< Hezekiel 11 >
1 Ruh beni yine yukarıya kaldırıp RAB'bin Tapınağı'nın Doğu Kapısı'na götürdü. Kapının giriş bölümünde yirmi beş adam vardı. Aralarında halkın önderlerinden Azzur oğlu Yaazanya'yı, Benaya oğlu Pelatya'yı gördüm.
Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kawo ni ƙofar gidan Ubangiji wadda take fuskantar gabas. Can a mashigi zuwa ƙofar akwai mutum ashirin da biyar, na kuma ga a cikinsu akwai Ya’azaniya ɗan Azzur da Felatiya ɗan Benahiya, shugabannin jama’a.
2 RAB bana, “İnsanoğlu, bunlar kötülük tasarlayan ve bu kentte kötü öğüt veren adamlardır” dedi,
Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan su ne mutanen da suke ƙulla mugunta suna kuma ba da muguwa shawara a cikin wannan birni.
3 “Onlar, ‘Yıkım yakın değil, ev yapmanın zamanıdır. Bu kent kazan, biz de etiz’ diyorlar.
Suna cewa, ‘Lokaci bai yi kusa da za a gina gidaje ba? Wannan birni yana tukunyar dahuwa, mu ne kuwa naman.’
4 Bundan ötürü onları uyar, ey insanoğlu, onları uyar.”
Saboda haka yi annabci a kansu; yi annabci, ɗan mutum.”
5 Sonra RAB'bin Ruhu üzerime inip şunları söylememi buyurdu: “RAB şöyle diyor: Ey İsrail halkı, neler söylediğinizi ve neler düşündüğünüzü bilirim.
Sai Ruhun Ubangiji ya sauko a kaina, ya kuma faɗa mini in ce, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, haka kuke cewa, ya gidan Isra’ila, amma na san abin da yake a zuciyarku.
6 Bu kentte birçok kişi öldürdünüz, kentin sokaklarını ölülerle doldurdunuz.
Kun kashe mutane da yawa a wannan birni kuka kuma cika titunanta da gawawwaki.
7 “Bundan ötürü Egemen RAB şöyle diyor: Oraya attığınız ölüler et, kent de kazandır. Ama sizi kentin dışına süreceğim.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa gawawwakin da kuka zubar a can su ne naman, wannan birni kuwa ita ce tukunya, amma zan kore ku daga cikinta.
8 Kılıçtan korktunuz, ama ben üzerinize kılıç göndereceğim. Egemen RAB böyle diyor.
Kuna jin tsoron takobi, kuma takobi ne zan kawo muku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 Sizi kentten çıkarıp yabancıların eline teslim edeceğim. Sizi cezalandıracağım.
Zan kore ku daga birnin in miƙa ku a hannuwan baƙi in kuma azabtar da ku.
10 Kılıçla öldürüleceksiniz. Sizi İsrail sınırında cezalandıracağım. O zaman benim RAB olduğumu anlayacaksınız.
Za ku mutu ta wurin takobi, zan kuma hukunta ku a iyakokin Isra’ila. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
11 Bu kent sizin için kazan olmayacak, siz de onun içinde et olmayacaksınız. Sizi İsrail sınırında cezalandıracağım.
Wannan birni ba za tă zama muku tukunya ba, ba kuwa za ku zama nama a cikinta ba; zan hukunta ku a iyakokin Isra’ila.
12 O zaman benim RAB olduğumu anlayacaksınız. Kurallarımı izlemediniz, ilkelerime uymadınız; çevrenizdeki ulusların ilkelerine uydunuz.”
Za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji, gama ba ku bi ƙa’idodina ba balle ku kiyaye dokokina, amma kuka bi hanyoyin al’ummai kewaye da ku.”
13 Ben peygamberlikte bulunurken Benaya oğlu Pelatya öldü. Yüzüstü yere kapanıp, “Ah, ey Egemen RAB! Geri kalan İsrailliler'i büsbütün mü yok edeceksin?” diye yüksek sesle haykırdım.
Yanzu yayinda nake yin annabci, sai Felatiya ɗan Benahiya ya mutu. Sai na fāɗi rubda ciki na kuma yi kuka da babbar murya na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Za ka hallaka raguwar Isra’ila ƙaƙaf ne?”
14 RAB bana şöyle seslendi:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
15 “Ey insanoğlu, Yeruşalim'de yaşayanlar senin kardeşlerin, akrabaların ve öbür İsrailliler için, ‘Onlar RAB'den uzaklar, bu ülke mülk olarak bize verildi’ demişler.”
“Ɗan mutum,’yan’uwanka,’yan’uwanka waɗanda suke danginka na cikinka da kuma dukan gidan Isra’ila su ne waɗanda mutanen Urushalima suka ce, ‘Su ne da nisa daga Ubangiji; an ba mu wannan ƙasa ta zama mallakarmu.’
16 “Bu yüzden de ki, ‘Egemen RAB şöyle diyor: Onları uzaktaki uluslar arasına gönderdim, ülkeler arasına dağıttım. Öyleyken gittikleri ülkelerde kısa süre için onlara barınak oldum.’
“Saboda haka ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ko da yake na kore su zuwa cikin al’ummai na kuma warwatsa su cikin ƙasashe, duk da haka na zama wuri mai tsarki a gare su a ƙasashen da suka tafi.’
17 “De ki, ‘Egemen RAB şöyle diyor: Sizi uluslar arasından toplayacak, dağılmış olduğunuz ülkelerden geri getirecek, İsrail ülkesini yeniden size vereceğim.’
“Saboda haka, ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan tattaro ku daga al’ummai in kuma dawo da ku daga ƙasashen da aka warwatsa ku, zan kuwa sāke mayar muku da ƙasar Isra’ila.’
18 “Ülkeye dönecek, tiksindirici, iğrenç putları oradan söküp atacaklar.
“Za su dawo gare ta su kawar da dukan mugayen siffofi da gumaka masu banƙyama.
19 Onlara tek bir yürek vereceğim, içlerine yeni bir ruh koyacağım. İçlerindeki taş yüreği çıkarıp onlara etten bir yürek vereceğim.
Zan ba su zuciya ɗaya in kuma sa sabon ruhu a cikinsu; zan fid da zuciyar dutse daga gare su in kuma ba su zuciya ta nama.
20 O zaman kurallarımı izleyecek, ilkelerime uymaya özen gösterecekler. Onlar halkım olacak, ben de onların Tanrısı olacağım.
Sa’an nan za su bi ƙa’idodina su kuma yi hankali ga kiyaye dokokina. Za su zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnsu.
21 Tiksindirici, iğrenç putlara gönülden yönelenlere gelince, yaptıklarının aynısını başlarına getireceğim. Böyle diyor Egemen RAB.”
Amma game da waɗanda zukatansu suka karkata ga bin mugayen siffofi da gumakan banƙyama, zan sāka musu gwargwadon ayyukansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
22 Keruvlar kanatlarını açtı, tekerlekler yanlarında duruyordu. İsrail Tanrısı'nın görkemi onların üzerindeydi.
Sa’an nan kerubobi, tare da da’irori kusa da su, suka buɗe fikafikansu, ɗaukakar Allah kuwa tana a bisansu.
23 RAB'bin görkemi kentin ortasından yükselip kentin doğusundaki dağa kondu.
Ɗaukakar Ubangiji ta haura daga cikin birnin ta sauka a bisa dutse gabas da shi.
24 Görümde Tanrı'nın Ruhu beni yukarı kaldırıp Kildan ülkesindeki sürgünlerin yanına götürdü. Sonra gördüğüm görüm kayboldu.
Ruhu ya ɗaga ni sama ya kuma kawo ni ga masu zaman bauta a ƙasar Babilon cikin wahayin da Ruhun Allah ya bayar. Sa’an nan wahayin da na gani ya rabu da ni,
25 Ben de RAB'bin bana gösterdiği her şeyi sürgündekilere anlattım.
na kuwa faɗa wa masu zaman bautan dukan abin da Ubangiji ya nuna mini.