< Yaratiliş 45 >

1 Yusuf adamlarının önünde kendini tutamayıp, “Herkesi çıkarın buradan!” diye bağırdı. Kendini kardeşlerine tanıttığında yanında kimse olmasın istiyordu.
Yusuf bai ƙara iya daurewa a gaban dukan masu yi masa hidima ba, sai ya yi kuka da ƙarfi ya ce, “Kowa yă tashi daga gabana!” Saboda haka ba kowa a wurin sa’ad da Yusuf ya sanar da kansa ga’yan’uwansa.
2 O kadar yüksek sesle ağladı ki, Mısırlılar ağlayışını işitti. Bu haber firavunun ev halkına da ulaştı.
Sai ya yi kuka da ƙarfi har Masarawa suka ji, har labarin ya kai gidan Fir’auna.
3 Yusuf kardeşlerine, “Ben Yusuf'um!” dedi, “Babam yaşıyor mu?” Kardeşleri donup kaldı, yanıt veremediler.
Yusuf kuwa ya ce wa’yan’uwansa, “Ni ne Yusuf! Mahaifina yana nan da rai har yanzu?” Amma’yan’uwansa ba su iya amsa masa ba, gama sun firgita ƙwarai a gabansa.
4 Yusuf, “Lütfen bana yaklaşın” dedi. Onlar yaklaşınca Yusuf şöyle devam etti: “Mısır'a sattığınız kardeşiniz Yusuf benim.
Sa’an nan Yusuf ya ce wa’yan’uwansa, “Ku zo kusa da ni.” Da suka yi haka, sai ya ce, “Ni ne ɗan’uwanku Yusuf, wannan da kuka sayar zuwa Masar!
5 Beni buraya sattığınız için üzülmeyin. Kendinizi suçlamayın. Tanrı insanlığı korumak için beni önden gönderdi.
Yanzu dai, kada ku damu, kada kuma ku yi fushi da kanku saboda kun sayar da ni a nan, gama Allah ya aiko ni gabanku ne don in ceci rayuka.
6 Çünkü iki yıldır ülkede kıtlık var, beş yıl daha sürecek. Kimse çift süremeyecek, ekin biçemeyecek.
Ga shi shekaru biyu ke nan ake yunwa a ƙasar, kuma da sauran shekara biyar masu zuwa da ba za a yi noma ko girbi ba.
7 Tanrı yeryüzünde soyunuzu korumak ve harika biçimde canınızı kurtarmak için beni önünüzden gönderdi.
Amma Allah ya aiko ni gabanku ne don in adana muku raguwa a duniya, in kuma ceci rayukanku ta wurin ceto mai girma.
8 Beni buraya gönderen siz değilsiniz, Tanrı'dır. Beni firavunun başdanışmanı, sarayının efendisi, bütün Mısır ülkesinin yöneticisi yaptı.
“Saboda haka fa, ba ku ba ne kuka aiko ni nan, Allah ne. Ya mai da ni mahaifi ga Fir’auna, shugaban dukan gidansa da kuma mai mulkin dukan Masar.
9 Hemen babamın yanına gidin, ona oğlun Yusuf şöyle diyor deyin: ‘Tanrı beni Mısır ülkesine yönetici yaptı. Durma, yanıma gel.
Yanzu sai ku gaggauta zuwa wurin mahaifina ku faɗa masa, ‘Abin da ɗanka Yusuf ya ce; Allah ya mai da ni shugaban dukan Masar. Gangaro wurina; kada ka jinkirta.
10 Goşen bölgesine yerleşirsin; çocukların, torunların, davarların, sığırların ve sahip olduğun her şeyle birlikte yakınımda olursun.
Za ka yi zama a yankin Goshen, ka kasance kusa da ni. Kai,’ya’yanka da kuma jikokinka, garkunanka da shanunka, da kuma dukan abin da kake da shi.
11 Orada sana bakarım, çünkü kıtlık beş yıl daha sürecek. Yoksa sen de ailen ve sana bağlı olan herkes de perişan olursunuz.’
Zan tanada maka a nan, domin akwai saura shekaru biyar na yunwa masu zuwa. In ba haka ba, kai da gidanka da dukan mallakarka za ku zama gajiyayyu.’
12 “Hepiniz gözlerinizle görüyorsunuz, kardeşim Benyamin, sen de görüyorsun konuşanın gerçekten ben olduğumu.
“Ku kanku kun gani, haka ma ɗan’uwana Benyamin, cewa tabbatacce ni ne nake magana da ku.
13 Mısır'da ne denli güçlü olduğumu ve bütün gördüklerinizi babama anlatın. Babamı hemen buraya getirin.”
Faɗa wa mahaifina game da dukan girman da aka ba ni a Masar, da kuma game da kome da kuka gani. Ku kuma kawo mahaifina a nan da sauri.”
14 Sonra kardeşi Benyamin'in boynuna sarılıp ağladı. Benyamin de ağlayarak ona sarıldı.
Sa’an nan ya rungume ɗan’uwansa Benyamin ya yi kuka, sai Benyamin ya rungume shi yana kuka.
15 Yusuf ağlayarak bütün kardeşlerini öptü. Sonra kardeşleri onunla konuşmaya başladı.
Ya sumbaci dukan’yan’uwansa, ya kuma yi kuka a kansu. Bayan haka sai’yan’uwansa suka yi masa magana.
16 Yusuf'un kardeşlerinin geldiği haberi firavunun sarayına ulaşınca, firavunla görevlileri hoşnut oldu.
Sa’ad da labarin ya kai fadan Fir’auna cewa’yan’uwan Yusuf sun zo, sai Fir’auna da dukan hafsoshin suka ji daɗi.
17 Firavun Yusuf'a şöyle dedi: “Kardeşlerine de ki, ‘Hayvanlarınızı yükleyip Kenan ülkesine gidin.
Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Faɗa wa’yan’uwanka, ‘Yi wannan; ku jibge dabbobinku ku koma zuwa ƙasar Kan’ana,
18 Babanızı ve ailelerinizi buraya getirin. Size Mısır'ın en iyi topraklarını vereceğim. Ülkenin kaymağını yiyeceksiniz.’
Ku kawo mahaifinku da iyalanku zuwa wurina. Zan ba ku mafi kyau na ƙasar Masar, za ku kuwa ci moriyar ƙasar.’
19 Onlara ayrıca şöyle demeni de buyuruyorum: ‘Çocuklarınızla karılarınız için Mısır'dan arabalar alın, babanızla birlikte buraya gelin.
“An kuma umarce ka, ka faɗa musu, ‘Ku yi wannan, ku ɗauki wagonu daga Masar domin’ya’yanku da matanku, ku ɗauki mahaifinku ku zo.
20 Gözünüz arkada kalmasın, çünkü Mısır'da en iyi ne varsa sizin olacak.’”
Kada ku damu da mallakarku, gama mafi kyau na Masar za su zama naku.’”
21 İsrail'in oğulları söyleneni yaptı. Firavunun buyruğu üzerine Yusuf onlara araba ve yol için azık verdi.
Sai’ya’yan Isra’ila maza suka yi haka. Yusuf ya ba su wagonu kamar yadda Fir’auna ya umarta, ya kuma ba su guzuri don tafiyarsu.
22 Hepsine birer kat yedek giysi, Benyamin'e ise üç yüz parça gümüşle beş kat yedek giysi verdi.
Ya ba da sababbin riguna ga kowannensu amma ga Benyamin ya ba shi shekel ɗari uku na azurfa da riguna kashi biyar.
23 Böylece babasına Mısır'da en iyi ne varsa hepsiyle yüklü on eşek, yolculuk için buğday, ekmek ve azık yüklü on dişi eşek gönderdi.
Ga kuma abin da ya aika wa mahaifinsa, jakuna goma da aka jibge da abubuwa mafi kyau na Masar, da jakuna mata guda goma ɗauke da hatsi da burodi da waɗansu tanade-tanade don tafiyarsa.
24 Kardeşlerini yolcu ederken onlara, “Yolda kavga etmeyin” dedi.
Sa’an nan ya sallami’yan’uwansa, yayinda suke barin wurin ya ce musu, “Kada ku yi faɗa a hanya!”
25 Yusuf'un kardeşleri Mısır'dan ayrılıp Kenan ülkesine, babaları Yakup'un yanına döndüler.
Saboda haka suka haura, suka fita daga Masar, suka zo wurin maihaifinsu Yaƙub a ƙasar Kan’ana.
26 Ona, “Yusuf yaşıyor!” dediler, “Üstelik Mısır'ın yöneticisi olmuş.” Babaları donup kaldı, onlara inanmadı.
Suka faɗa masa, “Yusuf yana da rai! Gaskiya, shi ne mai mulkin dukan Masar.” Gaban Yaƙub ya fāɗi, domin bai gaskata su ba.
27 Yusuf'un kendilerine bütün söylediklerini anlattılar. Kendisini Mısır'a götürmek için Yusuf'un gönderdiği arabaları görünce, Yakup'un keyfi yerine geldi.
Amma sa’ad da suka faɗa masa kome da Yusuf ya faɗa musu, da kuma sa’ad da ya ga wagonun da Yusuf ya aika don a ɗauke shi a kai da shi can, sai ya farfaɗo, ya dawo cikin hankalinsa.
28 “Tamam!” dedi, “Oğlum Yusuf yaşıyor. Ölmeden önce gidip onu göreceğim.”
Sai Yaƙub ya ce, “Na yarda! Ɗana Yusuf yana da rai har yanzu. Zan tafi in gan shi kafin in mutu.”

< Yaratiliş 45 >