< Yasa'Nin Tekrari 3 >

1 “Bundan sonra dönüp Başan'a doğru ilerledik. Başan Kralı Og'la ordusu bizimle savaşmak için Edrei'de karşımıza çıktı.
Biye da wannan muka juya muka haura ta hanyar wajen Bashan, inda Og, sarkin Bashan tare da dukan mayaƙansa suka fito don su sadu da mu a yaƙi, a Edireyi.
2 RAB bana, ‘Ondan korkma!’ dedi, ‘Çünkü onu da ordusuyla ülkesini de senin eline teslim ettim. Amorlular'ın Heşbon'da yaşayan Kralı Sihon'a yaptığının aynısını ona da yapacaksın.’
Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ji tsoronsa, gama na riga na miƙa shi da dukan mayaƙansa da kuma ƙasarsa gare ka. Yi masa abin da ka yi wa Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon.”
3 “Böylece Tanrımız RAB, Başan Kralı Og'u ve halkını da elimize teslim etti. Hiçbirini sağ bırakmadan hepsini yok ettik.
Saboda haka Ubangiji Allahnmu ya ba da Og, sarkin Bashan da dukan mayaƙansa a hannuwanmu. Muka karkashe su, ba mu bar wani da rai ba.
4 Bütün kentlerini ele geçirdik. Ele geçirmediğimiz tek kent kalmadı. Hepsi altmış kentti: Başan'da Og'un ülkesi olan bütün Argov bölgesi.
A wannan lokaci muka kwashe dukan biranensa. Babu ɗaya daga birane sittin da ba mu ɗauke daga gare su ba, dukan yankin Argob, masarautar Og a Bashan.
5 Bütün bu kentler yüksek surlarla, kapılarla, sürgülerle sağlamlaştırılmıştı. Bunlardan başka surla çevrilmemiş birçok köy de vardı.
Dukan biranen nan masu katanga da suke da tsayi masu ƙofofi da ƙyamare, akwai kuma manya ƙauyukan da ba su da katanga.
6 Heşbon Kralı Sihon'a yaptığımız gibi hepsini yok ettik. Her kenti, kadın, erkek ve çocuklarla birlikte, tümüyle yok ettik.
Muka hallaka su ƙaƙaf, kamar yadda muka yi wa Sihon sarkin Heshbon, muka hallaka kowace birni, maza, mata da yara.
7 Hayvanlara ve kentlerdeki mallara ise el koyduk.
Amma dukan dabbobin da kuma ganimar daga biranensu muka kwaso wa kanmu.
8 “Arnon Vadisi'nden Hermon Dağı'na kadar Şeria Irmağı'nın doğu yakasındaki toprakları iki Amorlu kralın elinden aldık.
A lokacin ne muka ƙwace wannan ƙasa daga hannun sarakunan nan biyu na Amoriyawa, wato, ƙasa wadda take a hayin Urdun, daga Kwarin Arnon zuwa Dutsen Hermon.
9 –Saydalılar Hermon'a Siryon, Amorlular'sa Senir derler.–
(Hermon ne Sidoniyawa suke kira Siriyon, Amoriyawa kuwa suna kira shi Senir.)
10 Ovadaki bütün kentleri, bütün Gilat'ı, Og'un ülkesine ait kentler olan Salka ve Edrei'ye uzanan bütün Başan'ı ele geçirdik.”
Muka kama dukan biranen da suke kan tudu, da dukan Gileyad, da dukan Bashan, har zuwa Saleka da Edireyi, biranen masarautar Og a Bashan.
11 –Refalılar'dan yalnız Başan Kralı Og sağ kalmıştı. Og'un Ammonlular'ın Rabba Kenti'ndeki yatağı demirdendi. O gün kullanılan arşın ölçüsüne göre uzunluğu dokuz, eni dört arşındı.–
(Og sarkin Bashan, ne kaɗai ya ragu cikin Refahiyawa. An yi gadonsa da ƙarfe, tsawon gadon ya fi ƙafa goma sha uku, fāɗinsa kuwa ƙafa shida ne. Yana nan a Rabba ta Ammonawa har yanzu.)
12 “O sırada ele geçirdiğimiz topraklardan Arnon Vadisi yakınındaki Aroer Kenti'nin kuzeyini, Gilat dağlık bölgesinin yarısıyla oradaki kentleri Ruben ve Gad oymaklarına verdim.
Cikin ƙasar da muka kwasa a lokacin, na ba wa mutanen Ruben da mutanen Gad yankin arewa na Arower ta Kwarin Arnon, haɗe da rabin ƙasar tudu ta Gileyad, tare da biranenta.
13 Gilat'ın geri kalan bölümünü ve Og'un ülkesi Başan'ı Manaşşe oymağının yarısına verdim. Başan'daki Argov bölgesi Refalılar ülkesi diye bilinirdi.
Sai kuma na ba wa rabin kabilar Manasse sauran rabin ƙasar tudu ta Gileyad da kuma dukan Bashan, masarautar Og (Wato, dukan yankin ƙasan nan na Argob a Bashan da dā ake kira ƙasar Refahiyawa.
14 Manaşşe soyundan Yair, Geşur ile Maaka sınırına dek uzanan bütün Argov bölgesini aldı. Başan denilen bölgeye kendi adını verdi. Orası bugün de Havvot-Yair diye anılıyor.
Yayir na zuriyar Manasse ya karɓi dukan yankin ƙasar Argob a Bashan har zuwa iyakar Geshurawa da Ma’akatiyawa. Sai ya kira ƙauyukan wurin da sunansa, Hawwot Yayir.)
15 Makir'e Gilat'ı verdim.
Na kuma ba da Gileyad ga Makir.
16 Gilat'la Arnon Vadisi arasında kalan toprakları Ruben ve Gad oymaklarına verdim. Vadinin ortası onların sınırıydı; Ammonlular'la sınırları ise Yabbuk Irmağı'ydı.
Amma ga mutanen Ruben da mutanen Gad, na ba da yankin da ya tashi daga Gileyad, ya gangara zuwa Kwarin Arnon (tsakiyar kwarin kuwa shi ne iyaka) ya fita zuwa Kogin Yabbok, wanda yake shi ne iyakar Ammonawa.
17 Arava'da da sınır Şeria Irmağı'ydı; Kinneret'ten Arava –Lut– Gölü'ne, doğuda Pisga yamaçlarının aşağısına kadar uzanıyordu.
Iyakarsa daga yamma kuwa shi ne Urdun a Araba, daga Kinneret zuwa Tekun Araba (wato, Tekun Gishiri) a gangaren gindin Dutsen Fisga wajen gabas.
18 “O zaman size şöyle buyruk verdim: ‘Tanrınız RAB mülk edinmek için bu ülkeyi size verdi. Bütün savaşçılarınız silahlı olarak İsrailli kardeşlerinizin önüsıra gitsin.
Na umarce ku a lokacin na ce, “Ubangiji Allahnku ya ba ku wannan ƙasa ku mallake ta. Dukan mayaƙanku za su haye da shirin yaƙi a gaban’yan’uwanku, Isra’ilawa.
19 Ancak RAB sizi rahata erdirdiği gibi onları da rahata erdirene ve onlar Tanrınız RAB'bin Şeria Irmağı'nın karşı yakasında kendilerine vereceği toprakları ele geçirene kadar, kadınlarınız, çocuklarınız ve hayvanlarınız –biliyorum, birçok hayvanınız var– size verdiğim kentlerde kalsın. Ondan sonra, her biriniz size verdiğim toprağa dönebilir.’”
Amma matanku, yaranku da dabbobinku (na sani kuna da dabbobi masu yawa), su ne za ku bari a garuruwan da na ba ku,
sai Ubangiji ya ba da hutu ga sauran’yan’uwanku, yadda ya yi da ku, su ma suka sami ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba su, a ƙetaren Urdun, sa’an nan kowannenku zai komo ga mallakar da na ba ku.”
21 “O zaman Yeşu'ya, ‘Tanrın RAB'bin bu iki krala neler yaptığını gözlerinle gördün’ dedim, ‘RAB gideceğin bütün ülkelere aynısını yapacak.
A lokacin nan na umarci Yoshuwa na ce, “Da idanunka ka ga dukan abin da Ubangiji Allahnku ya yi da waɗannan sarakuna biyu. Haka Ubangiji zai yi da dukan masarautai a can, inda za ku.
22 Onlardan korkmayın! Tanrınız RAB sizin için savaşacak.’
Kada ku ji tsoronsu, gama Ubangiji Allahnku zai yi yaƙi dominku.”
23 “Sonra RAB'be yalvardım:
A lokacin, na roƙi Ubangiji na ce,
24 ‘Ey Egemen RAB, büyüklüğünü ve güçlü elini bana göstermeye başladın. Gökte ve yerde senin yaptığın yüce işleri yapabilecek başka bir tanrı yok!
“Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka fara nuna wa bawanka ɗaukakarka da ikonka. Akwai wani allah a sama ko a duniya, wanda zai aikata waɗannan manyan ayyukan kamar ka?
25 İzin ver de Şeria Irmağı'ndan geçip karşı yakadaki o verimli ülkeyi, o güzel dağlık bölgeyi ve Lübnan'ı göreyim.’
Ina roƙonka, bari in ƙetare in ga ƙasa mai kyau ɗin nan a ƙetaren Urdun, wannan ƙasar mai kyau ta tuddai, da kuma Lebanon.”
26 “Ama RAB sizin yüzünüzden bana öfkelendi, yalvarışıma kulak asmadı. Bana, ‘Yeter artık!’ dedi, ‘Bir daha bu konudan söz etme bana.
Amma saboda ku, Ubangiji ya yi fushi da ni, bai kuwa saurare ni ba. Sai Ubangiji ya ce, “Ya isa haka, kada ka ƙara yin magana da ni game da wannan batu.
27 Pisga Dağı'na çık. Batıya, kuzeye, güneye, doğuya bak. Gözlerinle gör. Çünkü Şeria Irmağı'ndan geçmeyeceksin.
Haura zuwa ƙwanƙolin Fisga, ka dubi ƙasar da idanunka daga kowane gefe, yamma, da arewa, da kudu, da kuma gabas, gama ba za ka ƙetare wannan Urdun ba.
28 Yeşu'ya görev ver. Onu güçlendir ve yüreklendir. Çünkü bu halk Şeria Irmağı'ndan onun önderliğinde geçecek. Göreceğin toprakları halka o miras olarak verecek.’
Amma ka umarci Yoshuwa, ka ƙarfafa shi, ka kuma ba shi ƙarfin gwiwa, gama shi ne zai jagoranci wannan mutane su haye, yă kuma ba su gādon ƙasar da za ka gani.”
29 Böylece Beytpeor'un karşısındaki vadide kaldık.”
Sai muka zauna a kwari kusa da Bet-Feyor.

< Yasa'Nin Tekrari 3 >