< Hâkimler 14 >
1 Şimşon bir gün Timna'ya gitti. Orada Filistli bir kadın gördü.
Samson ya gangara zuwa Timna a can ya ga wata daga cikin’yan mata Filistiyawa.
2 Geri dönünce annesiyle babasına, “Timna'da Filistli bir kadın gördüm” dedi, “Onu hemen bana eş olarak alın.”
Da ya komo, sai ya gaya wa mahaifinsa da mahaifiyarsa ya ce, “Na ga wata mace a Timna; ku auro mini ita ta zama matata.”
3 Annesiyle babası, “Akrabalarının ya da halkımızın kızları arasında kimse yok mu ki, sünnetsiz Filistliler'den kız almaya kalkıyorsun?” diye karşılık verdiler. Ama Şimşon babasına, “Bana o kadını al, ondan hoşlanıyorum” dedi.
Mahaifinsa da mahaifiyarsa suka ce, “Babu wata karɓaɓɓiyar yarinya a cikin zuriyarku ko cikin dukan mutanenmu ne? Dole ne ka tafi wajen Filistiyawa marasa kaciya ka nemi aure?” Amma Samson ya ce wa mahaifinsa, “A auro mini ita dai. Ita ta dace da ni.”
4 Şimşon'un annesiyle babası bunu isteyenin RAB olduğunu anlamadılar. Çünkü RAB o sırada İsrailliler'e egemen olan Filistliler'e karşı fırsat kolluyordu.
(Iyayensa ba su san cewa wannan daga wurin Ubangiji ne ba, wanda yake neman hanyar da za a kai wa Filistiyawa hari; gama a lokacin suna mulkin Isra’ila.)
5 Böylece Şimşon annesi ve babasıyla Timna'ya doğru yola koyuldu. Timna bağlarına vardıklarında, genç bir aslan kükreyerek Şimşon'un karşısına çıktı.
Sai Samson ya gangara zuwa Timna tare da mahaifinsa da kuma mahaifiyarsa. Da suka yi kusa da gonar inabin Timna, nan da nan sai ga ɗan zaki ya taso ya nufe shi yana ruri.
6 Şimşon üzerine inen RAB'bin Ruhu'yla güçlendi ve aslanı bir oğlak parçalar gibi çıplak elle parçaladı. Ama yaptığını ne annesine ne de babasına bildirdi.
Ruhun Ubangiji kuwa ya sauko masa da ƙarfi, ya sa ya yaga zakin kashi biyu da hannu kamar yadda akan yayyage ɗan akuya. Sai dai bai gaya wa iyayensa abin da ya yi ba.
7 Sonra gidip kadınla konuştu ve ondan çok hoşlandı.
Sa’an nan ya gangara ya yi magana da yarinyar, yana kuwa sonsa.
8 Bir süre sonra kadınla evlenmek üzere yine Timna'ya giderken, aslanın leşini görmek için yoldan saptı. Bir arı sürüsünün aslanın leşini kovana çevirdiğini gördü.
Daga baya, da ya koma don yă aure ta, sai ya ratse don yă ga gawar zakin. Sai ga taron ƙudan zuma da zuma a ciki,
9 Kovandaki balı avuçlarına doldurdu, yiye yiye oradan uzaklaştı. Annesiyle babasının yanına varınca baldan onlara da verdi, onlar da yedi. Ama balı aslanın leşinden aldığını söylemedi.
wanda ya sa hannu ya ɗebo yana tafiya yana sha. Sa’ad da ya iso wurin iyayensa, ya ba su zuman, su ma suka sha. Sai dai bai gaya musu cewa ya ɗebo zuman daga gawar zaki ba.
10 Babası kadını görmeye gidince, Şimşon da damat geleneğine uyarak orada bir şölen düzenledi.
To, mahaifinsa ya gangara don yă ga yarinyar. Samson kuwa ya shirya wata liyafa a can, yadda yake bisa ga al’adar angwaye.
11 Filistliler onu görünce ona eşlik etmek üzere otuz genç getirdiler.
Sa’ad da ya bayyana, sai aka haɗa shi abokai talatin.
12 Şimşon onlara, “Size bir bilmece sorayım” dedi, “Şölenin yedi günü içinde kesin yanıtı bulup bana bildirirseniz, size otuz keten mintan, otuz takım da üst giysi vereceğim.
Sai Samson ya ce, “Bari in yi muku kacici-kacici, in kun ba ni amsa cikin kwana bakwai na wannan biki, zan ba ku riguna lilin talatin da kuma tufafi talatin.
13 Ama bilmeceyi çözemezseniz, o zaman da siz bana otuz keten mintanla otuz takım üst giysi vereceksiniz.” Ona, “Seni dinliyoruz” dediler, “Söyle bakalım bilmeceni.”
In kuma ba ku iya ba ni amsar ba, dole ku ba ni rigunan lilin talatin da tufafi talatin.” Suka ce, “Ka gaya mana kacici-kacicin.”
14 Şimşon, “Yiyenden yiyecek, Güçlüden tatlı çıktı” dedi. Üç gün geçtiyse de bilmeceyi çözemediler.
Sai ya ce, “Daga mai ci, abinci ya fito; daga mai ƙarfi, abu mai zaki ya fito.” Har kwana uku ba su iya ba da amsa ba.
15 Dördüncü gün gençler Şimşon'un karısına, “Kocanı kandır da bize bilmecenin yanıtını versin” dediler, “Yoksa, seni de babanın evini de yakarız. Bizi soymak için mi buraya çağırdınız?”
A rana ta huɗu suka ce wa matar Samson “Ki rarrashi mijinki yă bayyana mana kacici-kacicin, ko kuwa mu ƙone ki da gidan mahaifinki duka da wuta. Kun kira mu domin ku yi mana fashi ne?”
16 Şimşon'un karısı ağlayarak ona, “Benden nefret ediyorsun” dedi, “Beni sevmiyorsun. Soydaşlarıma bir bilmece sordun, yanıtını bana söylemedin.” Şimşon karısına, “Bak” dedi, “Anneme babama bile söylemedim, sana mı söyleyeceğim?”
Sa’an nan matar Samson ta kwanta masa a jiki tana kuka tana cewa, “Kai maƙiyina ne, lalle ba ka ƙaunata, ka yi wa mutanena kacici-kacici, amma ba ka gaya mini amsar ba.” Ya amsa ya ce, “Ban ma bayyana wa mahaifina ko mahaifiyata ba, to, don me zan bayyana miki?”
17 Kadın şölen boyunca yedi gün ağlayıp durdu. Kadının sürekli sıkıştırması üzerine Şimşon yedinci gün bilmecenin yanıtını ona söyledi. Kadın da yanıtı soydaşlarına iletti.
Ta yi ta kuka har kwana bakwai na bikin. Saboda haka a rana ta bakwai sai ya gaya mata, don ta dame shi. Ita kuwa ta bayyana kacici-kacicin wa mutanenta.
18 Yedinci gün, gün batmadan kentli gençler Şimşon'a geldiler. “Baldan tatlı, Aslandan güçlü ne var?” dediler. Şimşon, “Düvemle çift sürmüş olmasaydınız, bilmecemi çözemezdiniz” diye karşılık verdi.
Kafin rana ta fāɗi a rana ta bakwai mutane garin suka ce masa, “Me ya fi zuma zaki? Me ya fi zaki ƙarfi?” Samson ya ce musu, “Da ba don kun haɗa baki da matata ba, da ba za ku san amsar kacici-kacici ba.”
19 RAB'bin Ruhu üzerine inince güçlenen Şimşon Aşkelon'a gitti; otuz kişi vurup mallarını yağmaladı, giysilerini de bilmeceyi çözenlere verdi. Öfkeden kudurmuş bir halde babasının evine döndü.
Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko masa da iko. Sai ya fita ya gangara zuwa Ashkelon, ya kashe mutanensu talatin, ya kwashe kayansu ya kuma ba da rigunarsu ga waɗanda suka bayyana kacici-kacicin. Cike da fushi, ya haura zuwa gidan mahaifinsa.
20 Şimşon'un karısı ise Şimşon'a eşlik eden sağdıca verildi.
Aka kuma ɗauki matar Samson aka ba wa ɗaya daga cikin waɗanda suka yi masa hidima a bikin.