< Eyüp 27 >
1 Eyüp anlatmaya devam etti:
Ayuba kuwa ya ci gaba da magana,
2 “Hakkımı elimden alan Tanrı'nın varlığı hakkı için, Bana acı çektiren Her Şeye Gücü Yeten'in hakkı için,
“Na rantse da Allah mai rai, wanda ya danne mini gaskiyata, Maɗaukaki, wanda ya sa nake cikin ɗacin rai.
3 İçimde yaşam belirtisi olduğu sürece, Tanrı'nın soluğu burnumda olduğu sürece,
Muddin ina da rai a cikina kuma numfashin Allah yana cikin hancina,
4 Ağzımdan kötü söz çıkmayacak, Dilimden yalan dökülmeyecek.
bakina ba zai faɗi mugun abu ba, harshena kuma ba zai yi ƙarya ba.
5 Size asla hak vermeyecek, Son soluğumu verene dek suçsuz olduğumu söyleyeceğim.
Ba zan taɓa yarda cewa kuna da gaskiya ba; har in mutu, ba zan daina kāre mutuncina ba.
6 Doğruluğuma sarılacak, onu bırakmayacağım, Yaşadığım sürece vicdanım beni suçlamayacak.
Zan ci gaba da adalcina, ba zan fasa ba; lamirina ba zai taɓa yashe ni ba, dukan kwanakin raina.
7 “Düşmanlarım kötüler gibi, Bana saldıranlar haksızlar gibi cezalandırılsın.
“Bari maƙiyana su zama kamar mugaye, masu gāba da ni kuma su zama kamar marasa adalci.
8 Tanrısız insanın umudu nedir Tanrı onu yok ettiğinde, canını aldığında?
Gama wane bege marar tsoron Allah yake da shi, lokacin da aka datse shi, lokacin da Allah ya ɗauke ransa?
9 Başına sıkıntı geldiğinde, Tanrı feryadını duyar mı?
Ko Allah yana sauraron kukansa lokacin da ƙunci ya auko masa?
10 Her Şeye Gücü Yeten'den zevk alır mı? Her zaman Tanrı'ya yakarır mı?
Ko zai sami farin ciki daga Maɗaukaki? Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?
11 “Tanrı'nın gücünü size öğreteceğim, Her Şeye Gücü Yeten'in tasarısını gizlemeyeceğim.
“Zan koya muku game da ikon Allah; ba zan ɓoye hanyoyin Maɗaukaki ba.
12 Aslında siz, hepiniz gördünüz bunu, Öyleyse ne diye boş boş konuşuyorsunuz?
Duk kun ga wannan ku da kanku saboda haka me ya sa kuke maganganun nan marasa ma’ana?
13 “Kötünün Tanrı'dan alacağı pay, Zorbanın Her Şeye Gücü Yeten'den alacağı miras şudur:
“Ga abin da mugaye za su samu gādon da azzalumi zai samu daga Maɗaukaki.
14 Çocukları ne kadar çok olursa olsun, kılıçla öldürülecek, Soyu yeterince ekmek bulamayacaktır.
Kome yawan’ya’yansa, takobi za tă gama da su; zuriyarsa ba za su taɓa samun isashen abinci ba.
15 Sağ kalanlar hastalıktan ölüp gömülecek, Dul karıları ağlamayacaktır.
Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.
16 Kötü insan kum gibi gümüş yığsa, Yığınla giysi biriktirse,
Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,
17 Onun biriktirdiğini doğru insan giyecek, Gümüşü suçsuz paylaşacak.
abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.
18 Evini güve kozası gibi inşa eder, Bekçinin kurduğu çardak gibi.
Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.
19 Zengin olarak yatar, ama bu öyle sürmez, Gözlerini açtığında hepsi yok olup gitmiştir.
Attajiri zai kwanta, amma daga wannan shi ke nan; lokacin da zai buɗe idanunsa, kome ya tafi.
20 Dehşet onu sel gibi basar, Kasırga gece kapar götürür.
Tsoro zai kwashe shi kamar ambaliyar ruwa; Da dare iska za tă tafi da shi.
21 Doğu rüzgarı onu uçurup götürür, Yerinden silip süpürür.
Iskar gabas za tă tafi da shi; shi ke nan ya ƙare; za tă share shi daga wurinsa.
22 Acımasızca üzerine eser, Elinden kaçmaya çalışırken.
Za tă murɗe shi ba tausayi, lokacin da yake guje wa ikon iskar.
23 Onunla alay ederek el çırpar, Yerinden ıslık çalar.”
Zai tafa hannu yă yi tsaki yă kawar da shi daga wurinsa.”