< Yeşaya 34 >

1 Ey uluslar, işitmek için yaklaşın! Ey halklar, kulak verin! Dünya ve üzerindeki herkes, Yeryüzü ve ondan türeyenlerin hepsi işitsin!
Ku zo kusa, ku al’ummai, ku kuwa saurara ku kasa kunne, ku mutane! Bari duniya ta ji, da kuma dukan abin da yake cikinta, duniya, da dukan abin da yake fitowa daga gare ta!
2 RAB bütün uluslara öfkelendi, Onların ordularına karşı gazaba geldi. Onları tümüyle mahvolmaya, Boğazlanmaya teslim edecek.
Ubangiji yana fushi da dukan al’ummai; hasalarsa tana a kan mayaƙansu. Zai hallaka su tas, zai ba da su a karkashe.
3 Ölüleri dışarı atılacak, Pis kokacak cesetleri; Dağlar kanlarıyla sulanacak.
Za a jefar da waɗanda aka kashe gawawwakinsu za su yi wari; duwatsu za su jiƙu da jininsu.
4 Bütün gök cisimleri küçülecek, Gökler bir tomar gibi dürülecek; Gök cisimleri, asma yaprağı, İncir yaprağı gibi dökülecek.
Za a tumɓuke dukan taurarin sammai za a kuma nannaɗe sararin sama kamar littafi; dukan rundunar sama za su fāffāɗi kamar ganyayen da suka yanƙwane daga kuringa, kamar’ya’yan ɓauren da suka bushe daga itacen ɓaure.
5 “Kılıcım göklerde kanıncaya kadar içti. Şimdi de Edom'un, Tümüyle yıkmaya karar verdiğim halkın Üzerine inecek” diyor RAB.
Takobina ya sha zararsa a cikin sammai; duba, ya sauko cikin hukunci a kan Edom, mutanen da zan hallaka tas.
6 RAB'bin kılıcı kana, Kuzu ve teke kanına doydu; Yağla, koç böbreklerinin yağıyla kaplandı. Çünkü RAB'bin Bosra'da bir kurbanı, Edom'da büyük bir kıyımı var.
Takobin Ubangiji ya jiƙu da jini, ya rufu da kitse, jinin raguna da na awaki, kitse daga ƙodar raguna. Gama Ubangiji ya yi hadayar Bozra da kuma babban kisa a Edom.
7 Onlarla birlikte yaban öküzleri, Körpe boğalarla güçlü boğalar da yere serilecek. Toprakları kana doyacak, yağla sulanacak.
Babban bijimin jeji zai fāɗi tare da su, maruƙan bijimi da manyan bijimai. Ƙasarsu za tă cika da jini, ƙura kuma zai cika da kitse.
8 Çünkü RAB'bin bir öç günü, Siyon'un davasını güdeceği bir karşılık yılı olacak.
Gama Ubangiji yana da ranar ɗaukar fansa, shekarar ramuwa, don biya wa Sihiyona bukata.
9 Edom dereleri zifte, toprağı kükürde dönecek; ülkenin her yanı yanan zift olacak.
Za a mai da rafuffukan Edom rami, ƙurarta za tă zama kibiritun farar wuta; ƙasarta za tă zama rami mai ƙuna!
10 Zift gece gündüz sönmeyecek, dumanı hep tütecek. Ülke kuşaklar boyu ıssız kalacak, sonsuza dek oradan kimse geçmeyecek.
Ba za a kashe ta ba dare da rana; hayaƙinta za tă yi ta tashi har abada. Daga tsara zuwa tsara za tă zama kango; babu wani da zai ƙara wucewa ta wurin.
11 Baykuşların mülkü olacak orası, büyük baykuşlarla kargalar yaşayacak orada. RAB, Edom'un üzerine kargaşa ipini, boşluk çekülünü gerecek.
Mujiyar hamada da mujiya mai kuka za su mallake ta; babban mujiya da hankaka za su yi sheƙa a can. Allah zai miƙe a kan Edom magwajin bala’i da ma’aunin kango.
12 Kral ilan edebilecekleri soylular kalmayacak, bütün önderlerinin sonu gelecek.
Sarakunanta ba za su kasance da wani abin da ake kira masarauta ba, dukan sarakunanta za su ɓace.
13 Saraylarında dikenler, kalelerinde ısırganlarla böğürtlenler bitecek. Orası çakalların barınağı, baykuşların yurdu olacak.
Ƙayayuwa za su mamaye fadodinta ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya za su cika kagaranta. Za tă zama mazaunin diloli da gida don mujiyoyi.
14 Yabanıl hayvanlarla sırtlanlar orada buluşacak, tekeler karşılıklı böğürecek. Lilit oraya yerleşip rahata kavuşacak.
Halittun hamada za su sadu da kuraye, awakin jeji za su yi ta kiran juna; a can halittun dare su ma za su huta su kuma nemi wurin hutu wa kansu.
15 Baykuşlar orada yuva kurup yumurtlayacak, kuluçkaya yatıp yavrularını kendi gölgelerinde toplayacak. Çaylaklar eşleşip orada toplanacaklar.
Mujiya za tă yi sheƙa a can ta zuba ƙwai; za tă ƙyanƙyashe su, ta kuma kula da’ya’yanta a inuwar fikafikanta; a can kuma shirwa za su taru, kowa da abokinsa.
16 RAB'bin kitabını okuyup araştırın: Bunlardan hiçbiri eksik kalmayacak, eşten yoksun hiçbir hayvan olmayacak. Çünkü bu buyruk RAB'bin ağzından çıktı, Ruhu da onları toplayacak.
Duba a cikin littafin Ubangiji ka kuma karanta. Babu wani a cikin waɗannan da ya ɓace, babu ko ɗaya da ba ta da abokiya. Gama bakinsa ne ya ba da umarni, Ruhunsa kuma zai tara su wuri ɗaya.
17 RAB onlar için kura çekti, ülkeyi ölçüp aralarında pay etti. Orayı sonsuza dek sahiplenip kuşaklar boyu orada yaşayacaklar.
Ya ba su rabonsu; hannunsa ya rarraba musu ta wurin awo. Za su mallake ta har abada su kuma zauna a can daga tsara zuwa tsara.

< Yeşaya 34 >