< Yeşaya 1 >
1 Yahuda kralları Uzziya, Yotam, Ahaz ve Hizkiya zamanında Amots oğlu Yeşaya'nın Yahuda ve Yeruşalim'le ilgili görümü:
Wahayi game da Yahuda da Urushalima wanda Ishaya ɗan Amoz ya gani a zamanin da Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, suka yi mulkin Yahuda.
2 Ey gökler dinleyin, ey yeryüzü kulak ver! Çünkü RAB konuşuyor: “Çocuklar yetiştirip büyüttüm, Ama bana başkaldırdılar.
Ku kasa kunne, ya sammai! Ki saurara, ya duniya! Gama Ubangiji ya yi magana, “Na yi renon’ya’ya, na kuma raya su, amma sun tayar mini.
3 Öküz sahibini, eşek efendisinin yemliğini bilir, Ama İsrail halkı bu kadarını bile bilmiyor, Halkım anlamıyor.”
Saniya ta san maigidanta, jaki ya san wurin sa wa dabbobi abinci maigidansa, amma Isra’ila ba su sani, mutanena ba su gane ba.”
4 Günahlı ulusun, suç yüklü halkın, Kötülük yapan soyun, Baştan çıkmış çocukların vay haline! RAB'bi terk ettiler, İsrail'in Kutsalı'nı hor gördüler, O'na sırt çevirdiler.
Kash, ya ke al’umma mai zunubi, mutane cike da laifi, tarin masu aikata mugunta,’ya’yan da aka miƙa wa lalaci! Sun yashe Ubangiji; sun rena Mai Tsarkin nan na Isra’ila suka juya masa baya.
5 Neden bir daha dövülesiniz? Neden vefasızlığı sürdürüyorsunuz? Baş büsbütün hasta, yürek büsbütün yaralı.
Me ya sa za a ƙara yin muku dūka? Me ya sa kuka nace ga yin tayarwa? An yi wa dukan kanku rauni, zuciyarku duk tana ciwo.
6 Bedeniniz tepeden tırnağa sağlıksız, Taze darbe izleriyle, yara bereyle dolu, Temizlenmemiş, yağla yumuşatılmamış, sarılmamış.
Daga tafin ƙafarku zuwa saman kanku ba lafiya, sai miyaku da ƙujewa da manyan gyambuna, ba a tsabtacce su ba ko a daure ko shafa musu magani.
7 Ülkeniz ıssız, kentleriniz ateşe verilmiş. Yabancılar topraklarınızı Gözünüzün önünde yiyip bitiriyor! Sanki ülkenin kökünü kazımışlar.
Ƙasarku ta zama kufai, an ƙone biranenku da wuta; baƙi suna ƙwace gonakinku a idanunku, ta zama kango kamar sa’ad da baƙi suka rushe ta.
8 Siyon kızı bağdaki çardak, Salatalık bostanındaki kulübe gibi, Kuşatılmış bir kent gibi kalakalmış.
An bar diyar Sihiyona kamar rumfar mai ƙumu a gonar inabi, kamar bukka a gonar kabewa, kamar birnin da aka kewaye da yaƙi.
9 Her Şeye Egemen RAB bazılarımızı Sağ bırakmamış olsaydı, Sodom gibi olur, Gomora'ya benzerdik.
Da ba a ce Ubangiji Maɗaukaki ya bar mana raguwar masu rai ba, da mun zama kamar Sodom, da mun zama kamar Gomorra.
10 Ey Sodom yöneticileri, RAB'bin söylediklerini dinleyin; Ey Gomora halkı, Tanrımız'ın yasasına kulak verin.
Ku saurari maganar Ubangiji, ku masu mulkin Sodom; ku kasa kunne ga dokar Allahnmu, ku mutanen Gomorra!
11 “Kurbanlarınızın sayısı çokmuş, Bana ne?” diyor RAB, “Yakmalık koç sunularına, Besili hayvanların yağına doydum. Boğa, kuzu, teke kanı değil istediğim.
Ubangiji ya ce, “Yawan hadayunku, mene ne suke a gare ni?” Ina da isashen hadayun ƙonawa, na raguna da na kitsen dabbobi masu ƙiba; ba na jin daɗin jinin bijimai da na tumaki da kuma na awaki.
12 Huzuruma geldiğinizde Avlularımı çiğnemenizi mi istedim sizden?
Sa’ad da kuka zo don ku bayyana a gabana, wa ya nemi wannan daga gare ku, da kuke kai da kawowa a filayen gidana?
13 Anlamsız sunular getirmeyin artık. Buhurdan iğreniyorum. Kötülük dolu törenlere, Yeni Ay, Şabat Günü kutlamalarına Ve düzenlediğiniz toplantılara dayanamıyorum.
Ku daina kawo hadayu marasa amfani! Turarenku abin ƙyama ne gare ni. Ina ƙin bukukkuwanku na Sabon Wata, da na ranakun Asabbaci, da taronku na addini, ba zan iya jure wa mugun taronku ba.
14 Yeni Ay törenlerinizden, bayramlarınızdan nefret ediyorum. Bunlar bana yük oldu, Onları taşımaktan yoruldum.
Bukukkuwanku na Sabon Wata da na tsarkakan ranaku na ƙi su. Sun zama mini kaya; na gaji da ɗaukansu.
15 “Ellerinizi açıp bana yakardığınızda Gözlerimi sizden kaçıracağım. Ne kadar çok dua ederseniz edin dinlemeyeceğim. Elleriniz kan dolu.
Sa’ad da kuka ɗaga hannuwanku wajen yin addu’a, zan ɓoye fuskata daga gare ku; ko da kun miƙa addu’o’i masu yawa, ba zan kasa kunne ba. Hannuwanku sun cika da jini!
16 Yıkanıp temizlenin, Kötülük yaptığınızı gözüm görmesin, Kötülük etmekten vazgeçin.
Ku yi wanka ku kuma tsabtacce kanku. Ku kawar da mugayen ayyukanku daga gabana; Ku daina aikata mugunta.
17 İyilik etmeyi öğrenin, Adaleti gözetin, zorbayı yola getirin, Öksüzün hakkını verin, Dul kadını savunun.”
Ku koyi yin nagarta; ku nemi adalci. Ku ƙarfafa waɗanda aka zalunta. Ku ba wa marayu hakkinsu, ku taimaki gwauruwa.
18 RAB diyor ki, “Gelin, şimdi davamızı görelim. Günahlarınız sizi kana boyamış bile olsa Kar gibi ak pak olacaksınız. Elleriniz kırmız böceği gibi kızıl olsa da Yapağı gibi bembeyaz olacak.
Ubangiji ya ce, “Yanzu fa ku zo, bari mu dubi batun nan tare, Ko da zunubanku sun yi ja kamar garura, za su zama fari kamar ƙanƙara; ko da sun yi ja kamar mulufi, za su zama kamar ulu.
19 İstekli olur, söz dinlerseniz, Ülkenin en iyi ürünlerini yiyeceksiniz.
In kuna da niyya kuna kuma yi mini biyayya, za ku ci abubuwa masu kyau daga ƙasar;
20 Ama direnip başkaldırırsanız, Kılıç sizi yiyip bitirecek.” Bunu söyleyen RAB'dir.
amma in kuka yi tsayayya kuka kuma yi tayarwa, za a kashe ku da takobi.” Ni Ubangiji na faɗa.
21 Sadık kent nasıl da fahişe oldu! Adaletle doluydu, doğruluğun barınağıydı, Şimdiyse katillerle doldu.
Dubi yadda amintacciyar birni ta zama karuwa! Dā ta cika da yin gaskiya; dā masu adalci a can suke zama, amma yanzu sai masu kisankai kaɗai!
22 Gümüşü cüruf oldu, Şarabına su katıldı.
Azurfarki ta zama jebu, an gauraye ruwan inabinki mafi kyau da ruwa.
23 Yöneticileri asilerle hırsızların işbirlikçisi; Hepsi rüşveti seviyor, Armağan peşine düşmüş. Öksüzün hakkını vermiyor, Dul kadının davasını görmüyorlar.
Masu mulkinki’yan tawaye ne, abokan ɓarayi; dukansu suna ƙaunar cin hanci suna bin kyautai. Ba sa taɓa tsare marayu a ɗakin shari’a; ba sa taimakon gwauruwa.
24 Bu yüzden Rab, Her Şeye Egemen RAB, İsrail'in Güçlüsü şöyle diyor: “Hasımlarımı cezalandırıp rahata kavuşacağım, Düşmanlarımdan öç alacağım.
Saboda haka Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, Mai Iko nan na Isra’ila, ya furta, “Kai, zan sami hutu daga maƙiyana in kuma yi ramuwa a kan abokan gābana.
25 Sana karşı duracak, Kül suyuyla arıtır gibi seni cüruftan arıtıp temizleyeceğim.
Zan juye hannuna a kanki; zan wanke ke sarai in fitar da dukan ƙazantarki.
26 Eskiden, başlangıçta olduğu gibi, Sana yöneticiler, danışmanlar yetiştireceğim. Ondan sonra ‘Doğruluk Kenti’, ‘Sadık Kent’ diye adlandırılacaksın.”
Zan maido da alƙalanki kamar yadda suke a dā can, mashawartanki kamar yadda suke da fari. Bayan haka za a ce da ke Birnin Masu Adalci, Amintacciyar Birni.”
27 Siyon adalet sayesinde, Tövbe edenleri de doğruluk sayesinde kurtulacak.
Za a fanshi Sihiyona da adalci, masu tubanta kuma da aikin gaskiya.
28 Ama başkaldıranlarla günahlılar Birlikte yıkıma uğrayacaklar. RAB'bi terk edenler yok olacak.
Amma za a karye’yan tawaye da masu zunubi, waɗanda suka rabu da Ubangiji kuma za su hallaka.
29 “Sevip altında tapındığınız yabanıl fıstık ağaçlarından utanacaksınız, Putperest törenleriniz için seçtiğiniz bahçelerden ötürü yüzünüz kızaracak.
“Za ku ji kunya saboda masujadan ƙarƙashin itatuwan oak da kuka yi farin ciki; za a kunyata ku saboda lambun da kuka zaɓa.
30 Yaprakları solmuş yabanıl fıstık ağacına, Susuz bahçeye döneceksiniz.
Za ku zama kamar itacen oak mai busasshen ganyaye, kamar lambu marar ruwa.
31 Güçlü adamlarınız kıtık gibi, Yaptıkları işler kıvılcım gibi olacak; İkisi birlikte yanacak ve söndüren olmayacak.”
Mutum mai ƙarfi zai zama kamar rama, aikinsa kuma kamar tartsatsin wuta; duka za su ƙone tare, ba kuwa wanda zai kashe wutar.”