< Yaratiliş 39 >
1 İsmaililer Yusuf'u Mısır'a götürmüştü. Firavunun görevlisi, muhafız birliği komutanı Mısırlı Potifar onu İsmaililer'den satın almıştı.
To, aka kai Yusuf Masar, Fotifar wani mutumin Masar wanda yake ɗaya daga cikin hafsoshin Fir’auna, shugaban masu tsaro, ya saye shi daga mutanen Ishmayel waɗanda suka kai shi can.
2 RAB Yusuf'la birlikteydi ve onu başarılı kılıyordu. Yusuf Mısırlı efendisinin evinde kalıyordu.
Ubangiji kuwa yana tare da Yusuf, Yusuf kuwa yi nasara, ya zauna a gidan mutumin Masar maigidansa.
3 Efendisi RAB'bin Yusuf'la birlikte olduğunu, yaptığı her işte onu başarılı kıldığını gördü.
Sa’ad da maigidansa ya ga cewa Ubangiji yana tare da Yusuf, kuma cewa Ubangiji ya ba shi nasara a kome da ya yi,
4 Yusuf'tan hoşnut kalarak onu özel hizmetine aldı. Evinin ve sahip olduğu her şeyin sorumluluğunu ona verdi.
sai Yusuf ya sami tagomashi a idanunsa, ya kuma zama mai hidimarsa. Fotifar ya sa shi yă zama shugaba a gidansa, ya kuma danƙa masa kome da yake da shi.
5 Yusuf'u evinin ve sahip olduğu her şeyin sorumlusu atadığı andan itibaren RAB Yusuf sayesinde Potifar'ın evini kutsadı. Evini, tarlasını, kendisine ait her şeyi bereketli kıldı.
Daga lokacin da ya sa shi shugaban gidansa da kuma a kan dukan abin da yake da shi, sai Ubangiji ya albarkaci gidan mutumin Masar saboda Yusuf. Albarkar Ubangiji tana a kan kome da Fotifar yake da shi a gida da kuma a jeji.
6 Potifar sahip olduğu her şeyin sorumluluğunu Yusuf'a verdi; yediği yemek dışında hiçbir şeyle ilgilenmedi. Yusuf güzel yapılı, yakışıklıydı.
Saboda haka sai ya bar kome a ƙarƙashin kulawar Yusuf, bai dame kansa a wani abu ba sai dai abincin da yake ci. To, fa, Yusuf ƙaƙƙarfa ne, kyakkyawa kuma,
7 Bir süre sonra efendisinin karısı ona göz koyarak, “Benimle yat” dedi.
bayan an ɗan jima sai matar maigidansa ta fara sha’awar Yusuf, sai ta ce, “Zo ka kwana da ni!”
8 Ama Yusuf reddetti. “Ben burada olduğum için efendim evdeki hiçbir şeyle ilgilenme gereğini duymuyor” dedi, “Sahip olduğu her şeyin yönetimini bana verdi.
Amma ya ƙi. Ya ce mata, “Ga shi kome yana a ƙarƙashina, don haka ne ma maigidana bai dami kansa da wani abu a cikin gidan nan ba; kome da ya mallaka, ya danƙa ga kulawata.
9 Bu evde ben de onun kadar yetkiliyim. Senin dışında hiçbir şeyi benden esirgemedi. Sen onun karısısın. Nasıl böyle bir kötülük yapar, Tanrı'ya karşı günah işlerim?”
Babu wani da ya fi ni a wannan gida. Maigidana bai hana ni kome ba sai ke, saboda ke matarsa ce. Yaya fa, zan yi irin wannan mugun abu, in yi zunubi wa Allah?”
10 Potifar'ın karısı her gün kendisiyle yatması ya da birlikte olması için direttiyse de, Yusuf onun isteğini kabul etmedi.
Ko da yake ta yi ta yin wa Yusuf maganar kowace rana, amma ya ƙi yă kwana da ita, ko ma yă zauna da ita.
11 Bir gün Yusuf olağan işlerini yapmak üzere eve gitti. İçerde ev halkından hiç kimse yoktu.
Wata rana, ya shiga cikin gida don yă yi ayyukansa, ba wani daga cikin bayin gidan da yake ciki.
12 Potifar'ın karısı Yusuf'un giysisini tutarak, “Benimle yat” dedi. Ama Yusuf giysisini onun elinde bırakıp evden dışarı kaçtı.
Sai ta cafke shi a riga, ta ce, “Zo ka kwana da ni!” Amma ya bar rigarsa a hannunta, ya gudu ya fita daga gidan.
13 Kadın Yusuf'un giysisini bırakıp kaçtığını görünce,
Sa’ad da ta ga ya bar rigarsa a hannunta ya gudu ya fita daga gidan,
14 uşaklarını çağırdı. “Bakın şuna!” dedi, “Kocamın getirdiği bu İbrani bizi rezil etti. Yanıma geldi, benimle yatmak istedi. Ben de bağırdım.
sai ta kira bayin gidan ta ce musu, “Duba, an kawo mana wannan mutumin Ibraniyawa don yă ci mutuncinmu! Ya zo nan don yă kwana da ni, amma na yi ihu.
15 Bağırdığımı duyunca giysisini yanımda bırakıp dışarı kaçtı.”
Sa’ad da ya ji na yi ihu neman taimako, sai ya bar rigarsa kusa da ni, ya gudu ya fita daga gida.”
16 Efendisi eve gelinceye kadar Yusuf'un giysisini yanında alıkoydu.
Ta ajiye rigar kusa da ita sai da maigidansa ya dawo gida.
17 Ona da aynı şeyleri anlattı: “Buraya getirdiğin İbrani köle yanıma gelip beni aşağılamak istedi.
Sa’an nan ta faɗa masa wannan labari, “Mutumin Ibraniyawan, bawan da ka kawo mana, ya zo wurina don yă ci mutuncina.
18 Ama ben bağırınca giysisini yanımda bırakıp kaçtı.”
Amma da zarar na yi ihu neman taimako, sai ya bar rigarsa kusa da ni, ya gudu ya fita daga gida.”
19 Karısının, “Kölen bana böyle yaptı” diyerek anlattıklarını duyunca, Yusuf'un efendisinin öfkesi tepesine çıktı.
Sa’ad da maigidansa ya ji labarin da matarsa ta faɗa masa cewa, “Ga yadda bawanka ya yi da ni,” sai ya husata.
20 Yusuf'u yakalayıp zindana, kralın tutsaklarının bağlı olduğu yere attı. Ama Yusuf zindandayken
Maigidan Yusuf ya ɗauke shi ya sa a kurkuku, wurin da ake tsare’yan kurkukun sarki. Amma yayinda Yusuf yake can a cikin kurkuku,
21 RAB onunla birlikteydi. Ona iyilik etti. Zindancıbaşı Yusuf'tan hoşnut kaldı.
Ubangiji ya kasance tare da shi; ya nuna masa alheri, ya kuma sa ya sami tagomashi a idanun mai gadin kurkukun.
22 Bütün tutsakların yönetimini ona verdi. Zindanda olup biten her şeyden Yusuf sorumluydu.
Saboda haka mai gadin ya sa Yusuf ya zama shugaban dukan waɗanda aka tsare a kurkukun, Yusuf ne kuma yake lura da dukan abin da ake yi a can.
23 Zindancıbaşı Yusuf'un sorumlu olduğu işlerle hiç ilgilenmezdi. Çünkü RAB Yusuf'la birlikteydi ve yaptığı her işte onu başarılı kılıyordu.
Mai gadin ba ya sa kansa game da kome da yake ƙarƙashin kulawar Yusuf, gama Ubangiji yana tare da Yusuf, ya kuma ba shi nasara a cikin dukan abin da ya yi.