< Hagay 1 >

1 Kral Darius'un krallığının ikinci yılında, altıncı ayın birinci günü RAB Peygamber Hagay aracılığıyla Şealtiel'in torunu Yahuda Valisi Zerubbabil ve Yehosadak oğlu Başkâhin Yeşu'ya seslendi:
A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus, a rana ta fari ga watan shida, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai zuwa ga Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, gwamnan Yahuda, da kuma Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist.
2 “Her Şeye Egemen RAB diyor ki, ‘Bu halk, RAB'bin Tapınağı'nı yeniden kurmak için vakit daha gelmedi diyor.’”
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Waɗannan mutane sun ce, ‘Lokaci bai yi ba tukuna da za a gina gidan Ubangiji.’”
3 Sonra RAB, Peygamber Hagay aracılığıyla şöyle seslendi:
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
4 “Bu tapınak yıkık durumdayken, sizin ağaç kaplamalı evlerinizde oturmanızın sırası mı?”
“Ashe, lokaci ya yi da za ku zauna a ɗakunan da kuka yi da rufin katako, amma haikalin nan yana zaman kufai?”
5 Her Şeye Egemen RAB diyor ki, “Şimdi tuttuğunuz yolları iyi düşünün!
To, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
6 Çok ektiniz ama az biçtiniz; yiyorsunuz ama doyamıyorsunuz, içiyorsunuz ama neşelenemiyorsunuz; giyiniyorsunuz ama ısınamıyorsunuz; ücretinizi alıyorsunuz ama paranızı sanki delik keseye koyuyorsunuz.”
Kun shuka da yawa, amma kun girbe kaɗan. Kun ci, amma ba ku ƙoshi ba. Kun sha, amma ba ku kashe ƙishirwa ba. Kun sa tufafi, amma ba ku ji ɗumi ba. Kuna karɓar albashi, ya zama sai ka ce kuna zuba a hudajjen aljihu.”
7 Her Şeye Egemen RAB, “Tuttuğunuz yolları iyi düşünün!” diyor, “Dağlara çıkıp kütük getirin, tapınağı yeniden kurun. Öyle ki, ondan hoşnut olayım, yüceltileyim.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
8
Ku haura zuwa kan duwatsu ku sauko da katakai don ku gina gidan, don ni ma in ji daɗinsa, in kuma sami ɗaukaka,” in ji Ubangiji.
9 Bol ürün umdunuz ama az topladınız. Eve ne getirdiyseniz üfleyip dağıttım. Acaba neden?” Böyle soruyor Her Şeye Egemen RAB. “Yıkık duran tapınağımdan ötürü! Oysa hepiniz kendi evinizle uğraşıyorsunuz.
“Ga shi, kukan sa rai za ku sami da yawa, amma sai ku ga kun sami kaɗan. Ɗan kaɗan ɗin ma da kukan kawo gida, nakan hura shi yă tafi. Me ya sa yake faruwa haka?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Saboda gidana da yake zaman kango, yayinda kowannenku yana faman gina gidansa.
10 İşte bunun içindir ki, gök çiyini, toprak ürününü sizden esirgiyor.
Shi ya sa, saboda ku sammai sun ƙi saukar da raɓa, ƙasa kuma ta ƙi ba da amfani.
11 Ülkeyi –dağlarını, tahılını, yeni şarabını, zeytinyağını, toprağın verdiği ürünleri, insanlarını, hayvanlarını, ellerinizin bütün emeğini– kuraklıkla cezalandırdım.”
Na kawo fări a ƙasar, da a kan duwatsu, da a kan hatsi, da a kan dukan abin da yake tsirowa daga ƙasa, da a kan mutane, da a kan dabbobi da kuma a kan wahalar hannuwanku.”
12 Şealtiel'in torunu Zerubbabil, Yehosadak oğlu Başkâhin Yeşu ve sürgünden dönen halkın tümü Tanrıları RAB'bin sözüne, O'nun tarafından gönderilen Peygamber Hagay'ın sözlerine kulak verdiler. Halk RAB'den korktu.
Sa’an nan sai Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, wanda yake babban firist, da kuma dukan raguwar jama’ar suka yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnsu da kuma saƙon annabi Haggai, domin Ubangiji Allahnsu ne ya aiko shi. Mutane kuwa suka ji tsoron Ubangiji.
13 Sonra RAB'bin ulağı Hagay, RAB'bin şu sözlerini halka bildirdi: “RAB, ‘Ben sizinle birlikteyim’ diyor.”
Sai Haggai, ɗan saƙon Ubangiji, ya ba da wannan saƙo na Ubangiji ga mutane cewa, “Ina tare da ku” in ji Ubangiji.
14 Böylece RAB Şealtiel'in torunu Yahuda Valisi Zerubbabil'i, Yehosadak oğlu Başkâhin Yeşu'yu ve sürgünden dönen halkın tümünü bu konuda harekete geçirdi. Darius'un krallığının ikinci yılında, altıncı ayın yirmi dördüncü günü gelip Tanrıları Her Şeye Egemen RAB'bin Tapınağı'nda işe başladılar.
Saboda haka Ubangiji ya motsa zuciyar Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, wanda yake gwamna a Yahuda, da kuma zuciyar Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma zukatan dukan raguwar jama’ar. Suka zo suka fara aiki a gidan Ubangiji Maɗaukaki, Allahnsu,
a ranar ashirin da huɗu ga watan shida. A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus,

< Hagay 1 >