< Yeşu 6 >
1 Eriha Kenti'nin kapıları İsrailliler yüzünden sımsıkı kapatılmıştı. Ne giren vardı, ne de çıkan.
Ƙofofin Yeriko kuwa a kulle suke ciki da waje saboda Isra’ilawa, ba mai fita babu kuma mai shiga.
2 RAB Yeşu'ya, “İşte Eriha'yı, kralını ve yiğit savaşçılarını senin eline teslim ediyorum” dedi,
Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Duba, na ba ka nasara a kan Yeriko, duk da sarkinta da mayaƙanta.
3 “Siz savaşçılar, kentin çevresini günde bir kez olmak üzere altı gün dolanacaksınız.
Da kai da dukan sojoji, ku zaga birnin sau ɗaya kullum. Ku yi haka har kwana shida.
4 Koç boynuzundan yapılmış birer boru taşıyan yedi kâhin sandığın önünden gitsin. Yedinci gün kentin çevresini yedi kez dolanın; bu arada kâhinler borularını çalsınlar.
Ka sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni raguna su kasance a gaban akwatin alkawari. A rana ta bakwai sai ku zaga birnin sau bakwai, firistocin suna busa ƙahoni.
5 Kâhinlerin koç boynuzu borularını uzun uzun çaldıklarını işittiğinizde, bütün halk yüksek sesle bağırsın. O zaman kentin surları çökecek ve herkes bulunduğu yerden dosdoğru kente girecek.”
Sa’ad da kuka ji sun ɗauki dogon lokaci suna busa ƙaho, sai mutane gaba ɗaya su tā da murya su yi ihu da ƙarfi; katangar birnin kuwa za tă rushe, sai sojoji su haura, ko wanne yă nufi inda ya fuskanta kai tsaye.”
6 Nun oğlu Yeşu kâhinleri çağırıp, “RAB'bin Antlaşma Sandığı'nı alın” dedi, “Yedi kâhin, ellerinde koç boynuzu borularla sandığın önünde yürüsün.”
Yoshuwa ɗan Nun kuwa ya kira firistoci ya ce musu, “Ku ɗauki akwatin alkawari, ku sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni su kasance a gabansa.”
7 Sonra halka, “Kalkın, kentin çevresini dolanmaya başlayın” dedi, “Silahlı öncüler RAB'bin Sandığı'nın önünden gitsin.”
Sai ya umarci jama’a ya ce, “Mu je zuwa! Ku zaga birnin, masu tsaro da makamai su shiga gaban akwatin alkawarin Ubangiji.”
8 Yeşu'nun bunları halka söylemesinden sonra, koç boynuzu birer boru taşıyan yedi kâhin borularını çalarak RAB'bin önünde ilerlemeye başladılar. Onları RAB'bin Antlaşma Sandığı izliyordu.
Da Yoshuwa ya gama yin wa mutane magana, sai firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai a gaban Ubangiji suka sha gaba suna busa ƙahoninsu, akwatin alkawari kuwa yana biye da su.
9 Silahlı öncüler boru çalan kâhinlerin önünden, artçılar da sandığın arkasından ilerliyor, bu arada borular çalınıyordu.
Masu tsaro da makamai kuma suna gaban firistoci waɗanda suke busa ƙahoni, masu tsaro daga baya kuma suna bin akwatin alkawari, ana ta busa ƙahoni.
10 Yeşu halka şu buyruğu verdi: “Savaş naraları atmayın, sesinizi yükseltmeyin. ‘Bağırın’ diyeceğim güne dek ağzınızdan tek bir söz çıkmasın. Buyruğumu duyunca bağırın.”
Amma Yoshuwa ya umarci mutane ya ce, “Kada ku yi kururuwar yaƙi, kada ku tā da murya, kada ku ce kome, sai ranar da na ce ku yi ihu, a sa’an nan ne sai ku yi ihu!”
11 Halk RAB'bin Sandığı'yla birlikte kentin çevresini bir kez dolandı, sonra ordugaha dönüp geceyi orada geçirdi.
Sai ya sa aka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji aka kewaye birnin da shi sau ɗaya, sa’an nan mutane suka dawo masauƙinsu suka kwana a can.
12 Ertesi sabah Yeşu erkenden kalktı. Kâhinler de RAB'bin Sandığı'nı yüklendiler.
Kashegari, Yoshuwa ya tashi da sassafe, firistoci kuma suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji.
13 Koç boynuzu borular taşıyan yedi kâhin RAB'bin Sandığı'nın önünde ilerliyor, bir yandan da borularını çalıyorlardı. Silahlı öncüler onların önünden gidiyor, artçılar da RAB'bin Sandığı'nı izliyordu. Bu arada borular sürekli çalınıyordu.
Firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai suka shiga gaba, suna takawa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji suna kuma busa ƙahoni, masu tsaro ɗauke da makamai suna gabansu, sai masu tsaro da suke baya suna biye da akwatin alkawarin Ubangiji.
14 Böylece ikinci gün de kentin çevresini bir kez dolanıp ordugaha döndüler. Aynı şeyi altı gün yinelediler.
A rana ta biyu suka sāke zaga birnin sau ɗaya, suka kuma koma masauƙinsu. Haka suka yi har kwana shida.
15 Yedinci gün erkenden, şafak sökerken kalkıp kentin çevresini aynı şekilde yedi kez dolandılar. Kentin çevresini yalnız o gün yedi kez dolandılar.
A rana ta bakwai, suka tashi da sassafe suka zaga birnin sau bakwai yadda suka saba. A wannan rana kaɗai ne suka zaga birnin sau bakwai.
16 Kâhinler yedinci turda borularını çalınca, Yeşu halka, “Bağırın! RAB kenti size verdi” dedi,
A zagawa ta bakwai, da firistoci suka busa ƙahoni, sai Yoshuwa ya ba sojojin umarni ya ce, “Ku yi ihu, gama Ubangiji ya ba ku birnin!
17 “Kent, içindeki her şeyle birlikte, RAB'be koşulsuz adanmıştır. Yalnız gönderdiğimiz ulakları saklamış olan fahişe Rahav'la evindekiler sağ bırakılacak.
Birnin da dukan abin da yake cikinta za a miƙa su ga Ubangiji. Rahab karuwan nan kaɗai ce, da dukan waɗanda suke tare da ita a gidanta za a bari da rai domin ta ɓoye’yan leƙen asirin ƙasa da muka aika.
18 Sakın RAB'be adanan herhangi bir şeye el sürmeyin. Adadığınız şeyleri alırsanız İsrail'in ordugahını felakete ve yıkıma sürüklersiniz.
Amma, ba za ku ɗauki wani abin da za a hallaka ba, idan kuka yi haka, za ku jawo masifa da hallaka a kan mutanen Isra’ila a inda kuka sauka.
19 Bütün altınla gümüş, tunç ve demir eşya RAB'be ayrılmıştır. Bunlar RAB'bin hazinesine girecek.”
Dukan azurfa da zinariya, da kwanonin tagulla da na ƙarfe, keɓaɓɓu ne ga Ubangiji, dole a sa su cikin ma’ajin Ubangiji.”
20 Halk bağırmaya başladı, kâhinler de borularını çaldılar. Boru sesini işiten halk daha yüksek sesle bağırdı. Kentin surları çöktü. Herkes bulunduğu yerden dosdoğru kente girdi. Böylece kenti ele geçirdiler.
Da aka busa ƙahoni, sojoji suka yi ihu, da jin ƙarar ƙahoni, mutane suka kuma yi ihu, sai katangar ta rushe; dukan mutanen kuwa suka shiga birnin kai tsaye, suka yi nasara a kanta.
21 Kadın erkek, genç yaşlı, küçük ve büyük baş hayvanlardan eşeklere dek, kentte ne kadar canlı varsa, hepsini kılıçtan geçirip yok ettiler.
Suka miƙa wa Ubangiji birnin, suka hallaka kowane abu mai ran da yake cikin birnin da takobi, maza da mata, yara da tsofaffi, shanu, tumaki da jakuna.
22 Yeşu ülkeye casus olarak gönderdiği iki adama, “O fahişenin evine gidin, ant içtiğiniz gibi, kadını ve bütün yakınlarını dışarı çıkarın” dedi.
Yoshuwa ya ce wa mutanen nan biyu waɗanda suka je leƙen asirin ƙasar, “Ku shiga gidan karuwan nan ku fitar da ita da duk waɗanda suke nata bisa ga alkawarin da kuka yi mata.”
23 Eve giren genç casuslar Rahav'ı, annesini, babasını, erkek kardeşleriyle bütün akrabalarını ve kendisine ait olan her şeyi alıp İsrail ordugahının yakınına getirdiler.
Sai samarin waɗanda suka je leƙen asirin suka shiga suka fitar da Rahab, mahaifinta da mahaifiyarta, da’yan’uwanta da duk abin da yake nata. Suka fitar da iyalinta gaba ɗaya suka sa su a wani wuri, ba a cikin masauƙin Isra’ilawa ba.
24 Sonra kenti içindekilerle birlikte ateşe verdiler. Ancak altını ve gümüşü, tunç ve demir eşyayı RAB'bin Tapınağı'nın hazinesine koydular.
Sa’an nan suka ƙona birnin tare da dukan abin da yake ciki tatas, amma suka sa azurfa da zinariya da kayan tagulla da na ƙarfe a cikin ma’aji na haikalin Ubangiji.
25 Yeşu fahişe Rahav'a, babasının ev halkıyla yakınlarına dokunmadı. Yeşu'nun Eriha'yı araştırmak için gönderdiği ulakları saklayan Rahav, bugün de İsrailliler'in arasında yaşıyor.
Amma Yoshuwa ya bar Rahab karuwan nan bai kashe ta ba, ita da iyalinta da duk abin da yake nata, domin ita ta ɓoye mutanen da Yoshuwa ya aika Yeriko don su leƙo asirin ƙasar kuma ta zauna tare da Isra’ilawa har wa yau.
26 Bundan sonra Yeşu şöyle ant içti: “Bu kenti, Eriha'yı yeniden kurmaya kalkışan, RAB'bin lanetine uğrasın. Buna kalkışan kişi büyük oğlunu kaybetme pahasına temel atacak, en küçük oğlunu kaybetme pahasına da kentin kapılarını yerine takacak.”
A lokacin nan Yoshuwa ya yi wannan alkawari cewa, “Ubangiji zai tsine wa mutumin da zai yi ƙoƙarin sāke gina birnin nan, Yeriko. “A bakin ran ɗan farinsa zai kafa harsashin birnin; a bakin ran ɗan autansa kuma zai sa ƙofofin birnin.”
27 RAB Yeşu'yla birlikteydi. Yeşu'nun ünü ülkenin her yanına yayıldı.
Ubangiji ya kasance tare da Yoshuwa, aka kuma san da shi a duk fāɗin ƙasar.