu yana kurallarımı çiğnediniz, onlara uymadınız. Bana dönün, ben de size dönerim” diyor Her Şeye Egemen RAB. “Oysa siz, ‘Nasıl döneriz?’ diye soruyorsunuz.
Tun zamanin kakanninku, kun juye wa ƙa’idodina baya, ba ku kuma kiyaye su ba. Ku komo gare ni, ni kuma zan koma gare ku,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya za mu koma gare ka?’
8 “İnsan Tanrı'dan çalar mı? Oysa siz benden çalıyorsunuz. “‘Senden nasıl çalıyoruz?’ diye soruyorsunuz. “Ondalıkları, sunuları çalıyorsunuz.
“Mutum zai iya yi wa Allah fashi ne? Duk da haka kun yi mini fashi. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya muka yi maka fashi?’ “A wajen zakka da hadayu.
9 Siz lanete uğradınız. Çünkü bütün ulus benden çalıyorsunuz.
Kuna ƙarƙashin la’ana, dukan al’ummarku, domin kuna yin mini fashi.
10 Tapınağımda yiyecek bulunması için bütün ondalıklarınızı ambara getirin. Beni bununla sınayın” diyor Her Şeye Egemen RAB. “Göreceksiniz ki, göklerin kapaklarını size açacağım, üzerinize dolup taşan bereket yağdıracağım.
Ku kawo dukan zakka cikin gidan ajiya, don a kasance da abinci a gidana. Ku gwada ni a wannan ku ga, ko ba zan buɗe taskokin sama in zubo muku albarka mai yawa, wadda har ba za ku rasa wurin sa ta ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
11 Çekirgelerin ekinlerinizi yemesini engelleyeceğim. Tarlada asmanız ürünsüz kalmayacak” diyor Her Şeye Egemen RAB.
Zan hana ƙwari su cinye hatsinku. Kuringar inabi a gonakinku kuma ba za su zubar da’ya’yansu kafin su nuna ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
12 “Bütün uluslar ne mutlu size diyecekler. Çünkü ülkeniz özlenen bir yer olacak.” Böyle diyor Her Şeye Egemen RAB.
“Sa’an nan dukan al’ummai za su ce da ku masu albarka, gama ƙasarku za tă yi daɗin zama,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
13 “Bana karşı sert sözler söylediniz” diyor RAB. “Oysa siz, ‘Sana karşı ne söyledik?’ diye soruyorsunuz.
“Kun faɗi mugayen abubuwa a kaina,” in ji Ubangiji. “Duk da haka kuka ce, ‘Me muka faɗa a kanka?’
14 “Şunu dediniz: ‘Tanrı'ya kulluk etmek yararsızdır. Her Şeye Egemen RAB'bin isteklerini yerine getirmek, O'nun önünde yas tutar gibi davranmak bize ne kazanç sağlıyor?
“Kun ce, ‘Ba amfani a bauta wa Allah. Wanda amfani muka samu ta wurin kiyaye umarnansa muna yawo kamar masu makoki a gaban Ubangiji Maɗaukaki?
15 Şimdi kendini beğenmişlere mutlu diyoruz. Kötülük edenler başarılı oluyor, Tanrı'yı deneyenler cezadan kurtuluyor.’”
A ganinmu, masu girman kai suna jin daɗi. Masu aikata mugunta kuwa ba arziki kaɗai suka yi ba, amma sukan gwada Allah da mugayen ayyukansu, su kuwa zauna lafiya.’”
16 Bunun üzerine RAB'den korkanlar birbirleriyle konuştular. RAB dediklerine kulak verip duydu. RAB'den korkup adını sayanlar için O'nun önünde bir anma kitabı yazıldı.
Sa’an nan waɗanda suke tsoron Ubangiji suka yi magana da juna, Ubangiji kuwa ya kasa kunne ya kuma ji. A gabansa aka rubuta a littafin tarihi waɗanda suke tsoron Ubangiji, suna kuma girmama sunansa.
17 Her Şeye Egemen RAB, “Öz halkımı ortaya çıkardığım gün, benim olacaklar” diyor, “Bir baba kendisine hizmet eden oğlunu nasıl esirgerse ben de onları öyle esirgeyeceğim.
“A ranar da na shirya ajiyayyen mallakata, za su zama nawa,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan ji kansu kamar yadda mahaifi cikin tausayi yakan ji kan ɗansa wanda yake masa hidima.
18 O zaman siz doğru kişiyle kötü kişi, Tanrı'ya kulluk edenle etmeyen arasındaki ayrımı yine göreceksiniz.”
Za ku kuma ga bambanci tsakanin masu adalci da mugaye, tsakanin waɗanda suke wa Allah hidima da kuma waɗanda ba sa yi.

< Malaki 3 >