< Vaiz 12 >

1 Bu yüzden zor günler gelmeden, “Zevk almıyorum” diyeceğin yıllar yaklaşmadan, Güneş, ışık, ay ve yıldızlar kararmadan Ve yağmurdan sonra bulutlar geri dönmeden, Gençlik günlerinde seni yaratanı anımsa.
Ka tuna da Mahaliccinka a kwanakin ƙuruciyarka, kafin lokacin wahala ta zo shekaru kuma su ƙarato sa’ad da za ka ce, “Ba na jin daɗinsu,”
2
kafin rana da haske wata da taurari su daina haske, gizagizai kuma su tattaru bayan da suka sheƙa ruwa;
3 O gün, evi bekleyenler titreyecek, Güçlüler eğilecek, Öğütücüler azaldığı için duracak, Pencereden bakanlar kararacak.
sa’ad da masu tsaron gida suke rawar jiki, majiya ƙarfi kuma suka rasa ƙarfi, sa’ad da masu niƙa suka daina don ba su da yawa, idanun da suke duba ta taga suka duhunta;
4 Değirmen sesi yavaşlayınca, Sokağa açılan çift kapı kapanacak, İnsanlar kuş sesiyle uyanacak, Ama şarkıların sesini duyamayacaklar.
sa’ad da aka rufe ƙofofin shiga tituna ƙarar niƙa kuma ya tsagaita; sa’ad da kukan tsuntsaye ta farkar da mutane, ba a kuwa jin waƙoƙinsu,
5 Dahası yüksek yerden, Sokaktaki tehlikelerden korkacaklar; Badem ağacı çiçek açacak, Çekirge ağırlaşacak, Tutku zayıflayacak. Çünkü insan sonsuzluk evine gidecek, Yas tutanlar sokakta dolaşacak.
sa’ad da mutane suke jin tsoron tudu da kuma hatsarori a tituna; sa’ad da itacen almon ya toho, fāra kuma ya yi ta jan jikinsa da ƙyar, sha’awace-sha’awace sun kafe. Daga nan mutum ya tafi madawwamiyar gidansa ya bar masu makoki suna ta yi.
6 Gümüş tel kopmadan, Altın tas kırılmadan, Testi çeşmede parçalanmadan, Kuyu makarası kırılmadan,
Ka tuna da shi, kafin igiyar azurfa ta katse, ko tasar zinariya ta fashe; kafin tulu yă ragargaje a maɓulɓula, ko guga ta tsinke a rijiya,
7 Toprak geldiği yere dönmeden, Ruh onu veren Tanrı'ya dönmeden, Seni yaratanı anımsa.
turɓaya ta koma ƙasar da ta fito, rai kuma yă koma ga Allah wanda ya ba da shi.
8 “Her şey boş” diyor Vaiz, “Bomboş!”
“Ba amfani! Ba amfani!” In ji Malami, “Gaba ɗaya ba amfani!”
9 Vaiz yalnız bilge değildi, bildiklerini halka da öğretiyordu. Hesap etti, araştırdı ve birçok özdeyişi düzene soktu.
Ba kawai Malami ya kasance mai hikima ba, amma kuma ya koyar da mutane. Ya yi tunani ya kuma yi binciken da ya tsara karin magana masu yawa.
10 Güzel sözler bulmaya çalıştı. Yazdıkları gerçek ve doğrudur.
Malami ya yi bincike don yă sami kalmomin da suka dace, kuma abin da ya rubuta daidai ne da kuma gaskiya.
11 Bilgelerin sözleri üvendire gibidir, derledikleri özdeyişlerse, iyi çakılan çivi gibi; bir tek Çoban tarafından verilmişler.
Kalmomin masu hikima kamar tsinken tsokanar dabba ne, tarin maganganunsu kuma kamar ƙusoshi ne da aka kafa daram, da aka ba wa Makiyayi guda.
12 Bunların dışındakilerden sakın, evladım. Çok kitap yazmanın sonu yoktur, fazla araştırma da bedeni yıpratır.
Ka yi hankali ɗana, game da duk wani ƙari a kan waɗannan. Wallafa littattafai ba shi da iyaka, kuma yawan karatu yakan gajiyar da jiki.
13 Her şey duyuldu, sonuç şu: Tanrı'ya saygı göster, buyruklarını yerine getir, Çünkü her insanın görevi budur.
Yanzu an ji kome; ga ƙarshen magana. Ka ji tsoron Allah ka kuma kiyaye umarnansa, gama wannan shi ne dukan hakkin mutum.
14 Tanrı her işi, her gizli şeyi yargılayacaktır, İster iyi ister kötü olsun.
Gama Allah zai shari’anta kowane irin aiki, har da waɗanda aka yi a ɓoye, ko nagari ne, ko mugu.

< Vaiz 12 >