< Yeşaya 30 >

1 RAB, “Vay haline bu dikbaşlı soyun!” diyor, “Benim değil, kendi tasarılarını yerine getirip Ruhuma aykırı anlaşmalar yaparak Günah üstüne günah işliyorlar.
“Kaiton’ya’ya masu tayarwa,” in ji Ubangiji, “ga waɗanda suke ƙulle-ƙullen da ba nawa ba, suna yin yarjejjeniya, amma ba ta Ruhuna ba, suna jibga zunubi a kan zunubi;
2 Bana danışmadan firavunun koruması altına girmek, Mısır'ın gölgesine sığınmak için oraya gidiyorlar.
waɗanda suka gangara zuwa Masar ba tare da sun nemi shawarata; waɗanda suke neman taimakon kāriyar Fir’auna, don neman inuwar mafakar Masar.
3 Ne var ki, firavunun koruması onlar için utanç, Mısır'ın gölgesine sığınmaları onlar için rezillik olacak.
Amma kāriyar Fir’auna za tă zama muku abin kunya, inuwar Masar za tă jawo muku kunya.
4 Önderleri Soan'da olduğu, Elçileri Hanes'e ulaştığı halde,
Ko da yake suna da shugabanni a Zowan kuma jakadunsu sun iso Hanes,
5 Kendilerine yararı olmayan bir halk yüzünden hepsi utanacak. O halkın onlara ne yardımı ne de yararı olacak, Ancak onları utandırıp rezil edecek.”
kowa zai sha kunya saboda mutanen da ba su da amfani gare su, waɗanda ba sa taimako ko amfani, sai dai jawo kunya da da-na-sani.”
6 Negev'deki hayvanlara ilişkin bildiri: “Elçiler erkek ve dişi aslanların, Engereklerin, uçan yılanların yaşadığı Çetin ve sıkıntılı bir bölgeden geçerler. Servetlerini eşeklerin sırtına, Hazinelerini develerin hörgücüne yükleyip Kendilerine hiç yararı olmayan halka taşırlar.
Allah ya faɗa game da dabbobin Negeb cewa, Ta cikin ƙasa mai wahala da mai hatsari inda zakoki da zakanya, inda macizai masu dafi da macizai masu tashi sama suke, jakadu na ɗaukan arzikinsu a kan jakuna, dukiyarsu a kan raƙuma, zuwa ƙasan nan marar riba,
7 Mısır'ın yardımı boş ve yararsızdır, Bu yüzden Mısır'a ‘Haylaz Rahav’ adını verdim.
zuwa Masar, wadda taimakonta marar amfani ne. Saboda haka na yi mata laƙabi Rahab Marar Yin Kome.
8 “Şimdi git, söylediğimi onların önünde Bir levhaya yazıp kitaba geçir ki, Gelecekte kalıcı bir tanık olsun.
Tafi yanzu, ka rubuta musu a kan allo, ka rubuta shi a kan littafi, cewa kwanaki suna zuwa zai zama madawwamin shaida.
9 Çünkü o asi bir halk, yalancı bir soy, RAB'bin yasasını duymak istemeyen bir soydur.
Waɗannan mutane masu tawaye,’ya’ya masu ruɗu,’ya’yan da ba sa niyya su saurara ga umarnan Ubangiji.
10 Bilicilere, ‘Artık görüm görmeyin’, Görenlere, ‘Bizim için doğru şeyler görmeyin, Bize güzel şeyler söyleyin, asılsız şeyler açıklayın’ diyorlar,
Sukan ce wa masu gani, “Kada ku ƙara ganin wahayi!” Ga annabawa kuwa sukan ce, “Kada ku ƙara ba mu wahayin abin da yake daidai! Faɗa mana abubuwan da muke so mu ji ne kawai, ku yi annabcin abin da zai ruɗe mu.
11 ‘Yoldan çekilin, yolu açın, Bizi İsrail'in Kutsalı'yla yüzleştirmekten vazgeçin.’”
Ku bar wannan hanya, ku tashi daga wannan hanya, ku kuma daina kalubalantarmu da Mai Tsarkin nan na Isra’ila!”
12 Bu nedenle İsrail'in Kutsalı diyor ki, “Madem bu bildiriyi reddettiniz, Baskıya ve hileye güvenip dayandınız;
Saboda haka, ga abin da Mai Tsarkin nan na Isra’ila yake cewa, “Saboda haka kun ƙi wannan saƙo, kuka dogara ga aikin kama-karya kuka kuma dogara ga yin ruɗu,
13 Bu suçunuz yüksek bir surda Sırt veren çatlağa benziyor. Böyle bir sur birdenbire yıkılıverir.
wannan zunubi zai zama muku kamar bango mai tsayi, tsagagge da yake kuma fāɗuwa, da zai rushe nan da nan, ba tsammani.
14 O, toprak çömlek gibi parçalanacak. Parçalanması öyle şiddetli olacak ki, Ocaktan ateş almaya ya da sarnıçtan su çıkarmaya Yetecek büyüklükte bir parça kalmayacak.”
Zai rushe kucu-kucu kamar tukunyar yumɓu, ya ragargaje ƙaf har cikin gutsattsarinsa ba za a sami ko ɗan katanga don ɗiba garwashin wuta ko a ɗiba ruwa daga tanki ba.”
15 Egemen RAB, İsrail'in Kutsalı şöyle diyor: “Bana dönün, huzur bulun, kurtulursunuz. Kaygılanmayın, bana güvenin, güçlü olursunuz. Ama bunu yapmak istemiyorsunuz.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya faɗa, “Cikin tuba da hutu ne kaɗai cetonku yake, cikin shiru da dogara gare ni ne za ku sami ƙarfinku, amma ba za ku sami ko ɗaya a cikinsu ba.
16 ‘Hayır, atlara binip kaçarız’ diyorsunuz, Bu yüzden kaçmak zorunda kalacaksınız. ‘Hızlı atlara bineriz’ diyorsunuz, Bu yüzden sizi kovalayanlar da hızlı olacak.
Kun ce, ‘A’a, za mu gudu a kan dawakai.’ Saboda haka za ku gudu! Kun ce, ‘Za mu hau dawakai masu sauri mu gudu.’ Saboda haka masu fafararku za su fi ku gudu!
17 Bir kişinin tehdidiyle bin kişi kaçacak, Beş kişinin tehdidiyle hepiniz kaçacaksınız; Dağ başında bir gönder, Tepede bir sancak gibi kalana dek kaçacaksınız.
Dubu za su gudu don barazanar mutum guda; da jin barazanar mutane biyar dukanku za ku yi ta gudu sai an bar ku kamar sandar tuta a kan dutse, kamar tuta a kan tudu.”
18 “Yine de RAB size lütfetmeyi özlemle bekliyor, Size merhamet göstermek için harekete geçiyor. Çünkü RAB adil Tanrı'dır. Ne mutlu O'nu özlemle bekleyenlere!”
Duk da haka Ubangiji yana marmari ya yi muku alheri; ya tashi don yă nuna muku jinƙai. Gama Ubangiji Allah ne mai aikata gaskiya. Masu albarka ne dukanku waɗanda suke dogara gare shi!
19 “Ey Yeruşalim'de oturan Siyon halkı, Artık ağlamayacaksın! Feryat ettiğinde Rab sana nasıl da lütfedecek! Feryadını duyar duymaz seni yanıtlayacak.
Ya mutanen Sihiyona, waɗanda suke zama a Urushalima, ba za ku ƙara kuka ba. Zai zama mai alheri sa’ad da kuka yi kukan neman taimako! Da zarar ya ji, zai amsa muku.
20 Rab ekmeği sıkıntıyla, Suyu cefayla verse de, Öğretmeniniz artık gizlenmeyecek, Gözünüzle göreceksiniz onu.
Ko da yake Ubangiji yakan ba da abincin azaba da ruwan wahala, ba za a ƙara ɓoye malamanku ba; da idanunku za ku gan su.
21 Sağa ya da sola sapacağınız zaman, Arkanızdan, ‘Yol budur, bu yoldan gidin’ Diyen sesini duyacaksınız.
Ko kun juye dama ko hagu, kunnuwanku za su ji murya a bayanku tana cewa, “Ga hanya; ku yi tafiya a kai.”
22 Gümüş kaplı oyma putlarınızı, Altın kaplama dökme putlarınızı ‘Kirli’ ilan edecek, Kirli bir âdet bezi gibi atıp ‘Defol’ diyeceksiniz.
Sa’an nan za ku ƙazantar da gumakanku da kuka dalaye da zinariya; za ku zubar da su kamar rigar al’adar mace ku kuma ce musu, “Ku ɓace mana da gani!”
23 Rab toprağa ektiğiniz tohum için yağmur verecek, Toprağın ürünü olan yiyecek bol ve zengin olacak. O gün sığırlarınız geniş otlaklarda otlanacak.
Zai kuma aiko muku da ruwan sama don shuki a ƙasa, kuma abincin da zai fito daga gona zai zama mai albarka da kuma mai yawa. A wannan rana shanu za su yi kiwo a wadatacciyar makiyaya.
24 Toprağı işleyen öküzlerle eşekler Kürekle, yabayla savrulmuş, Tuzlanmış yem yiyecekler.
Shanunku da jakunanku da suke huɗar gonakinku za su ci harawa mafi kyau, wanda an sheƙe shi da babban cokali mai yatsu da kuma babban cokali.
25 Kulelerin yıkıldığı o büyük kıyım günü Her yüksek dağda, her yüce tepede Akarsular olacak.
A ranar babban kisa, sa’ad da hasumiyoyi za su fāɗi, rafuffukan ruwa za su malalo a kan kowane dutse da kowane tudu mai tsawo.
26 RAB halkının kırıklarını sardığı, Vuruşuyla açtığı yaraları iyileştirdiği gün, Ay güneş gibi parlayacak, Güneş yedi kat, yedi günün toplam parlaklığı kadar parlak olacak.”
Wata zai yi haske kamar rana, kuma hasken rana zai ma yi sau bakwai na haskenta, kamar hasken cikakku ranaku bakwai, sa’ad da Ubangiji zai ɗaura raunukan mutanensa ya kuma warkar da raunukan da ya yi musu.
27 Bakın, RAB'bin kendisi uzaktan geliyor, Kızgın öfkeyle kara bulut içinde. Dudakları gazap dolu, Dili her şeyi yiyip bitiren ateş sanki.
Duba, Sunan Ubangiji yana zuwa daga nesa, tare da fushi mai ƙuna da kuma baƙin hayaƙi; leɓunansa sun cika da fushi, harshensa kuma wuta ce mai cinyewa.
28 Soluğu adam boynuna dek yükselmiş taşkın ırmak gibi. Ulusları elekten geçirecek, değersizleri ayıracak, Halkların ağzına yoldan saptıran bir gem takacak.
Numfashinsa kamar raƙuman ruwa masu gudu yana tashi har zuwa wuya. Yakan tankaɗe al’ummai cikin lariyar hallaka; yakan sa a muƙamuƙan mutane linzamin da zai jagorance su su kauce.
29 Ama sizler bayram gecesini kutlar gibi Ezgiler söyleyeceksiniz. RAB'bin dağına, İsrail'in Kayası'na Kaval eşliğinde çıktığınız gibi İçten sevineceksiniz.
Za ku kuma rera kamar a daren da kuke shagalin biki mai tsarki; zukatanku za su yi farin ciki kamar sa’ad da mutane sukan haura da busa zuwa dutsen Ubangiji, zuwa Dutse na Isra’ila.
30 RAB heybetli sesini işittirecek; Kızgın öfkeyle, her şeyi yiyip bitiren ateş aleviyle, Sağanak yağmurla, fırtına ve doluyla Bileğinin gücünü gösterecek.
Ubangiji zai sa mutane su ji muryarsa mai daraja ya kuma sa su ga hannunsa na saukowa tare da fushi mai ƙuna da kuma wuta mai cinyewa, gizagizai za su ɓarke, za a yi hadarin tsawa da ƙanƙara.
31 Asur RAB'bin sesiyle dehşete düşecek, O'nun değneğiyle vurulacak.
Muryar Ubangiji za tă firgita Assuriya da sandar mulkinsa zai kashe su.
32 RAB'bin terbiye değneğiyle onlara indirdiği her darbeye Tef ve lir eşlik edecek. RAB silahlarını savura savura onlarla savaşacak.
Kowane bugun da Ubangiji zai yi musu da bulalarsa na hukunci zai zama kiɗi ga ganguna da garaya, yayinda yake yaƙi da su da naushin hannunsa.
33 Tofet çoktan hazırlandı, Evet, kral için hazırlandı. Geniş ve yüksektir odun yığını, Ateşi, odunu boldur. RAB kızgın kükürt selini andıran Soluğuyla tutuşturacak onu.
An riga an shirya wurin ƙonawa; an shirya shi saboda sarki. An haƙa ramin wutarsa da zurfi da kuma fāɗi, da isashen wuta da itacen wuta; numfashin Ubangiji, yana kamar kibiritu mai ƙuna, da aka sa masa wuta.

< Yeşaya 30 >