< Misir'Dan Çikiş 7 >

1 RAB, “Bak, seni firavuna karşı Tanrı gibi yaptım” dedi, “Ağabeyin Harun senin peygamberin olacak.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Duba, na maishe ka kamar Allah ga Fir’auna, ɗan’uwanka Haruna kuma zai zama annabinka.
2 Sana buyurduğum her şeyi ağabeyine anlat. O da firavuna İsrailliler'i ülkesinden salıvermesini söylesin.
Za ka faɗi kome da na umarce ka, ɗan’uwanka Haruna kuwa zai faɗa wa Fir’auna, yă bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa.
3 Ben firavunu inatçı yapacağım ki, belirtilerimi ve şaşılası işlerimi Mısır'da artırabileyim.
Amma zan taurare zuciyar Fir’auna, kuma ko da na ninka mu’ujizai da kuma alamu a Masar,
4 Ama firavun sizi dinlemeyecek. O zaman elimi Mısır'ın üzerine koyacağım ve onları ağır biçimde cezalandırarak halkım İsrail'i ordular halinde Mısır'dan çıkaracağım.
ba zai saurare ku ba. Don haka zan miƙa hannuna a kan Masar, in murƙushe ta da bala’i iri-iri, bayan haka zan fitar da taron mutanen Isra’ila daga ƙasar Masar ta wurin hukuntaina masu girma.
5 Mısır'a karşı elimi kaldırdığım ve İsrailliler'i aralarından çıkardığım zaman Mısırlılar benim RAB olduğumu anlayacak.”
Masarawa kuwa za su san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na miƙa hannuna a kan Masar, na kuma fitar da Isra’ilawa daga gare ta.”
6 Musa'yla Harun RAB'bin buyurduğu gibi yaptılar.
Musa da Haruna suka aikata yadda Ubangiji ya umarce su.
7 Firavunla konuştuklarında Musa seksen, Harun seksen üç yaşındaydı.
Musa yana da shekara tamanin da haihuwa, Haruna kuma yana da shekara tamanin da uku, sa’ad da suka yi magana da Fir’auna.
8 RAB Musa'yla Harun'a şöyle dedi:
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
9 “Firavun size, ‘Bir mucize yapın’ dediğinde, söyle Harun'a, değneğini alıp firavunun önüne atsın. Değnek yılan olacak.”
“Sa’ad da Fir’auna ya ce muku, ‘Aikata wani al’ajabi,’ sai ka ce wa Haruna, ‘Ɗauki sandanka ka jefa shi a ƙasa, a gaban Fir’auna,’ zai kuwa zama maciji.”
10 Böylece Musa'yla Harun firavunun yanına gittiler ve RAB'bin buyurduğu gibi yaptılar. Harun değneğini firavunla görevlilerinin önüne attı. Değnek yılan oluverdi.
Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna, suka yi yadda Ubangiji ya umarce su. Haruna ya jefa sandansa ƙasa, a gaban Fir’auna da bayinsa, sai sandan ya zama maciji.
11 Bunun üzerine firavun kendi bilgelerini, büyücülerini çağırdı. Mısırlı büyücüler de büyüleriyle aynı şeyi yaptılar.
Fir’auna kuwa ya kira masu hikima da masu sihiri, sai bokayen Masarawa ma suka yi irin abubuwan nan da bokancinsu.
12 Her biri değneğini attı, değnekler yılan oldu. Ancak Harun'un değneği onların değneklerini yuttu.
Kowannensu ya jefa sandansa ƙasa, ya kuwa zama maciji. Amma sandan Haruna ya haɗiye sandunansu.
13 Yine de, RAB'bin söylediği gibi firavun inat etti ve Musa'yla Harun'u dinlemedi.
Duk da haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurare su ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
14 RAB Musa'ya, “Firavun inat ediyor, halkı salıvermeyi reddediyor” dedi,
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Zuciyar Fir’auna taurariya ce, ya ƙi yă bar mutanen su tafi.
15 “Sabah git, firavun Nil'e inerken onu karşılamak için ırmak kıyısında bekle. Yılana dönüşen değneği eline al
Ka je wurin Fir’auna da safe, yayinda za shi kogi. Ka jira a bakin Nilu don ka sadu da shi, ka ɗauki sandan nan da ya canja zuwa maciji a hannunka.
16 ve ona de ki, ‘Halkımı salıver, çölde bana tapsınlar, demem için İbraniler'in Tanrısı RAB beni sana gönderdi. Ama sen şu ana kadar kulak asmadın.
Sa’an nan ka ce masa, ‘Ubangiji, Allah na Ibraniyawa, ya aiko ni in faɗa maka, Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada a hamada. Amma har yanzu ba ka yi biyayya ba.
17 Benim RAB olduğumu şundan anla, diyor RAB. İşte, elimdeki değneği ırmağın sularına vuracağım, sular kana dönecek.
Ga abin da Ubangiji ya ce, da wannan za ka san cewa ni ne Ubangiji. Da sandan da yake hannuna zan bugi ruwan Nilu, zai kuma zama jini.
18 Irmaktaki balıklar ölecek, ırmak leş gibi kokacak, Mısırlılar artık ırmağın suyunu içemeyecekler.’”
Kifi a ciki Nilu za su mutu, ruwan kuma zai yi ɗoyi; Masarawa ba za su iya shan ruwansa ba.’”
19 Sonra RAB Musa'ya şöyle buyurdu: “Harun'a de ki, ‘Değneğini al ve elini Mısır'ın suları üzerine –ırmakları, kanalları, havuzları, bütün su birikintileri üzerine– uzat, hepsi kana dönsün. Bütün Mısır'da tahta ve taş kaplardaki sular bile kana dönecek.’”
Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka ɗauki sandanka, ka miƙa hannunka kan ruwan Masar, kan kogunansu da rafuffukansu da kududdufansu da kuma dukan tafkunansu, za su zama jini.’ Jini zai kasance ko’ina a Masar, har ma a cikin abubuwan ajiyar ruwansu da aka yi da itace da kuma dutse.”
20 Musa'yla Harun RAB'bin buyurduğu gibi yaptılar. Harun firavunla görevlilerinin gözü önünde değneğini kaldırıp ırmağın sularına vurdu. Bütün sular kana dönüştü.
Musa da Haruna suka yi yadda Ubangiji ya umarta. Ya ɗaga sandansa a gaban Fir’auna da bayinsa, ya bugi ruwan Nilu, dukan ruwan kuwa ya zama jini.
21 Irmaktaki balıklar öldü, ırmak kokmaya başladı. Mısırlılar ırmağın suyunu içemez oldular. Mısır'ın her yerinde kan vardı.
Kifin da suke cikin Nilu suka mutu, kogin kuwa ya yi wari sosai yadda Masarawa ba su iya shan ruwan ba. Jini ya bazu ko’ina a Masar.
22 Mısırlı büyücüler de kendi büyüleriyle aynı şeyi yaptılar. RAB'bin söylediği gibi firavun inat etti ve Musa'yla Harun'u dinlemedi.
Amma bokayen Masar ma suka yi abubuwan nan da sihirinsu, sai zuciyar Fir’auna ta taurare; bai saurari Musa da Haruna ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
23 Olanlara aldırmadan sarayına döndü.
A maimakon yă saurara, sai ya juya ya koma fadarsa, bai ma damu da abin da aka yi ba.
24 Mısırlılar içecek su bulmak için ırmak kıyısını kazmaya koyuldular. Çünkü ırmağın suyunu içemiyorlardı.
Sai dukan Masarawa suka yi ta tonon gefen Nilu don su sami ruwan sha, domin ba su iya shan ruwan kogin ba.
25 RAB'bin ırmağı vurmasının üzerinden yedi gün geçti.
Kwana bakwai suka wuce bayan da Ubangiji ya bugi kogin.

< Misir'Dan Çikiş 7 >