< Yeşaya 2 >
1 Amots oğlu Yeşaya'nın Yahuda ve Yeruşalim'le ilgili görümü:
Ga abin da Ishaya ɗan Amoz ya gani game da Yahuda da Urushalima.
2 RAB'bin Tapınağı'nın kurulduğu dağ, Son günlerde dağların en yücesi, Tepelerin en yükseği olacak. Oraya akın edecek ulusların hepsi.
A kwanaki masu zuwa za a kafa dutsen haikalin Ubangiji a matsayin babba cikin duwatsu; za a daga shi bisa tuddai, kuma dukan al’ummai za su bumbunto zuwa gare shi.
3 Birçok halk gelecek, “Haydi, RAB'bin Dağı'na, Yakup'un Tanrısı'nın Tapınağı'na çıkalım” diyecekler, “O bize kendi yolunu öğretsin, Biz de O'nun yolundan gidelim.” Çünkü yasa Siyon'dan, RAB'bin sözü Yeruşalim'den çıkacak.
Mutane da yawa za su zo su ce, “Ku zo, bari mu haura zuwa dutsen Ubangiji, zuwa gidan Allah na Yaƙub. Zai koya mana hanyoyinsa, domin mu yi tafiya cikin hanyoyinsa.” Dokar za tă fito daga Sihiyona, maganar Ubangiji daga Urushalima.
4 RAB uluslar arasında yargıçlık edecek, Birçok halkın arasındaki anlaşmazlıkları çözecek. İnsanlar kılıçlarını çekiçle dövüp saban demiri, Mızraklarını bağcı bıçağı yapacaklar. Ulus ulusa kılıç kaldırmayacak, Savaş eğitimi yapmayacaklar artık.
Zai shari’anta tsakanin al’ummai zai kuma sulhunta faɗar mutane masu yawa. Za su mai da takubansu su zama garemani māsunsu su zama wuƙaƙen askin itatuwa. Al’umma ba za tă ƙara ɗauki takobi a kan al’umma ba, ba kuwa za su ƙara yin horarwar yaƙi.
5 Ey Yakup soyu, gelin RAB'bin ışığında yürüyelim.
Ki zo, ya gidan Yaƙub, bari mu yi tafiya a hasken Ubangiji.
6 Ya RAB, halkını, Yakup soyunu terk ettin, Çünkü yürekleri doğu kökenli inançlarla dolu. Filistliler gibi falcılıkla uğraşıyor, Yabancılarla el sıkışıyorlar.
Ka rabu da mutanenka, gidan Yaƙub. Sun cika da ayyukan sihiri da aka kawo daga Gabas; suna yin duba kamar Filistiyawa suna tafa hannuwa tare da marasa sanin Allah.
7 Ülkeleri altınla, gümüşle dolu, Hazinelerinin sonu yok, Sayısız atları, savaş arabaları var.
Ƙasarsu ta cika da azurfa da zinariya; dukiyarsu kuma ba iyaka. Ƙasarsu ta cika da dawakai; kekunan yaƙinsu kuma ba iyaka.
8 Ülkeleri putlarla dolu; Elleriyle yaptıkları, Parmaklarıyla biçim verdikleri Putların önünde eğiliyorlar.
Ƙasarsu ta cika da gumaka; sukan rusuna ga aikin hannuwansu, ga abin da yatsotsinsu suka yi.
9 Bu yüzden herkes alçaltılıp dize getirilecek. Onları bağışlama, ya RAB!
Saboda an jawo mutum ƙasa aka kuma ƙasƙantar da ɗan adam, kada ku gafarta musu.
10 RAB'bin dehşetinden, Yüce görkeminden kaçmak için kayalıklara gidin, Yerin altına saklanın.
Ku tafi cikin duwatsu, ku ɓuya cikin ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa!
11 İnsanın küstah bakışları alçaltılacak, Gururu kırılacak. O gün yalnız RAB yüceltilecek.
Za a ƙasƙantar da mai girman kai za a kuma lalatar da fariyar masu ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana.
12 Çünkü Her Şeye Egemen RAB o gün Kibirlileri, gururluları, kendini beğenmişleri alçaltacak;
Ubangiji Maɗaukaki yana da rana ajiye domin dukan masu girman kai da masu fariya domin dukan waɗanda aka ɗaukaka (zai kuwa ƙasƙantar da su),
13 Lübnan'ın bütün ulu, yüksek sedir ağaçlarını, Başan'ın bütün meşelerini yok edecek;
domin dukan al’ul na Lebanon, masu tsayi da masu fariya, da kuma dukan itatuwan oak na Bashan,
14 Bütün ulu dağları, yüksek tepeleri,
domin dukan dogayen duwatsu da kuma tuddai masu tsayi,
15 Bütün yüksek kuleleri, güçlü surları Yerle bir edecek;
domin kowace doguwar hasumiya da kowace katanga mai ƙarfi,
16 Ticaret gemilerinin, güzel teknelerinin hepsini yok edecek.
domin kowane jirgin ruwan kasuwanci da kuma jirgi mafi girma mafi kyau.
17 İnsanların gururu, kibiri kırılacak, O gün yalnız RAB yüceltilecek,
Za a jawo mai girman kai ƙasa a kuma ƙasƙantar da mai ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana,
18 Putlar tümüyle ortadan kalkacak.
za a kuma kawar da gumaka ƙaƙaf.
19 RAB kalkıp yeryüzünü sarsmaya başlayınca, İnsanlar O'nun dehşetinden Ve yüce görkeminden kaçmak için Kayalık mağaralara, yeraltı kovuklarına saklanacaklar.
Mutane za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma ramummuka a ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
20 O gün insanlar Yeryüzünü sarsmak üzere harekete geçen RAB'bin dehşetinden Ve yüce görkeminden kaçmak için Tapmak amacıyla yaptıkları altın, gümüş putları Köstebeklere, yarasalara atıp Kaya kovuklarına, uçurumlardaki yarıklara saklanacaklar.
A wannan rana mutane za su zubar wa jaba da jamage gumakansu na azurfa da gumakansu na zinariya da suka yi don su bauta musu.
Za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma zuwa tsagaggun duwatsu daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
22 Ölümlü insana güvenmekten vazgeçin. Onun ne değeri var ki?
Ku daina dogara ga mutum, wanda numfashi ne kawai yake da shi a hancinsa. Wace daraja gare shi?