< Yeremya 5 >
1 “Yeruşalim sokaklarında dolaşın, Çevrenize bakıp düşünün, Kent meydanlarını araştırın. Eğer adil davranan, Gerçeği arayan bir kişi bulursanız, Bu kenti bağışlayacağım.
“Ku yi ta kai da kawowa a titunan Urushalima, ku dudduba ko’ina ku kuma lura, ku bincika cikin dandalinta. Ko za ku sami mutum guda wanda yake aikata adalci wanda yake kuma son bin gaskiya, sai in gafarta wa wannan birni.
2 ‘RAB'bin varlığı hakkı için’ deseler de, Aslında yalan yere ant içiyorlar.”
Ko da yake suna cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye,’ duk da haka suna rantsuwar ƙarya.”
3 Ya RAB, gözlerin gerçeği arıyor. Onları vurdun, ama incinmediler, Onları yiyip bitirdin, Ama yola gelmeyi reddettiler. Yüzlerini kayadan çok sertleştirdiler, Geri dönmek istemediler.
Ya Ubangiji, idanunka ba sa ganin gaskiya? Ka buge su, amma ba su ji zafi ba; ka ragargaza su, amma suka ƙi su gyara. Fuskarsu ta ƙeƙashe fiye da dutse suka ƙi su tuba.
4 “Bunlar sadece yoksul kişiler, Akılsızlar” dedim, “Çünkü RAB'bin yolunu, Tanrıları'nın buyruklarını bilmiyorlar.
Na yi tunani, “Waɗannan ne kawai matalauta; su wawaye ne, gama ba su san hanyar Ubangiji ba, ko abubuwan da Allahnsu yake bukata ba.
5 Büyüklere gidip onlarla konuşayım. RAB'bin yolunu, Tanrıları'nın buyruklarını bilirler kuşkusuz.” Gelgelelim onlar da boyunduruğu kırmış, Bağları koparmıştı.
Saboda haka zan tafi wurin shugabanni in yi musu magana; tabbatacce sun san hanyar Ubangiji, da abubuwan da Allahnsu yake bukata.” Amma da nufi guda su ma suka karye karkiyar suka tsintsinke sarƙoƙin.
6 Bu yüzden ormandan bir aslan çıkıp onlara saldıracak, Çölden gelen bir kurt onları parça parça edecek, Bir pars kentlerinin önünde pusu kuracak, Oradan çıkan herkes parçalanacak. Çünkü isyanları çok, Döneklikleri sayısızdır.
Saboda haka zaki daga kurmi zai fāɗa musu, kyarkeci kuma daga hamada zai cinye su, damisa za tă yi musu ƙawanya kusa da garuruwansu yă yayyage duk wanda ya kuskura ya fita, gama tawayensu da girma yake jan bayansu kuma yana da yawa.
7 “Yaptıklarından ötürü neden bağışlayayım seni? Çocukların beni terk etti, Tanrı olmayan ilahların adıyla ant içtiler. Onları doyurduğumda zina ettiler, Fahişelerin evlerine doluştular.
“Me zai sa in gafarta muku?’Ya’yanku sun yashe ni sun yi rantsuwa da allolin da ba alloli ba ne. Na biya musu dukan bukatunsu, duk da haka suka yi zina suka tattaru a gidajen karuwai.
8 Şehvet düşkünü, besili aygırlar! Her biri komşusunun karısına kişniyor.
An ciyar da su sosai, kamar ƙosassun ingarmu, masu jaraba, kowanne yana haniniya, yana neman matar maƙwabcinsa.
9 Bu yüzden onları cezalandırmayayım mı?” diyor RAB, “Böyle bir ulustan öcümü almayayım mı?
Ba zan hukunta su saboda wannan ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata in yi ramuwa a kan irin al’ummar nan ba?
10 “Bağlarını dolaşıp Asmalarını kesin, Ama büsbütün yok etmeyin. Dallarını koparıp atın, Çünkü onlar RAB'be ait değil.
“Ku ratsa cikin gonakin inabinta ku cinye su, amma kada ku hallaka su gaba ɗaya. Ku kakkaɓe rassanta, gama waɗannan mutane ba na Ubangiji ba ne.
11 İsrail ve Yahuda halkı Bana sürekli ihanet etti” diyor RAB.
Gidan Isra’ila da gidan Yahuda sun zama marasa aminci gaba ɗaya gare ni” in ji Ubangiji.
12 RAB için yalan söyleyerek, “O bir şey yapmaz. Felaket bize uğramayacak, Kılıç da kıtlık da görmeyeceğiz” dediler.
Sun yi ƙarya a kan Ubangiji; sun ce, “Ba zai yi kome ba! Ba wata masifar da za tă same mu; ba za mu taɓa ganin takobi ko yunwa ba.
13 Peygamberler lafebesidir, Tanrı'nın sözü onlarda değil. Onlara böyle yapılacak.
Annabawa holoƙo ne kawai maganar kuwa ba ta cikinsu; saboda haka bari abin da suke faɗi ya koma kansu.”
14 Bu yüzden, Her Şeye Egemen RAB Tanrı diyor ki, “Madem böyle şeyler konuşuyorsunuz, Ben de sözümü ağzınıza ateş, Bu halkı da odun edeceğim; Ateş onları yakıp yok edecek.
Saboda haka ga abin Ubangiji Allah Maɗaukaki yana cewa, “Domin mutanen sun yi waɗannan maganganu, zan mai da maganata a bakinku wuta waɗannan mutane kuwa su zama itacen da za tă ci.
15 Ey İsrail halkı, Uzaktan gelecek bir ulusu Üzerinize saldırtacağım” diyor RAB, “Köklü, eski bir ulus; Sen onların dilini bilmez, Ne dediklerini anlamazsın.
Ya gidan Isra’ila,” in ji Ubangiji, “Ina kawo al’umma daga nesa a kanku al’umma ce ta tun dā mai ƙarfin hali, mutane ne da ba ku san harshensu ba, waɗanda ba za ku fahimci abin da suke faɗa ba.
16 Oklarının kılıfı açık bir mezar gibidir, Hepsi birer yiğittir.
Kwarinsu kamar buɗaɗɗen kabari ne; dukansu jarumawa ne.
17 Ürününü, yiyeceklerini tüketecek, Oğullarını, kızlarını öldürecekler; Davarlarını, sığırlarını, Asmalarının, incir ağaçlarının meyvesini yiyecek, Güvendiğin surlu kentlerini Kılıçla yerle bir edecekler.
Za su cinye amfanin gonakinku da abincinku, za su cinye’ya’yanku maza da mata; za su cinye garkunan tumakinku da na awakinku, za su cinye’ya’yan inabinku da na ɓaurenku. Da takobi za su hallaka biranenku masu katanga.
18 “Ama o günlerde bile sizi büsbütün yok etmeyeceğim” diyor RAB.
“Amma ko a cikin waɗancan kwanaki,” in ji Ubangiji, “ba zan hallaka ku gaba ɗaya ba.
19 “‘Tanrımız RAB neden bize bütün bunları yaptı?’ diye sorduklarında, şöyle yanıtlayacaksın: ‘Beni nasıl bıraktınız, ülkenizde yabancı ilahlara nasıl kulluk ettinizse, siz de kendinize ait olmayan bir ülkede yabancılara öyle kulluk edeceksiniz.’
Sa’ad da kuma mutanen suka yi tambaya, ‘Me ya sa Ubangiji Allahnmu ya yi dukan wannan gare mu?’ Sai ka amsa musu, ‘Yadda kuka yashe ni kuka kuma bauta wa baƙin alloli a ƙasarku, haka yanzu za ku bauta wa baƙi a ƙasar da ba taku ba.’
20 “Yakup soyuna bildirin, Yahuda halkına duyurun:
“Ka sanar da wannan ga gidan Yaƙub ka yi shelarsa a Yahuda.
21 Ey gözleri olan ama görmeyen, Kulakları olan ama işitmeyen, Sağduyudan yoksun akılsız halk, Şunu dinle:
Ku ji wannan, ku wawaye marasa azanci, waɗanda suke da idanu amma ba sa gani, waɗanda suke da kunnuwa amma ba sa ji.
22 Benden korkman gerekmez mi?” diyor RAB, “Huzurumda titremen gerekmez mi? Ben ki, sonsuza dek geçerli bir kuralla Denize sınır olarak kumu koydum. Deniz sınırı geçemez; Dalgalar kabarsa da üstün gelemez, Kükrese de sınırı aşamaz.
Bai kamata ku ji tsorona ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata ku yi rawar jiki a gabana ba? Na sa yashi ya zama iyakar teku, madawwamiyar iyakar da ba zai tsallake ba. Raƙuman ruwa za su iya yin hauka, amma ba za su iya haye ta ba; za su iya yin ruri, amma ba za su iya ƙetare ta ba.
23 Ama bu halkın yüreği asi ve inatçı. Sapmışlar, kendi yollarına gitmişler.
Amma mutanen nan suna da tauraren zukata, kuma’yan tawaye ne; sun kauce suka kuma rabu da ni.
24 İçlerinden, ‘İlk ve son yağmurları zamanında yağdıran, Belli ürün biçme haftalarını bizim için koruyan Tanrımız RAB'den korkalım’ demiyorlar.
Ba sa faɗa wa kansu, ‘Bari mu ji tsoron Ubangiji Allahnmu, wanda yake ba mu ruwan sama a kan kari na kaka da na bazara, wanda kullum yake tabbatar mana da girbi.’
25 Bunları uzaklaştıran suçlarınızdı, Bu iyilikten sizi yoksun bırakan günahlarınızdı.
Laifofinku sun raba ku da waɗannan abubuwa; zunubanku sun hana ku samun alheri.
26 “Halkım arasında kötü kişiler var. Kuş avlamak için pusuya yatanlar gibi Tuzak kuruyor, insan yakalıyorlar.
“A cikin mutanena an sami mugaye waɗanda suke kwanton ɓauna kamar masu sa tarko wa tsuntsaye kamar waɗanda suke kafa tarko don su kama mutane.
27 Kuş dolu bir kafes nasılsa, Onların evleri de hileyle dolu. Bu sayede güçlenip zengin oldular,
Kamar keji cike da tsuntsaye, gidajensu sun cika da ruɗu; sun yi arziki suka kuma zama masu iko
28 Semirip parladılar, Yaptıkları kötülüklerle sınırı aştılar. Kazanabilecekleri halde öksüzün davasına bakmıyor, Yoksulun hakkını savunmuyorlar.
suka kuma yi ƙiba, suka yi bul-bul. Mugayen ayyukansu ba su da iyaka; ba sa wa marayu shari’ar adalci, ba sa kāre’yancin matalauta.
29 Bu yüzden onları cezalandırmayayım mı?” diyor RAB, “Böyle bir ulustan öcümü almayayım mı?
Bai kamata in hukunta su saboda wannan ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata in yi ramuwa a kan irin al’umma kamar wannan ba?
30 “Ülkede korkunç, dehşet verici bir şey oldu:
“Abin banmamaki da bantsoro ya faru a ƙasar.
31 Peygamberler yalan peygamberlik ediyor, Halkı başına buyruk kâhinler yönetiyor, Halkım da bunu benimsiyor. Ama bunun sonunda ne yapacaksınız?”
Annabawa suna annabcin ƙarya, firistoci suna mulki da ikon kansu, mutanena kuma suna son haka. Amma me za ku yi a ƙarshe?