< Yeşaya 38 >
1 O günlerde Hizkiya ölümcül bir hastalığa yakalandı. Amots oğlu Peygamber Yeşaya ona gidip şöyle dedi: “RAB diyor ki, ‘Ev işlerini düzene sok. Çünkü iyileşmeyecek, öleceksin.’”
A kwanakin nan sai Hezekiya ya kamu da ciwo ya kuma kusa ya mutu. Annabi Ishaya ɗan Amoz ya tafi wurinsa ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce ka shirya gidanka, domin za ka mutu; ba za ka warke ba.”
2 Hizkiya yüzünü duvara dönüp RAB'be yalvardı:
Hezekiya ya juye fuskarsa wajen bango ya kuma yi addu’a ga Ubangiji,
3 “Ya RAB, yürekten bir sadakatle önünde nasıl yaşadığımı, gözünde iyi olanı yaptığımı anımsa lütfen.” Sonra acı acı ağlamaya başladı.
“Ka tuna, ya Ubangiji, yadda na yi tafiya a gabanka da aminci da dukan zuciya na kuma yi abin da yake nagari a idanunka.” Sai Hezekiya ya yi kuka mai zafi.
4 Bunun üzerine RAB Yeşaya'ya seslendi:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Ishaya cewa,
5 “Git, Hizkiya'ya şunu söyle: ‘Atan Davut'un Tanrısı RAB diyor ki: Duanı işittim, gözyaşlarını gördüm. Bak, ömrünü on beş yıl daha uzatacağım.
“Ka tafi ka faɗa wa Hezekiya, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na kakanka Dawuda, ya ce na ji addu’arka na kuma ga hawayenka; zan ƙara maka shekaru goma sha biyar ga rayuwarka.
6 Bu kenti savunacak, seni de kenti de Asur Kralı'nın elinden kurtaracağım.
Zan kuwa cece ka da wannan birni daga hannun sarkin Assuriya. Zan kiyaye wannan birni.
7 Sözümü gerçekleştireceğime ilişkin sana vereceğim belirti şu olacak:
“‘Ga alamar Ubangiji gare ka cewa Ubangiji zai aikata kamar yadda ya yi alkawari.
8 RAB, batmakta olan güneşin Ahaz'ın inşa ettiği basamakların üzerine düşen gölgesini on basamak kısaltacak.’” Böylece batmakta olan güneşin gölgesi on basamak kısaldı.
Zan sa inuwar da rana ta yi a kan matakalar Ahaz ta koma baya da taki goma.’” Saboda haka inuwar ta koma da baya daga fuskar rana har taki goma.
9 Yahuda Kralı Hizkiya hastalanıp iyileştikten sonra şunları yazdı:
Rubutun Hezekiya sarkin Yahuda bayan ciwonsa da kuma warkarwarsa.
10 “Hayatımın baharında ölüler diyarının kapılarından geçip Ömrümün geri kalan yıllarından yoksun mu kalmalıyım?” demiştim, (Sheol )
Na ce, “Cikin tsakiyar rayuwata dole in bi ta ƙofofin mutuwa a kuma raba ni da sauran shekaruna?” (Sheol )
11 “Yaşayanlar diyarında RAB'bi, evet, RAB'bi bir daha görmeyeceğim, Bu dünyada yaşayanlar gibi insan yüzü görmeyeceğim bir daha.
Na ce, “Ba zan ƙara ganin Ubangiji ba, Ubangiji a ƙasa ta masu rai; ba zan ƙara ga wani mutum, ko in kasance tare da waɗanda suke zama a wannan duniya ba.
12 Evim bir çoban çadırı gibi bozuldu, alındı elimden. Dokumacı gibi dürdüm yaşamımı, RAB tezgahtan beni kesti, Bir gün içinde sonumu getiriverdi.
Kamar tentin makiyayi an rushe gidana aka kuma ƙwace ta daga gare ni. Kamar mai saƙa, na nannaɗe rayuwata, ya kuma yanke ni daga sandar saƙa; dare da rana ka kawo ni ga ƙarshe.
13 Sabırla bekledim sabaha kadar, RAB bir aslan gibi kırdı bütün kemiklerimi, Bir gün içinde sonumu getiriverdi.
Na yi jira da haƙuri har safiya, amma kamar zaki ya kakkarya ƙasusuwana duka; dare da rana ka kawo ni ga ƙarshe.
14 Kırlangıç gibi, turna gibi acı acı öttüm, Güvercin gibi inledim, gözlerim yoruldu yukarı bakmaktan. Ya Rab, eziyet çekiyorum, Yardım et bana.
Na yi kuka kamar mashirare ko zalɓe, na yi kuka kamar kurciya mai makoki. Idanuna suka rasa ƙarfi yayinda na duba sammai. Na damu; Ya Ubangiji, ka taimake ni!”
15 “Ne diyeyim? Bana seslenen de bunu yapan da Rab'dir. Tattığım bu acılardan sonra daha dikkatli yaşayacağım.
Amma me zan ce? Ya riga ya yi mini magana, shi kansa ne kuma ya aikata. Zan yi tafiya da tawali’u dukan kwanakina saboda wahalar raina.
16 Ya Rab, insanlar bunlarla yaşarlar. Canım da bunların sayesinde yaşıyor. İyileştirdin, yaşattın beni!
Ubangiji, ta waɗannan abubuwa ne mutane suke rayuwa; ruhuna kuma yana samun rai a cikinsu shi ma. Ka maido mini da lafiya ka kuma sa na rayu.
17 Çektiğim bunca acı esenlik bulmam içindi. Beni sevdiğin için yıkım çukuruna düşmekten alıkoydun, Günahlarımı arkana attın.
Tabbatacce wannan kuwa saboda ribata ne cewa in sha irin wahalan nan. Cikin ƙaunarka ka kiyaye ni daga ramin hallaka; ka sa dukan zunubaina a bayanka.
18 Çünkü ölüler diyarı sana şükredemez, Ölüm övgüler sunmaz sana. Ölüm çukuruna inenler senin sadakatine umut bağlayamaz. (Sheol )
Gama kabari ba zai yabe ka ba, matattu ba za su rera yabonka ba; waɗanda suka gangara zuwa rami ba za su sa zuciya ga amincinka ba. (Sheol )
19 Diriler, yalnız diriler Bugün benim yaptığım gibi sana şükreder; Babalar senin sadakatini çocuklarına anlatır.
Masu rai, masu rai, su suke yabonka, kamar yadda nake yi a yau; iyaye za su faɗa wa’ya’yansu game da amincinka.
20 Beni kurtaracak olan RAB'dir. Ömrümüz boyunca O'nun tapınağında Telli çalgılarımızı çalacağız.”
Ubangiji zai cece ni, za mu kuma rera da kayan kiɗi masu tsirkiya dukan kwanakinmu a cikin haikalin Ubangiji.
21 Yeşaya, “İncir pestili getirin, Hizkiya'nın çıbanına koyun, iyileşir” demişti.
Ishaya ya riga ya ce, “Ku shirya curin da aka yi da’ya’yan ɓaure ku kuma shafa a marurun, zai kuwa warke.”
22 Hizkiya da, “RAB'bin Tapınağı'na çıkacağıma ilişkin belirti nedir?” diye sormuştu.
Hezekiya ya riga ya yi tambaya ya ce, “Me zai zama alama ta cewa zan haura zuwa haikalin Ubangiji?”