< Misir'Dan Çikiş 22 >

1 “Bir adam öküz ya da davar çalıp boğazlar ya da satarsa, bir öküze karşılık beş öküz, bir koyuna karşılık dört koyun ödeyecektir.
“In mutum ya saci saniya ko tunkiya ya yanka, ko ya sayar, zai biya shanu biyar, a maimakon saniyar da ya sata, ko kuma tumaki huɗu, maimakon tunkiyar da ya sata.
2 “Bir hırsız bir eve girerken yakalanıp öldürülürse, öldüren kişi suçlu sayılmaz.
“In aka iske ɓarawo yana cikin ƙoƙarin shiga yă yi sata, aka buge shi har ya mutu, to, ba za a nemi alhakin jininsa daga wurin kowa ba;
3 Ancak olay güneş doğduktan sonra olmuşsa, kan dökmekten sorumlu sayılır. “Hırsız çaldığının karşılığını kesinlikle ödemelidir. Hiçbir şeyi yoksa, hırsızlık yaptığı için köle olarak satılacaktır.
amma in ya faru bayan wayewar gari, to, za a nemi alhakin jinin ɓarawon a hannun wanda ya bugi ɓarawon. “Ɓarawon da aka kama da abin da ya sata, dole yă yi cikakkiyar ramuwa, amma in ba shi da kome, dole a sayar da shi a biya abin da ya sata.
4 Çaldığı mal –öküz, eşek ya da koyun– sağ olarak elinde yakalanırsa, iki katını ödeyecektir.
In an sami dabbar, ko saniya, ko jaki, ko tunkiya da ya sata da rai a hannunsa, dole ɓarawon yă biya taran da za a ci shi, sau biyu na kowane ɗaya.
5 “Tarlada ya da bağda hayvanlarını otlatan bir adam, hayvanlarının başkasının tarlasında otlamasına izin verirse, zararı kendi tarlasının ya da bağının en iyi ürünleriyle ödeyecektir.
“In mutum ya sa dabbobinsa su yi kiwo a fili ko a gonar inabi, ya kuma bar dabbobinsa suka yi ɓarna a cikin gonar wani, sai a sa mai dabbar yă biya tara daga amfanin gonarsa mafi kyau duka.
6 “Birinin yaktığı ateş dikenlere sıçrar, ekin demetleri, tarladaki ekin ya da tarla yanarsa, yangın çıkaran kişi zararı ödeyecektir.
“In gobara ta tashi, ta kuma bazu cikin ƙayayyuwa, har ta cinye tarin hatsi, ko hatsin da ke tsaye, ko dukan gonar, dole wanda ya sa wutar, yă biya taran da aka yanka masa saboda ɓarnan da wutar ta yi.
7 “Biri komşusuna saklasın diye parasını ya da eşyasını emanet eder ve bunlar komşusunun evinden çalınırsa, hırsız yakalandığında iki katını ödemelidir.
“In mutum ya ba maƙwabcinsa azurfa, ko kaya ajiya, aka kuma sace su daga gidan maƙwabcin, in an kama ɓarawon, sai ɓarawon yă biya abin da ya sata har sau biyu.
8 Ama hırsız yakalanmazsa, komşusunun eşyasına el uzatıp uzatmadığının anlaşılması için ev sahibi yargıç huzuruna çıkmalıdır.
Amma in ba a sami ɓarawon ba, sai wanda aka yi ajiyar a gidansa, yă bayyana a gaban alƙalai a bincika ko yana da hannu a kan kayan maƙwabcinsa.
9 Emanete ihanet edilen konularda, öküz, eşek, koyun, giysi, herhangi bir kayıp eşya için ‘Bu benimdir’ diyen her iki taraf sorunu yargıcın huzuruna getirmelidir. Yargıcın suçlu bulduğu kişi komşusuna iki kat ödeyecektir.
A kowane rikicin cin amana da zai shiga tsakanin mutum biyu, ko a kan bijimi, ko jaki, ko tunkiya, ko riga, kai, ko a kan kowane irin abin da ya ɓata, da ma abin da aka samu a hannun wani, in akwai jayayya, za a kawo mutumin a gaban alƙalai. Wanda alƙali ya ce shi ne mai laifi, sai yă biya ɗayan taran da za a yanka, har sau biyu.
10 “Bir adam komşusuna korusun diye eşek, öküz, koyun ya da herhangi bir hayvan emanet ettiğinde, hayvan ölür, sakatlanır ya da kimse görmeden çalınırsa,
“In mutum ya ba da jaki, ko saniya, ko tunkiya, ko kowace dabba wa maƙwabcinsa ajiya, sai abin ya mutu, ko ya ji rauni, ko an ɗauke shi, in ba shaida,
11 komşusu adamın malına el uzatmadığına ilişkin RAB'bin huzurunda ant içmelidir. Mal sahibi bunu kabul edecek ve komşusu bir şey ödemeyecektir.
rantsuwa ce za tă raba tsakaninsu a gaban Ubangiji cewa babu hannunsa a dukiyar maƙwabcinsa. Mai dukiyar kuwa zai yarda da rantsuwar, ba za a bukaci wanda aka bai wa amanar yă biya ba.
12 Ama mal gerçekten ondan çalınmışsa, karşılığı sahibine ödenmelidir.
Amma idan satan dabbar ce aka yi, dole wanda aka bai wa ajiyar yă biya mai dabbar taran da aka ci masa.
13 Emanet hayvan parçalanmışsa, adam parçalarını kanıt olarak göstermelidir. Parçalanan hayvan için bir şey ödemeyecektir.
In naman jeji ne ya kashe ta, zai nuna gawar don shaida, ba za a kuwa sa maƙwabcin yă biya abin da naman jeji ya kashe ba.
14 “Biri komşusundan bir hayvan ödünç alır, sahibi yokken hayvan sakatlanır ya da ölürse, karşılığını ödemelidir.
“In mutum ya yi aron dabba daga wurin maƙwabcinsa, sai dabbar ta ji rauni ko ta mutu, yayinda mai shi ba ya nan, dole wanda ya yi aron dabbar yă biya.
15 Ama sahibi hayvanla birlikteyse, ödünç alan karşılığını ödemeyecektir. Hayvan kiralanmışsa, kayıp ödenen kiraya sayılmalıdır.”
Amma idan mai dabbar yana a wurin, wanda ya karɓa aron, ba zai biya kome ba. In an yi hayar dabbar ce, to, kuɗin da aka biya na hayar zai zama a madadin rashin.
16 “Eğer biri nişanlı olmayan bir kızı aldatıp onunla yatarsa, başlık parasını ödemeli ve onunla evlenmelidir.
“Idan mutum ya ruɗe budurwa, wadda ba wanda yake nemanta, ya kuma kwanta da ita, dole yă biya kuɗin aurenta, za tă kuma zama matarsa.
17 Babası kızını ona vermeyi reddederse, adam normal başlık parası neyse onu ödemelidir.
In mahaifinta ya ƙi yă ba da ita ga mutumin, dole mutumin yă biya dukiya daidai da abin da akan biya domin budurwai.
18 “Büyücü kadını yaşatmayacaksınız.
“Kada ku bar maiya da rai.
19 “Hayvanlarla cinsel ilişki kuran herkes öldürülecektir.
“Duk mutumin da ya yi jima’i da dabba dole a kashe shi.
20 “RAB'den başka bir ilaha kurban kesen ölüm cezasına çarptırılacaktır.
“Duk wanda ya yi hadaya ga wani allah ban da Ubangiji, dole a hallaka shi.
21 “Yabancıya haksızlık ve baskı yapmayacaksınız. Çünkü siz de Mısır'da yabancıydınız.
“Kada a wulaƙanta, ko a zalunci baƙo, domin dā ku baƙi ne a ƙasar Masar.
22 “Dul ve öksüzün hakkını yemeyeceksiniz.
“Kada ku ci zalin gwauruwa, ko maraya.
23 Yerseniz, bana feryat ettiklerinde onları kesinlikle işitirim.
In kuka yi haka, idan kuma suka yi kuka gare ni, zan ji kukansu.
24 Öfkem alevlenir, sizi kılıçtan geçirtirim. Kadınlarınız dul, çocuklarınız öksüz kalır.
Zan husata, in kuma kashe ku da takobi; matanku kuma, su ma su zama gwauraye,’ya’yanku kuwa su zama marayu.
25 “Halkıma, aranızda yaşayan bir yoksula ödünç para verirseniz, ona tefeci gibi davranmayacaksınız. Üzerine faiz eklemeyeceksiniz.
“In kun ba wa jama’ata matalauta da suke tsakaninku bashin kuɗi, kada ku zama kamar masu ba da rance; kada ku sa yă biya da ruwa.
26 Komşunuzun abasını rehin alırsanız, gün batmadan geri vereceksiniz.
In kun ɗauki mayafi maƙwabcinku a matsayin jingina, ku mayar masa kafin fāɗuwar rana,
27 Çünkü tek örtüsü abasıdır, ancak onunla örtünebilir. Onsuz nasıl yatar? Bana feryat ederse işiteceğim, çünkü ben iyilikseverim.
domin mayafin ne abin da yake da shi na rufe jikinsa. To, da me zai rufu yă yi barci? Sa’ad da ya yi mini kuka, zan ji, gama ni mai tausayi ne.
28 “Tanrı'ya sövmeyeceksiniz. Halkınızın önderine lanet etmeyeceksiniz.
“Kada ku yi maganar saɓo ga Allah, ko ku la’anta mai mulkin mutanenku.
29 “Ürününüzü ve şıranızı sunmakta gecikmeyeceksiniz. İlk doğan oğullarınızı bana vereceksiniz.
“Kada ku jinkirta fitar da zakarku daga rumbunanku, ko harajin kayan da kuka saya. “Dole ku ba ni’ya’yan farinku maza.
30 Öküzlerinize, davarlarınıza da aynı şeyi yapacaksınız. Yedi gün analarıyla kalacaklar, sekizinci gün onları bana vereceksiniz.
Ku yi haka da shanunku da tumakinku. Bari su kasance da iyayensu mata, har kwana bakwai, amma ku ba ni su a rana ta takwas.
31 “Benim kutsal halkım olacaksınız. Bunun içindir ki, kırda parçalanmış hayvanların etini yemeyecek, köpeklerin önüne atacaksınız.”
“Za ku kasance mutanena masu tsarki. Saboda kada ku ci naman da namun jeji suka kashe; ku jefa wa karnuka.

< Misir'Dan Çikiş 22 >