< Yeşaya 33 >
1 Vay sana, yıkıp yok eden Ama kendisi yıkılmamış olan! Vay sana, ihanete uğramamış hain! Yıkıma son verir vermez sen de yıkılacaksın, İhanetin sona erer ermez sen de ihanete uğrayacaksın.
Kaitonka, ya kai mai hallakarwa, kai da ba a hallakar da kai ba! Kaitonka, ya maciya amana, kai da ba a ci amanarka ba! Sa’ad da ka daina hallakarwa, za a hallaka ka; sa’ad da ka daina cin amana, za a ci amanarka.
2 Ya RAB, lütfet bize, Çünkü sana umut bağladık, Gün be gün gücümüz ol! Sıkıntıya düştüğümüzde bizi kurtar.
Ya Ubangiji, ka yi mana jinƙai; muna marmarinka. Ka zama ƙarfinmu kowace safiya, cetonmu a lokacin damuwa.
3 Kükreyişinden halklar kaçışır, Sen ayağa kalkınca uluslar darmadağın olur.
Da tsawar muryarka, mutane za su gudu; sa’ad da ka tashi, al’ummai za su watse.
4 Çekirgeler tarlayı nasıl yağmalarsa, Ganimetiniz de öyle yağmalanacak, ey uluslar. Malınızın üzerine çekirge sürüsü gibi saldıracaklar.
Ganimarku, ya al’ummai ƙanana fāri sun girbe; kamar tarin fārin da mutane sun fāɗa wa.
5 Yükseklerde oturan RAB yücedir, Siyon'u adalet ve doğrulukla doldurur.
Ubangiji da girma yake, gama yana zaune a bisa; zai cika Sihiyona cikin gaskiya da adalci.
6 Yaşadığınız sürenin güvencesi O'dur. Bol bol kurtuluş, bilgi ve bilgelik sağlayacak. Halkın hazinesi RAB korkusudur.
Zai zama tabbataccen harsashi na koyaushe, ma’ajin ceto da hikima da sani a yalwace; tsoron Ubangiji shi ne mabuɗin wannan dukiya.
7 İşte, en yiğitleri sokaklarda feryat ediyor, Barış elçileri acı acı ağlıyor.
Duba, jarumawansu suna kuka da ƙarfi a tituna; jakadun salama suna kuka mai zafi.
8 Anayollar bomboş, Yolculuk eden kimse kalmadı. Düşman antlaşmayı bozdu, kentleri hor gördü, İnsanları hiçe saydı.
An gudu an bar manyan hanyoyi, babu matafiye a kan hanyoyi. Aka keta yarjejjeniya, an rena shaidunsa ba a kuwa ganin girman kowa.
9 Ülke yas tutuyor, zayıflıyor. Lübnan utancından soldu, Şaron Ovası çöle döndü, Başan ve Karmel'de ağaçlar yaprak döküyor.
Ƙasa tana kuka an kuma gudu an bar ta, Lebanon ta sha kunya ta kuma yanƙwane; Sharon ta zama kamar Araba, Bashan da Karmel sun kakkaɓe ganyayensu.
10 RAB diyor ki, “Şimdi harekete geçeceğim, Ne denli yüce ve üstün olduğumu göstereceğim.
“Yanzu zan tashi,” in ji Ubangiji. “Yanzu ne za a ɗaukaka ni; yanzu za a ɗaga ni sama.
11 Samana gebe kalıp anız doğuracaksınız, Soluğunuz sizi yiyip bitiren bir ateş olacak.
Kun yi cikin yayi, kuka haifi kara; numfashinku wuta ne da zai cinye ku.
12 Halklar yanıp kül olacak, Kesilip yakılan dikenli çalı gibi olacak.
Za a ƙone mutane kamar da ƙuna farar ƙasa; kamar ƙayayyuwan da aka sare aka kuma sa musu wuta.”
13 “Ey uzaktakiler, ne yaptığımı işitin, Ey yakındakiler, gücümü anlayın.”
Ku da kuke da nesa, ku ji abin da na yi; ku da kuke kusa, ku san ikona!
14 Siyon'daki günahkârlar dehşet içinde, Tanrısızları titreme aldı. “Her şeyi yiyip bitiren ateşin yanında Hangimiz oturabilir? Sonsuza dek sönmeyecek alevin yanında Hangimiz yaşayabilir?” diye soruyorlar.
Masu zunubi a Sihiyona sun firgita; rawar jiki ya kama marasa sanin Allah suna cewa, “Wane ne a cikinmu zai iya zama da wuta mai ci? Wane ne a cikinmu zai iya zama da madawwamiyar ƙonewa?”
15 Ama doğru yolda yürüyüp doğru dürüst konuşan, Zorbalıkla edinilen kazancı reddeden, Elini rüşvetten uzak tutan, Kan dökenlerin telkinlerine kulak vermeyen, Kötülük görmeye dayanamayan,
Shi da yake tafiya cikin adalci yana kuma magana abin da yake daidai, wanda yake ƙin riba daga cuta yana kuma kiyaye hannunsa daga karɓan cin hanci, wanda yake hana kunnuwansa daga ƙulla kisa ya kuma rufe idanunsa a kan tunanin aikata mugunta,
16 Yükseklerde oturacak; Uçurumun başındaki kaleler onun korunağı olacak, Ekmeği sağlanacak, hiç susuz kalmayacak.
shi ne mutumin da zai zauna a bisa, wanda mafakarsa za tă zama kagarar dutse. Za a tanada abincinsa, kuma ruwa ba zai kāsa masa ba.
17 Kralı bütün güzelliğiyle görecek, Uçsuz bucaksız ülkeyi seyredeceksin.
Idanunku za su ga sarki a cikin kyansa ku kuma hangi ƙasar da take shimfiɗe can da nisa.
18 “Haracı tartıp kaydeden nerede, Kulelerden sorumlu olan nerede?” diyerek Geçmişteki dehşetli günleri düşüneceksin.
Cikin tunaninku za ku yi tunani firgitar da ta faru tun dā kuna cewa, “Ina hafsan nan? Ina wannan wanda yake karɓar haraji? Ina hafsan da yake lura da hasumiyoyi?”
19 Garip, anlaşılmaz bir yabancı dil konuşan O küstah halkı artık görmeyeceksin.
Ba za ku ƙara ganin waɗannan mutane masu girman kai kuma ba, waɗannan mutane masu magana da harshen da ba ku fahimta ba.
20 Bayramlarımızın kenti olan Siyon'a bak! Yeruşalim'i bir esenlik yurdu, Kazıkları asla yerinden sökülmeyen, Gergi ipleri hiç kopmayan, Sarsılmaz bir çadır olarak görecek gözlerin.
Ku duba Sihiyona, birnin shagulgulanmu; idanunku za su ga Urushalima, mazauni mai lafiya, tentin da ba za a taɓa gusar ba; wanda ba a taɓa tumɓuke turakunsa ba, ko a tsinke igiyoyinta.
21 Heybetli RAB orada bizden yana olacak. Orası geniş ırmakların, çayların yeri olacak. Bunların üzerinden ne kürekli tekneler, Ne de büyük gemiler geçecek.
A can Ubangiji zai zama Mai Iko Duka namu. Zai zama kamar inda manyan koguna da rafuffuka suke. Matuƙan jirgin ruwa ba za su kai wurinsu ba, manyan jiragen ruwa ba za su yi zirga-zirga a kansu ba.
22 Çünkü yargıcımız RAB'dir; Yasamızı koyan RAB'dir, Kralımız RAB'dir, bizi O kurtaracak.
Gama Ubangiji ne alƙalinmu, Ubangiji ne mai ba mu dokoki, Ubangiji ne sarkinmu; shi ne wanda zai cece mu.
23 Senin gemilerinin halatları gevşedi, Direklerinin dibini pekiştirmediler, Yelkenleri açmadılar. O zaman büyük ganimet paylaşılacak, Topallar bile yağmaya katılacak.
Maɗaurinku sun kunce ƙarfafan itacen jirgin ba su da kāriya, fikafikan jirgin ba su buɗu ba. Ta haka za a raba yalwar ganima har ma guragu za su kwashe ganimar.
24 Siyon'da oturan hiç kimse “Hastayım” demeyecek, Orada yaşayan halkın suçu bağışlanacak.
Ba wani mazauna a Sihiyona da zai ce, “Ina ciwo”; za a kuma gafarta zunuban waɗanda suke zama a can.