< Yeşaya 5 >
1 Sevgilimin bağı için yaktığı ezgiyi sevgilim için okuyayım: Toprağı verimli bir tepede Sevgilimin bir bağı vardı.
Zan rera waƙa wa ƙaunataccena waƙa game da gonar inabinsa. Ƙaunataccena yana da gonar inabi a gefen tudu mai dausayi.
2 Toprağı belleyip taşları ayıkladı, Seçme asmalar dikip orta yere bir gözcü kulesi yaptı. Üzüm sıkmak için bir çukur kazdı Ve bağının üzüm vermesini bekledi. Ama bağ yabanıl üzüm verdi.
Ya haƙa ƙasa ya kuma tsintsince duwatsun ya shuka mata inabi mafi kyau. Ya gina hasumiyar tsaro a cikinta ya kuma shirya wurin matsin ruwan inabi. Sa’an nan ya sa rai ga samun girbi mai kyau na inabin, amma sai ga shi inabin ya ba da munanan’ya’ya.
3 Sevgilim diyor ki, “Ey Yeruşalim'de yaşayanlar ve Yahuda halkı, lütfen benimle bağım arasında hakem olun!
“Yanzu fa ku mazauna cikin Urushalima da mutanen Yahuda, ku shari’anta tsakanina da gonar inabina.
4 Bağım için yapmadığım ne kaldı? Ben üzüm vermesini beklerken niçin yabanıl üzüm verdi?
Me kuma ya rage da za a yi wa gonar inabina fiye da abin da na yi mata? Da na nemi inabi masu kyau, me ya sa ta ba da munana’ya’ya?
5 Şimdi bağıma ne yapacağımı size söyleyeyim: Çitini söküp atacağım, varsın yiyip bitirsinler; duvarını yıkacağım, varsın çiğnesinler.
Yanzu zan faɗa muku abin da zan yi da gonar inabina. Zan cire katangar da ta kewaye ta, za tă kuwa lalace; zan rushe bangonta, za a kuwa tattake ta.
6 Viraneye çevireceğim onu; budanmayacak, çapalanmayacak; dikenli çalılar bitecek her yanında. Üzerine yağmur yağdırmasınlar diye bulutlara buyruk vereceğim.”
Zan mai da ita kango, ba zan aske ta ba, ba kuwa zan nome ta ba, sarƙaƙƙiya da ƙayayyuwa kuwa za su yi girma a can Zan umarci gizagizai kada su yi ruwan sama a kanta.”
7 Her Şeye Egemen RAB'bin bağı İsrail halkı, Hoşlandığı fidan da Yahuda halkıdır. RAB adalet bekledi, Zorbalık gördü; Doğruluk bekledi, Feryatlar duydu.
Gonar inabin Ubangiji Maɗaukaki ita ce gidan Isra’ila, mutanen Yahuda kuma su ne lambun farin cikinsa. Yana kuma nema ganin gaskiya, amma sai ga zub da jini; yana neman adalci, amma sai ga shi kukan azaba yake ji.
8 Evlerine ev, tarlalarına tarla katanların vay haline! Oturacak yer kalmadı, Ülkede bir tek siz oturuyorsunuz.
Kaitonku ku waɗanda kuke ƙara wa kanku gidaje kuke kuma haɗa gonaki da gonaki har babu sauran filin da ya rage ku kuma zauna ku kaɗai a ƙasar.
9 Her Şeye Egemen RAB'bin şöyle ant içtiğini duydum: “Büyük ve gösterişli çok sayıda ev ıssız kalacak, İçinde oturan olmayacak.
Ubangiji Maɗaukaki ya furta a kunnuwana, “Tabbatacce manyan gidajen za su zama kango, za a bar kyawawan gidajen nan ba kowa.
10 Çünkü on dönümlük bağ ancak bir bat şarap, Bir homer tohum ancak bir efa tahıl üretecek.”
Kadada goma na gonar inabi zai ba da garwan ruwan inabi ɗaya kaɗai, mudu guda na iri kuma zai ba da efa na hatsi guda kurum.”
11 Sabah erkenden kalkıp içki peşinden koşanların, gece geç vakte kadar şarap içip kızışanların vay haline!
Kaiton waɗanda suke tashi da sassafe don su nufi wurin shaye-shaye, waɗanda suke raba dare har sai sun bugu da ruwan inabi.
12 Onların şölenlerinde lir, çenk, tef ve kaval çalınır, şarap içilir. Ama RAB'bin yaptıklarına dikkat etmez, ellerinin yapıtına aldırmazlar.
Suna kaɗa garaya, da molaye a bukukkuwansu, ganguna da busa da ruwan inabi, amma ba su kula da ayyukan Ubangiji ba, ba sa biyayya ga aikin hannuwansa.
13 Halkım bilgisizliği yüzünden sürgün edilecek; saygın kişileri kıtlıktan ölecek, kalabalıklar susuzluktan kırılacak.
Saboda haka mutanena za su yi zaman bauta domin rashin fahimi; manyan mutanensu za su mutu da yunwa talakawansu kuma su mutu da ƙishirwa.
14 Bu yüzden doymak bilmeyen ölüler diyarı ağzını ardına kadar açtı; Yeruşalim'in soyluları, sıradan insanları ve gürültülü bir şekilde eğlenenleri oraya inecek. (Sheol )
Saboda haka kabari ya fadada marmarinsa ya kuma buɗe bakinsa babu iyaka; cikinsa manyan mutanensu da talakawansu za su gangara tare da dukan masu hayaniyarsu da masu murnansu. (Sheol )
15 Hepsi alçaltılacak; dize getirilecek, küstah bakışları alçaltılacak.
Ta haka za a ƙasƙantar da mutum kuma za a ƙasƙantar da’yan adam, za a ƙasƙanta da masu girman kai.
16 Ama Her Şeye Egemen RAB adaletinden ötürü yüceltilecek. Kutsal Tanrı doğruluğuyla kutsal olduğunu gösterecek.
Amma Ubangiji Maɗaukaki zai sami ɗaukaka ta wurin aikata gaskiya, kuma Allah mai tsarki zai nuna kansa ta wurin adalcinsa.
17 Kuzular kendi otlaklarındaymış gibi otlayacak, zenginlerin ıssız kalan konutlarını yabancılar ele geçirecek.
Sa’an nan tumaki za su yi kiwo kamar yadda suke yi a wurin kiwonsu; raguna za su yi kiwo cikin abubuwa masu kyau da suka lalace.
18 Suçu yalanla örülmüş iplerle, günahı araba urganıyla çekenlerin vay haline!
Kaiton waɗanda suke jan zunubi da igiyar ruɗu, da kuma mugunta da igiyoyin keken yaƙin,
19 Diyorlar ki, “Tanrı elini çabuk tutup işini hızlandırsın da görelim. İsrail'in Kutsalı tasarladığını yapsın da görelim.”
waɗanda suke cewa, “Bari Allah yă gaggauta, bari yă hanzarta aikinsa don mu gani. Bari yă iso, bari shirin Mai Tsarkin nan na Isra’ila yă zo, don mu sani.”
20 Kötüye iyi, iyiye kötü diyenlerin, karanlığı ışık, ışığı karanlık yerine koyanların, acıya tatlı, tatlıya acı diyenlerin vay haline!
Kaiton waɗanda suke ce da mugunta nagarta nagarta kuma mugunta, waɗanda suke mai da duhu haske haske kuma duhu, waɗanda suke mai da ɗaci zaƙi zaƙi kuma ɗaci.
21 Kendilerini bilge görenlerin, akıllı sananların vay haline!
Kaiton waɗanda suke tsammani suna da hikima da kuma wayo a idonsu.
22 Şarap içmekte sınır tanımayanların, içkileri karıştırıp içmekten çekinmeyenlerin, rüşvet uğruna kötüyü haklı çıkaranların, haklıların hakkını elinden alanların vay haline!
Kaiton waɗanda suke jarumawa a shan ruwan inabi da gwanaye a haɗin abubuwan sha,
waɗanda suke ƙyale masu laifi don sun ba da cin hanci, amma su hana a yi gaskiya wa marasa laifi.
24 Alev alev yanan ateş, samanı nasıl yiyip bitirirse, kuru ot alevin içinde nasıl birden tutuşup yok olursa, onlar da kökten çürüyüp gidecek, çiçekleri toz gibi havaya savrulacak. Çünkü Her Şeye Egemen RAB'bin yasasını reddettiler, İsrail'in Kutsalı'nın sözlerini küçümsediler.
Saboda haka kamar yadda harshen wuta yakan lashe kara kuma kamar yadda busasshiyar ciyawa takan ƙone ƙurmus a cikin wuta, haka saiwarsu za su ruɓa iska kuma ta hura furanninsu kamar ƙura; gama sun ƙi dokar Ubangiji Maɗaukaki suka kuma ƙyale maganar Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
25 Bu yüzden RAB'bin halkına karşı öfkesi alevlendi, elini kaldırıp onları vurdu. Dağlar titriyor, cesetler çöp gibi sokaklara serildi. Bütün bunlara karşın RAB'bin öfkesi dinmedi, eli hâlâ kalkmış durumda.
Saboda haka fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kan mutanensa; ya ɗaga hannunsa ya kuma buge su. Duwatsu sun jijjigu, gawawwaki kuwa suka zama kamar juji a tituna. Saboda wannan duka, fushinsa bai huce ba, bai kuwa janye hannunsa ba.
26 RAB uzaktaki ulusları bir sancak işaretiyle, dünyanın en uzağındakileri ıslık sesiyle çağıracak; hızla, hemen gelecekler.
Ya ɗaga tuta don al’ummai masu nisa, ya yi feɗuwa wa waɗanda suke a iyakar duniya. Ga shi sun iso, da sauri da kuma gaggawa!
27 Aralarında yorulan, sendeleyen olmayacak; uyuklamayacak, uyumayacaklar. Gevşek kemer, kopuk çarık bağı olmayacak.
Babu ko ɗayansu da ya gaji ko ya yi tuntuɓe, babu ko ɗaya da ya yi gyangyaɗi ko barci; babu abin ɗamarar da ya kunce a gindi, ba igiyar takalmin da ta tsinke.
28 Okları sivri, yayları kuruludur. Atlarının toynakları çakmaktaşı, arabalarının tekerlekleri kasırga gibidir.
Kibiyoyinsu masu tsini ne, an ɗaura dukan bakkunansu; kofatan dawakansu sun yi kamar dutsen ƙanƙara, ƙafafun keken yaƙinsu kamar guguwa ne.
29 Askerleri dişi aslan gibi, genç aslanlar gibi kükrüyor, homurdanarak avlarını kapıp götürüyorlar. Kimse avlarını pençelerinden kurtaramıyor.
Rurinsu ya yi kamar na zaki, suna ruri kamar’yan zakoki; suna yin gurnani yayinda suke kamun abin da suke farauta su ɗauke shi ba mai ƙwace shi.
30 O gün İsrail'e karşı denizin gürleyişi gibi gürleyecekler. Karaya bakan biri karanlık ve sıkıntı görecek. Işık karanlık bulutlarla kaplanacak.
A wannan rana za su yi ta ruri a kansa kamar rurin teku. Kuma in wani ya dubi ƙasar, zai ga duhu da damuwa; haske ma zai zama duhu ta wurin gizagizai.