< Misir'Dan Çikiş 11 >
1 RAB Musa'ya, “Firavunun ve Mısır'ın başına bir bela daha getireceğim” dedi, “O zaman gitmenize izin verecek, sizi buradan adeta kovacak.
To, fa, sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan ƙara kawo annoba guda a kan Fir’auna da kan Masar. Bayan haka, zai bar ku, ku fita daga nan. Sa’ad da ya yi haka kuwa, zai kore ku gaba ɗaya.
2 Halkına söyle, kadın erkek herkes komşusundan altın, gümüş eşya istesin.”
Ka faɗa wa mutane cewa dukan maza da mata, su roƙi maƙwabtansu kayan azurfa da na zinariya.”
3 RAB İsrail halkının Mısırlılar'ın gözünde lütuf bulmasını sağladı. Musa da Mısır'da, firavunun görevlilerinin ve halkın gözünde çok büyüdü.
(Ubangiji ya sa mutane suka sami tagomashi a idon Masarawa, Musa kuwa ya sami girma sosai a cikin ƙasar Masar a gaban fadawan Fir’auna da kuma a gaban jama’ar.)
4 Musa firavuna şöyle dedi: “RAB diyor ki, ‘Gece yarısı Mısır'ı boydan boya geçeceğim.
Saboda haka Musa ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Wajen tsakar dare, zan ratsa dukan Masar.
5 Tahtında oturan firavunun ilk çocuğundan, değirmendeki kadın kölenin ilk çocuğuna kadar, hayvanlar dahil Mısır'daki bütün ilk doğanlar ölecek.
Kowane ɗan fari, namiji, a Masar zai mutu, daga kan ɗan fari na Fir’auna wanda zai ci gadon sarauta, har zuwa kan ɗan fari na baiwa, wadda take niƙa, da kuma dukan’yan farin shanu.
6 Bütün Mısır'da benzeri ne görülmüş, ne de görülecek büyük bir feryat kopacak.
Za a yi kuka mai zafi ko’ina a Masar, irin wadda ba a taɓa yi ba, ba kuwa za a ƙara yi ba.
7 İsrailliler'e ya da hayvanlarına bir köpek bile havlamayacak.’ O zaman RAB'bin İsrailliler'le Mısırlılar'a nasıl farklı davrandığını anlayacaksınız.
Amma a cikin Isra’ilawa, ba karen da zai yi haushi wa mutum ko dabba.’ Ta haka za ku sani Ubangiji zai bambanta tsakanin Masar da Isra’ila.
8 Bu görevlilerinin hepsi gelip önümde eğilecek, ‘Sen ve seni izleyenler, gidin!’ diyecekler. Ondan sonra gideceğim.” Musa firavunun yanından büyük bir öfkeyle ayrıldı.
Dukan fadawan nan naka za su zo wurina, suna fāɗi a gabana suna cewa, ‘Ka fita, kai da dukan jama’arka!’ Sa’an nan zan fita.” Daga nan sai Musa ya fita daga gaban Fir’auna a husace.
9 RAB Musa'ya, “Mısır'da şaşılası işlerim çoğalsın diye firavun sizi dinlemeyecek” demişti.
Ubangiji ya ce wa Musa, “Fir’auna zai ƙi kasa kunne gare ka, sai na ƙara aikata waɗansu mu’ujizai cikin Masar.”
10 Musa'yla Harun firavunun önünde bütün bu şaşılası işleri yaptılar. Ama RAB firavunu inatçı yaptı. Firavun İsrailliler'i ülkesinden salıvermedi.
Musa da Haruna suka aikata dukan waɗannan mu’ujizai a gaban Fir’auna, amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa ba.