< Yeşu 8 >
1 RAB Yeşu'ya, “Korkma, yılma” dedi, “Bütün savaşçılarını yanına alıp Ay Kenti'nin üzerine yürü. Ay Kralı'nı, halkını ve kenti bütün topraklarıyla birlikte sana teslim ediyorum.
Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Kada ka ji tsoro; kada ka karaya. Ka ɗauki dukan sojojin ku kai wa Ai hari, gama na ba ka nasara a kan sarkin Ai, mutanensa, birninsa da kuma ƙasarsa.
2 Eriha'ya ve kralına ne yaptıysan, Ay Kenti'ne ve kralına da aynısını yap. Ama mal ve hayvanlardan oluşan ganimeti kendinize ayırın. Kentin gerisinde pusu kur.”
Za ku yi wa Ai yadda kuka yi wa Yeriko da sarkinta, sai dai za ku kwashe ganima da dabbobinta su zama naku. Ku yi kwanto a bayan birnin.”
3 Böylece Yeşu bütün savaşçılarıyla birlikte Ay Kenti'nin üzerine yürümeye hazırlandı. Seçtiği otuz bin yiğit savaşçıyı geceleyin yola çıkarırken
Yoshuwa da dukan sojojin suka fita su kai wa Ai hari. Sai ya zaɓi sojojinsa waɗanda suka fi saura duka iya yaƙi guda dubu talatin, ya tura su da dad dare
4 onlara şöyle buyurdu: “Gidip kentin gerisinde pusuya yatın. Kentin çok uzağında durmayın. Hepiniz her an hazır olun.
ya ba su umarni ya ce, “Ku ji da kyau, za ku yi kwanto a bayan birnin, kada ku yi nisa da birnin. Kowannenku yă kasance a faɗake.
5 Ben yanımdaki halkla birlikte kente yaklaşacağım. Bir önceki gibi, düşman kentten çıkıp üzerimize gelince, önlerinde kaçar gibi yapıp
Ni da waɗanda suke tare da ni za mu nufi birnin, a lokacin da mutanen suka taso mana yadda suka yi dā, sai mu guje musu.
6 onları kentten uzaklaştırıncaya dek ardımızdan sürükleyeceğiz. Önceki gibi onlardan kaçtığımızı sanacaklar. Biz kaçar gibi yaparken,
Za su bi mu har su yi nisa da birnin, gama za su ce, ‘Suna gudu kamar yadda suka yi dā.’ Saboda haka lokacin da muka guje musu,
7 siz de pusu kurduğunuz yerden çıkıp kenti ele geçirirsiniz. Tanrımız RAB orayı elinize teslim edecek.
sai ku tashi daga inda kuka yi kwanto, ku ci birnin da yaƙi, Ubangiji Allahnku zai ba da shi a hannunku.
8 Kenti ele geçirince ateşe verin. RAB'bin buyruğuna göre hareket edin. İşte buyruğum budur.”
Lokacin da kuka ƙwace birnin, sai ku sa masa wuta. Ku yi abin da Ubangiji ya umarta. Ku tabbata kun yi abubuwan da na ce.”
9 Ardından Yeşu onları yolcu etti. Adamlar gidip Beytel ile Ay Kenti arasında, Ay Kenti'nin batısında pusuya yattılar. Yeşu ise geceyi halkla birlikte geçirdi.
Sai Yoshuwa ya sallame su, suka kuma tafi wurin da za su yi kwanto, suka kwanta suna fako tsakanin Betel da Ai, yamma da Ai, amma Yoshuwa ya kwana tare da mutanen.
10 Yeşu sabah erkenden kalkarak halkı topladı. Sonra kendisi ve İsrail'in ileri gelenleri önde olmak üzere Ay Kenti'ne doğru yola çıktılar.
Kashegari da sassafe Yoshuwa ya tattara mutanensa, sai shi da shugabannin Isra’ilawa suka sha gaba suka taka zuwa Ai.
11 Yeşu, yanındaki bütün savaşçılarla kentin üzerine yürüdü. Yaklaşıp kentin kuzeyinde ordugah kurdular. Kentle aralarında bir vadi vardı.
Dukan sojojin da suke tare da shi suka nufi birnin, da suka kai kuwa sai suka kafa sansaninsu a arewancin Ai. Tsakaninsu da Ai akwai kwari.
12 Yeşu beş bin kişi kadar bir güçle Beytel ile Ay Kenti arasında, kentin batısında pusu kurdurdu.
Yoshuwa ya sa mutum dubu biyar suka yi kwanto tsakanin Betel da Ai, a yammancin birnin.
13 Ardından hem kuzeyde ordugah kuranlar, hem batıda pusuya yatanlar savaş düzenine girdiler. Yeşu o gece vadide ilerledi.
Mutanen suka kafa sansaninsu arewa da birnin, sansani na’yan kwanto kuwa yana yamma da birnin, amma Yoshuwa ya kwana a kwarin.
14 Bunu gören Ay Kralı, kent halkıyla birlikte sabah erkenden kalktı. Zaman yitirmeden, İsrailliler'e karşı savaşmak üzere Arava bölgesinin karşısında belirlenen yere çıktı. Ne var ki, kentin gerisinde kendisine karşı kurulan pusudan habersizdi.
Sa’ad da sarkin Ai ya ga haka, shi da duk mutanen birnin suka hanzarta da sassafe don su gamu da Isra’ilawa, su yi yaƙi da su a wani wurin da yake fuskantar Araba. Amma bai san cewa an yi masa kwanto a bayan birnin ba.
15 Yeşu ile yanındaki İsrailliler, kent halkı önünde bozguna uğramış gibi, çöle doğru kaçmaya başladılar.
Yoshuwa da duk Isra’ilawa suka bari aka fafare su, sai suka gudu zuwa cikin jeji.
16 Kentteki bütün halk İsrailliler'i kovalamaya çağrıldı. Ama Yeşu'yu kovalarken kentten uzaklaştılar.
Aka kira duk mazan Ai su fafare su, suka kuwa fafari Yoshuwa, aka yaudare su suka yi nisa da birnin.
17 Ay Kenti'yle Beytel'den İsrailliler'i kovalamaya çıkmayan tek kişi kalmamıştı. İsrailliler'i kovalamaya çıkarlarken kent kapılarını açık bıraktılar.
Ba namijin da ya rage a Ai ko Betel da bai fita don yă fafari Isra’ilawa ba. Suka bar birnin a buɗe, suka tafi fafarar Isra’ilawa.
18 RAB Yeşu'ya, “Elindeki palayı Ay Kenti'ne doğru uzat; orayı senin eline teslim ediyorum” dedi. Yeşu elindeki palayı kente doğru uzattı.
Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Ka riƙe māshin da yake hannunka ka nuna wajen Ai, gama zan ba da birnin a hannunka.” Yoshuwa kuwa ya miƙa māshin ta wajen Ai.
19 Elini uzatır uzatmaz, pusudakiler yerlerinden fırlayıp kente girdiler; kenti ele geçirip hemen ateşe verdiler.
Da yin haka kuwa sai mutanen da suka yi kwanto suka tashi nan da nan daga inda suke, suka nufi birnin a guje, suka shiga suka ci birnin da yaƙi, suka kuma cinna mata wuta da sauri.
20 Kentliler arkalarına dönüp bakınca, yanan kentten göklere yükselen dumanı gördüler. Çöle doğru kaçan İsrailliler de geri dönüp onlara saldırınca artık kaçacak hiçbir yerleri kalmadı.
Mutanen Ai suka juya suka ga hayaƙin birninsu yana tashi sama, amma ba yadda za su iya tsira ta ko’ina, gama Isra’ilawan da suke gudu zuwa cikin jeji suka juya suka fara fafarar waɗanda suke fafararsu.
21 Pusuya yatmış olanların kenti ele geçirdiğini, kentten dumanlar yükseldiğini gören Yeşu ile yanındaki İsrailliler, geri dönüp Ay halkına saldırdılar.
Lokacin da Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka ga waɗanda suka yi kwanto sun ci birnin da yaƙi, hayaƙi kuwa ya cika birnin, sai suka juya suka kai wa mutanen Ai hari.
22 Kenti ele geçirenler de çıkıp saldırıya katılınca, kent halkı iki yönden gelen İsrailliler'in ortasında kaldı. İsrailliler tek canlı bırakmadan hepsini öldürdüler.
Mutanen da suka yi kwanto su ma suka fito daga birnin suka tasar musu, ya zama an kama su a tsakiya, ga Isra’ilawa daga kowane gefe. Isra’ilawa kuwa suka karkashe su duka ba su bar wani da rai ba, ba kuma wanda ya tsere.
23 Sağ olarak tutsak aldıkları Ay Kralı'nı Yeşu'nun önüne çıkardılar.
Amma suka tafi da sarkin Ai da rai suka kawo shi wurin Yoshuwa.
24 İsrailliler Ay Kenti'nden çıkıp kendilerini kırsal alanlarda ve çölde kovalayanların hepsini kılıçtan geçirdikten sonra kente dönüp geri kalanları da kılıçtan geçirdiler.
Da Isra’ilawa suka gama kashe duk mutanen Ai a filaye da kuma a cikin jeji inda suka fafare su, kuma da aka karkashe kowane mutumin Ai da takobi sai dukan Isra’ilawa suka koma Ai suka karkashe duk waɗanda suke cikinsa.
25 O gün Ay halkının tümü öldürüldü. Öldürülenlerin toplamı, kadın erkek, on iki bin kişiydi.
A ranan nan, dukan mutanen Ai da aka kashe, mutum dubu goma sha biyu ne maza da mata.
26 Yeşu kentte yaşayanların tümü yok edilinceye dek pala tutan elini indirmedi.
Gama Yoshuwa bai janye hannunsa da yake riƙe da māshinsa ba har sai da ya hallaka dukan mazaunan Ai.
27 İsrailliler, RAB'bin Yeşu'ya verdiği buyruk uyarınca, kentin yalnız hayvanlarıyla mallarını yağmaladılar.
Amma Isra’ilawa suka kwashe ganima da dabbobin birnin nan yadda Ubangiji ya umarci Yoshuwa.
28 Ardından Yeşu Ay Kenti'ni ateşe verdi, yakıp yıkıp viraneye çevirdi. Yıkıntıları bugün de duruyor.
Yoshuwa kuwa ya ƙone Ai, ya mai da ita tarin ƙasa, ta zama kufai har wa yau.
29 Ay Kralı'nı ağaca asıp akşama dek orada bırakan Yeşu, güneş batarken cesedi ağaçtan indirerek kent kapısının dışına attırdı. Cesedin üzerine taşlardan büyük bir yığın yaptılar. Bu yığın bugün de duruyor.
Ya rataye sarkin Ai a kan itace, ya bar shi a can har yamma. Da rana ta fāɗi, Yoshuwa ya umarta a ɗauke gawar sarkin a jefa a gaban ƙofar birnin. Suka kuma tara manyan duwatsu a kan gawar, tsibin na nan har wa yau.
30 Bundan sonra Yeşu Eval Dağı'nda İsrail'in Tanrısı RAB'be bir sunak yaptı.
Yoshuwa kuwa ya yi wa Ubangiji, Allah na Isra’ila bagade a Dutsen Ebal,
31 Sunak, RAB'bin kulu Musa'nın İsrail halkına verdiği buyruk uyarınca, Musa'nın Yasa Kitabı'nda yazıldığı gibi yontulmamış, demir alet değmemiş taşlardan yapıldı. RAB'be orada yakmalık sunular sundular, esenlik kurbanları kestiler.
kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya umarci Isra’ilawa. Ya gina bisa ga abin da yake a rubuce a cikin Littafin Dokoki na Musa, bagade na duwatsun da ba a sassaƙa su ba, waɗanda ba wani ƙarfen da ya taɓa su. Suka miƙa wa Ubangiji hadayu na ƙonawa da hadayu na salama a kai.
32 Yeşu Musa'nın İsrail halkının önünde yazmış olduğu Kutsal Yasa'nın kopyasını orada taş levhalara yazdı.
A can, a gaban Isra’ilawa, Yoshuwa ya rubuta dokokin Musa a kan duwatsun.
33 Bütün İsrailliler, ileri gelenleriyle, görevlileriyle ve hâkimleriyle birlikte –yabancılar dahil– RAB'bin Antlaşma Sandığı'nın iki yanında, yüzleri, sandığı taşıyan Levili kâhinlere dönük olarak dizildiler. Halkın yarısı sırtını Gerizim Dağı'na, öbür yarısı da Eval Dağı'na verdi. Çünkü RAB'bin kulu Musa kutsanmaları için bu şekilde durmalarını daha önce buyurmuştu.
Sai Isra’ilawa duka, da baƙi, da haifaffun gida, da dattawansu, da shugabanninsu, da alƙalansu, suka tsaya a gefe-gefen akwatin alkawarin Ubangiji, suna fuskantar waɗanda suke ɗauke da shi, wato, firistoci waɗanda su ne Lawiyawa. Rabin mutanen suka tsaya a gaban Dutsen Gerizim, rabinsu kuma suka tsaya a gaban Dutsen Ebal, kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya riga ya umarta, cewa su sa wa mutanen Isra’ilawa albarka.
34 Ardından Yeşu yasanın tümünü, kutsama ve lanetle ilgili bölümleri Yasa Kitabı'nda yazılı olduğu gibi okudu.
Bayan haka, Yoshuwa ya karanta duk abin da yake a cikin Dokoki, albarku da la’anoni, kamar yadda suke a rubuce a cikin Littafin Dokoki.
35 Böylece Yeşu'nun, yabancıların da aralarında bulunduğu kadınlı, çocuklu bütün İsrail topluluğuna, Musa'nın buyruklarından okumadığı tek bir söz kalmadı.
Babu wata kalmar da Musa ya umarta da Yoshuwa bai karanta wa dukan taron Isra’ilawa ba, haɗe da mata, da yara, da baƙin da suke zama tare da su.