< Yahuda 1 >

1 İsa Mesih'in kulu, Yakup'un kardeşi ben Yahuda'dan, Baba Tanrı tarafından sevilip İsa Mesih için korunmuş olan çağrılmışlara selam!
Yahuda, bawan Yesu Kiristi, ɗan’uwan Yaƙub, Zuwa ga waɗanda aka kira, waɗanda Allah Uba yake ƙauna, waɗanda kuma Yesu Kiristi ya kiyaye.
2 Merhamet, esenlik ve sevgi artan ölçüde sizin olsun.
Jinƙai, salama da kuma ƙauna, su kasance tare da ku a yalwace.
3 Sevgili kardeşlerim, size ortak kurtuluşumuzla ilgili yazmaya çok gayret ettim. Bu arada sizi kutsallara ilk ve son kez emanet edilen iman uğrunda mücadeleye özendirmek için yazma gereğini duydum.
Abokaina ƙaunatattu, ko da yake na yi marmari ƙwarai in rubuta muku game da ceton nan namu, sai na ga ya dace in rubuta, in gargaɗe ku ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiya wadda aka danƙa wa mutane masu tsarki na Allah sau ɗaya tak.
4 Çünkü Tanrımız'ın lütfunu sefahate araç eden, tek Efendimiz ve Rabbimiz İsa Mesih'i yadsıyan bazı tanrısızlar gizlice aranıza sızdılar. Onların yargılanacakları çoktan beri yazılmıştır.
Na faɗa haka ne domin waɗansu mutanen da aka rubuta hukuncinsu tun dā sun shiga cikinku a ɓoye. Su fa marasa tsoron Allah ne. Su ne waɗanda suka mai da alherin Allahnmu ya zama dalilin yin fasikanci, suna kuma mūsun Yesu Kiristi wanda shi ne Makaɗaici Mai Iko Duka da kuma Ubangijinmu.
5 Bütün bunları bildiğiniz halde, size anımsatmak isterim ki, ilk ve son kez halkı Mısır'dan kurtaran Rab iman etmeyenleri daha sonra yok etti.
Ko da yake kun riga kun san duk wannan, ina so in tuna muku cewa Ubangiji ya ceci mutanensa daga Masar, duk da haka daga baya ya hallaka waɗanda ba su ba da gaskiya ba.
6 Yetkilerinin sınırı içinde kalmayıp kendilerine ayrılan yeri terk etmiş olan melekleri, büyük yargı günü için çözülmez bağlarla bağlayarak karanlığa hapsetti. (aïdios g126)
Haka ma mala’ikun da ba su riƙe matsayinsu na iko ba, waɗanda suka bar ainihin mazauninsu, su ne ya tsare a duhu daure da dawwammamun sarƙoƙi don hukunci ta babbar Ranan nan. (aïdios g126)
7 Sodom, Gomora ve çevrelerindeki kentler de benzer biçimde kendilerini fuhuş ve sapıklığa teslim ettiler. Sonsuza dek ateşte yanma cezasını çeken bu kentler ders alınacak birer örnektir. (aiōnios g166)
Haka ma Sodom da Gomorra da garuruwan da suke kewaye da su, waɗanda su ma suka ba da kansu ga fasikanci da muguwar sha’awar jiki, sun zama misalin waɗanda suke shan hukuncin madawwamiyar wuta. (aiōnios g166)
8 Aranıza sızan bu kişiler de onlar gibi gördükleri düşlere dayanarak öz bedenlerini kirletiyor, Rab'bin yetkisini hiçe sayıyor, yüce varlıklara sövüyorlar.
Haka yake da masu mafarke-mafarken nan, gama sun ƙazantar da jikunansu, suka ƙi bin masu mulki, suna ɓata sunan talikan sararin sama.
9 Oysa Başmelek Mikail bile Musa'nın cesedi konusunda İblis'le çekişip tartışırken, söverek onu yargılamaya kalkışmadı. Ancak, “Seni Rab azarlasın” dedi.
Kai, ko Mika’ilu babban shugaban mala’iku ma, sa’ad da yake mūsu da Iblis game da gawar Musa, bai yi garajen ɗora masa laifi da baƙar magana ba, sai dai ya ce, “Ubangiji yă tsawata maka!”
10 Ama bu kişiler anlamadıkları her şeye sövüyorlar. Öte yandan, akıldan yoksun hayvanlar gibi içgüdüleriyle anladıkları ne varsa, onları yıkıma götürüyor.
Duk da haka mutanen nan suna maganar banza a kan kome da ba su gane ba; kuma abubuwan da suka fahimta bisa ga jiki, kamar dabbobi marasa hankali, waɗannan abubuwa ne suke hallaka su.
11 Vay onların haline! Çünkü Kayin'in yolundan gittiler. Kazanç için kendilerini Balam'ınkine benzer bir yanılgıya kaptırdılar. Korah'ınkine benzer bir isyanda mahvoldular.
Kaitonsu! Gama sun kama hanyar Kayinu; sun ruga a guje garin neman riba cikin kuskure kamar Bala’am; aka kuma hallaka su cikin tawayen Kora.
12 Sevgi şölenlerinizde sizinle birlikte pervasızca yiyip içen bu kişiler birer kara lekedir. Yalnız kendilerini besleyen çobanlardır. Rüzgarın sürüklediği yağmursuz bulutlara, iki kez ölmüş, kökünden sökülmüş, sonbaharın meyvesiz ağaçlarına benzerler.
Waɗannan mutane sun zama kamar ƙazanta a taronku na soyayya, suna ta ciye-ciye a cikinku, ba kunya ba tsoro. Su masu kiwo ne da suke ciyar da kansu kawai. Su kamar hadari ne da babu ruwa da iska take kori. Su kamar itatuwa ne, marasa’ya’ya da rani, waɗanda aka tumɓuke, ko kamar itatuwan da aka tumɓuke suka kuma mutu ƙurmus.
13 Köpüğünü savuran denizin azgın dalgaları gibi ayıplarını çevreye savururlar. Serseri yıldızlar gibidirler. Onları sonsuza dek sürecek koyu karanlık bekliyor. (aiōn g165)
Su kamar raƙuman ruwan teku ne masu hauka, suna taƙama da tumbatsan kumfar kunyarsu. Su kamar taurari ne masu yawo barkatai, waɗanda aka ajiye mugun duhu saboda su har abada. (aiōn g165)
14 Adem'den sonraki altıncı kuşaktan olan Hanok, bu adamlara ilişkin şu peygamberlikte bulundu: “İşte Rab herkesi yargılamak üzere on binlerce kutsalıyla geliyor. Tanrı yoluna aykırı, tanrısızca yapılan bütün işlerden ve tanrısız günahkârların kendisine karşı söylediği bütün ağır sözlerden ötürü Rab, bütün insanlara suçluluklarını gösterecektir.”
Enok ma, wanda yake na bakwai daga Adamu, ya yi annabci game da waɗannan mutane cewa, “Duba, Ubangiji yana zuwa da dubu dubban tsarkakansa
don yă yi wa kowa shari’a, yă kuma hukunta duk marasa tsoron Allah game da dukan ayyukansu na rashin tsoron Allah da suka aikata ta hanyar rashin tsoron Allah, da kuma dukan baƙaƙen kalmomin da masu zunubi marasa tsoron Allah suka faɗa game da shi.”
16 Bunlar hep yakınıp söylenir, kendi tutkularının peşinden giderler. Ağızlarından kurumlu sözler çıkar, kendi çıkarları için başkalarını pohpohlarlar.
Waɗannan mutane dai, gunaguni gare su, kullum ganin laifin waɗansu suke yi. Muguwar sha’awa ce kaɗai tunaninsu. Sun cika da banzar magana ta yabon kansu. Suna ruɗin mutane da zaƙin baki don samun ribar kansu.
17 Ama siz, sevgili kardeşlerim, Rabbimiz İsa Mesih'in elçileri tarafından önceden söylenen sözleri anımsayın.
Amma ku abokaina ƙaunatattu, ku tuna da abin da manzannin Ubangijinmu Yesu Kiristi suka faɗa a dā.
18 Size demişlerdi ki, “Dünyanın son günlerinde alay edenler, tanrısızlığa yönelip kendi tutkularına göre yaşayanlar olacaktır.”
Sun ce muku, “A kwanakin ƙarshe za a kasance da masu ba’a waɗanda za su bi sha’awace-sha’awacensu na rashin tsoron Allah.”
19 Bunlar bölücü, insan doğasıyla sınırlı, Kutsal Ruh'tan yoksun kişilerdir.
Waɗannan mutanen ne, suke kawo rabe-rabe, masu bin abin da jiki yake so, marasa Ruhu.
20 Ama siz, sevgili kardeşlerim, kendinizi tümden kutsal olan imanınızın temeli üzerinde geliştirin. Kutsal Ruh'un yönetiminde dua edin.
Amma ku, abokaina ƙaunatattu, ku gina kanku cikin bangaskiyarku mafi tsarki, ku kuma yi addu’a cikin Ruhu Mai Tsarki.
21 Rabbimiz İsa Mesih'in sizi sonsuz yaşama kavuşturacak olan merhametini beklerken kendinizi Tanrı'nın sevgisinde koruyun. (aiōnios g166)
Ku zauna cikin ƙaunar Allah yayinda kuke jira jinƙan Ubangijinmu Yesu Kiristi don yă kawo ku ga rai madawwami. (aiōnios g166)
22 Kimi kararsızlara merhamet edin.
Ku ji tausayin waɗanda suke shakka;
23 Kimini ateşten çekip kurtarın. Kimine de korkuyla merhamet edin. Ama günahlı bir bedenin lekelediği giysiden bile tiksinin.
ku cece waɗansu ta wurin fizge su daga wuta. Ga waɗansu kuma ku ji tausayinsu, amma tare da tsoro, har ma ku yi ƙyamar tufafin da suka ɓata da ayyukansu na jiki.
24 Kurtarıcımız tek Tanrı, sizi düşmekten alıkoyacak, büyük sevinç içinde lekesiz olarak yüce huzuruna çıkaracak güçtedir.
To, yabo yă tabbata a gare shi, shi wanda yake da iko yă tsare ku daga fāɗuwa, yă kuma miƙa ku marasa laifi a gaban ɗaukakarsa da matuƙar farin ciki.
25 Yücelik, ululuk, güç ve yetki Rabbimiz İsa Mesih aracılığıyla bütün çağlardan önce, şimdi ve bütün çağlar boyunca Tanrı'nın olsun! Amin. (aiōn g165)
Gare shi kuma, shi da yake kaɗai Allah Mai Cetonmu, ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu, bari ɗaukaka, daraja, iko da mulki, su tabbata a gare shi, tun farkon zamanai, yanzu, da har abada abadin! Amin. (aiōn g165)

< Yahuda 1 >