< Yaratiliş 40 >
1 Bir süre sonra Mısır Kralı'nın sakisiyle fırıncısı efendilerini gücendirdiler.
Bayan ɗan lokaci, sai mai riƙon kwaf da mai tuyan sarkin Masar suka yi wa maigidansu, sarkin Masar laifi.
2 Firavun bu iki görevlisine, baş sakiyle fırıncıbaşına öfkelendi.
Fir’auna ya yi fushi da hafsoshin nan nasa guda biyu, shugaban masu shayarwa da shugaban masu tuya,
3 Onları muhafız birliği komutanının evinde, Yusuf'un tutsak olduğu zindanda göz altına aldı.
ya kuma sa su a kurkuku a cikin gidan shugaban masu tsaro, a wannan kurkukun da aka sa Yusuf.
4 Muhafız birliği komutanı Yusuf'u onların hizmetine atadı. Bir süre zindanda kaldılar.
Sai shugaban masu tsaro ya danƙa su a hannun Yusuf, ya kuwa yi musu hidima. Bayan sun jima cikin kurkuku,
5 Firavunun sakisiyle fırıncısı tutsak oldukları zindanda aynı gece birer düş gördüler. Düşleri farklı anlamlar taşıyordu.
sai kowanne a cikin mutum biyun nan, mai riƙon kwaf da mai tuya na sarkin Masar, waɗanda aka sa a kurkuku, suka yi mafarki a dare ɗaya, kuma kowane mafarki ya kasance da fassara irin tasa.
6 Sabah Yusuf yanlarına gittiğinde, onları tedirgin gördü.
Sa’ad da Yusuf ya zo wurinsu kashegari, sai ya ga duk sun damu.
7 Efendisinin evinde, kendisiyle birlikte zindanda kalan firavunun görevlilerine, “Niçin suratınız asık bugün?” diye sordu.
Saboda haka ya tambayi hafsoshin Fir’auna, waɗanda suke a kurkuku tare da shi, a gidan maigidansa ya ce, “Me ya sa fuskokinku suke a ɓace haka?”
8 “Düş gördük ama yorumlayacak kimse yok” dediler. Yusuf, “Yorum Tanrı'ya özgü değil mi?” dedi, “Lütfen düşünüzü bana anlatın.”
Sai suka amsa, “Mu biyu, mun yi mafarki, amma babu wani da zai fassara mana su.” Sa’an nan Yusuf ya ce musu, “Fassara ba daga Allah take zuwa ba? Ku faɗa mini mafarkanku.”
9 Baş saki düşünü Yusuf'a anlattı: “Düşümde önümde bir asma gördüm.
Sai shugaban masu shayarwa ya faɗa wa Yusuf mafarkinsa. Ya ce masa, “A cikin mafarkina, na ga kuringa a gabana,
10 Üç çubuğu vardı. Tomurcuklar açar açmaz çiçeklendi, salkım salkım üzüm verdi.
kuma a kuringar, akwai rassa uku. Nan da nan kuringar ta yi toho, ta huda, ta kuma yi nonna har suka nuna, suka zama inabi.
11 Firavunun kâsesi elimdeydi. Üzümleri alıp firavunun kâsesine sıktım. Sonra kâseyi ona verdim.”
Kwaf Fir’auna kuwa yana a hannuna, na kuma ɗiba inabin na matse su cikin kwaf Fir’auna, na kuma sa kwaf ɗin a hannunsa.”
12 Yusuf, “Bu şu anlama gelir” dedi, “Üç çubuk üç gün demektir.
Yusuf ya ce masa, “Ga abin da mafarkin yake nufi, ‘Rassan nan uku, kwana uku ne.
13 Üç gün içinde firavun seni zindandan çıkaracak, yine eski görevine döneceksin. Geçmişte olduğu gibi yine ona sakilik yapacaksın.
Cikin kwana uku, Fir’auna zai fitar da kai, yă maido da kai a matsayinka, za ka kuwa sa kwaf Fir’auna cikin hannunsa, kamar yadda ka saba yi sa’ad da kake mai riƙon kwaf nasa.
14 Ama her şey yolunda giderse, lütfen beni anımsa. Bir iyilik yap, firavuna benden söz et. Çıkar beni bu zindandan.
Amma fa, sa’ad da kome ya zama maka da kyau, ka tuna da ni, ka kuma yi mini alheri, ka ambace ni wa Fir’auna, ka fid da ni daga wannan kurkuku.
15 Çünkü ben İbrani ülkesinden zorla kaçırıldım. Burada da zindana atılacak bir şey yapmadım.”
Gama da ƙarfi ne aka ɗauke ni daga ƙasar Ibraniyawa, ko a nan ma ban yi wani abin da ya cancanci a sa ni cikin kurkuku ba.’”
16 Fırıncıbaşı bu iyi yorumu duyunca, Yusuf'a, “Ben de bir düş gördüm” dedi, “Başımın üstünde üç sepet beyaz ekmek vardı.
Sa’ad da shugaban masu tuya ya ga cewa Yusuf ya ba da fassara mai gamsarwa, sai ya ce, wa Yusuf, “Ni ma na yi mafarki. A kaina, akwai kwanduna uku na burodi.
17 En üstteki sepette firavun için pişirilmiş çeşitli pastalar vardı. Kuşlar başımın üstündeki sepetten pastaları yiyorlardı.”
A kwandon na bisa, akwai kayan iri-iri da aka toya, masu kyau domin Fir’auna, amma tsuntsaye suka ci su a kwandon da yake kaina.”
18 Yusuf, “Bu şu anlama gelir” dedi, “Üç sepet üç gün demektir.
Yusuf ya ce, “Ga abin da mafarkin yake nufi, ‘Kwanduna uku, kwanaki uku ne.
19 Üç gün içinde firavun seni zindandan çıkarıp ağaca asacak. Kuşlar etini yiyecekler.”
Cikin kwana uku, Fir’auna zai fid da kai, yă rataye ka a kan itace. Tsuntsaye kuwa za su ci naman jikinka.’”
20 Üç gün sonra, firavun doğum gününde bütün görevlilerine bir şölen verdi. Görevlilerinin önünde baş sakisiyle fırıncıbaşını zindandan çıkardı.
To, a rana ta uku ne, ranar tunawa da haihuwar Fir’auna, ya kuwa yi biki wa dukan hafsoshinsa. Ya fid da shugaban masu shayarwa da kuma shugaban masu tuya a gaban hafsoshinsa.
21 Yusuf'un yaptığı yoruma uygun olarak baş sakisini eski görevine atadı. Baş saki firavuna şarap sunmaya başladı. Ama firavun fırıncıbaşını astırdı.
Ya mai da shugaban masu shayarwa a matsayinsa, saboda haka shugaban masu shayarwa ya sāke sa kwaf a hannun Fir’auna,
amma ya rataye shugaban masu tuya, kamar dai yadda Yusuf ya faɗa musu a fassarar mafarkan da suka yi.
23 Gelgelelim, baş saki Yusuf'u anımsamadı, unuttu gitti.
Shugaban masu shayarwa fa, bai tuna da Yusuf ba; ya mance da shi.