< Yasa'Nin Tekrari 13 >

1 “Aranızdan bir peygamber ya da düş gören biri çıkarsa, bir belirtiyi ya da şaşılası bir olayı önceden bildirirse,
In wani annabi ko mai mafarkai, ya bayyana a cikinku, ya kuma yi muku shelar wata alama mai banmamaki ko al’ajabi,
2 ‘Bilmediğiniz başka ilahlara yönelip tapınalım’ derse, söz ettiği belirti, şaşılası olay gerçekleşse bile,
in kuwa alamar, ko al’ajabin da annabin ya yi faɗin ya faru, ya kuma ce, “Bari mu bi waɗansu alloli (allolin da ba ku sani ba) mu kuma yi musu sujada,”
3 o peygamberi ya da düş göreni dinlememelisiniz. Tanrınız RAB kendisini bütün yüreğinizle, bütün canınızla sevip sevmediğinizi anlamak için sizi sınamaktadır.
kada ku saurari kalmomin wannan annabi ko mai mafarki. Ubangiji Allahnku yana gwada ku ne don yă sani ko kuna ƙaunarsa da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku.
4 Tanrınız RAB'bin ardınca yürüyün, O'ndan korkun. Buyruklarına uyun, O'nun sözüne kulak verin. O'na kulluk edin, O'na bağlı kalın.
Ubangiji Allahnku ne za ku bi, shi ne kuma za ku girmama. Ku kiyaye umarnansa, ku kuma yi masa biyayya; ku bauta masa, ku kuma manne masa.
5 O peygamber ya da düş gören öldürülecek. O, sizi Mısır'dan çıkaran, köle olduğunuz ülkeden kurtaran Tanrınız RAB'be karşı gelmeye kışkırttı. Tanrınız RAB'bin yürümenizi buyurduğu yoldan sizi saptırmaya çalıştı. Aranızdaki kötülüğü ortadan kaldırmalısınız.
Dole a kashe wannan annabi ko mai mafarki, domin ya yi wa’azin tawaye ga Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar, ya fanshe ku daga ƙasar bauta; gama annabin nan ya yi ƙoƙari yă juye daga hanyar da Ubangiji Allahnku ya umarce ku, ku bi. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
6 “Öz kardeşin, oğlun, kızın, sevdiğin karın ya da en yakın dostun seni gizlice ayartmaya çalışır, senin ve atalarının önceden bilmediğiniz, dünyanın bir ucundan öbür ucuna dek uzakta, yakında, çevrenizde yaşayan halkların ilahları için, ‘Haydi gidelim, bu ilahlara tapalım’ derse,
In ɗan’uwanka, ko ɗanka, ko’yarka, ko matar da kake ƙauna, ko abokinka na kusa, a ɓoye ya ruɗe ka, yana cewa, “Mu je mu yi wa waɗansu alloli sujada” (allolin da ko kai, ko kakanninka ba su sani ba,
7
allolin mutanen kewayenku, ko na kusa, ko na nisa, daga wannan ƙarshen ƙasar zuwa wancan),
8 ona uymayacak, onu dinlemeyeceksin. Ona acımayacak, sevecenlik göstermeyecek, onu korumayacaksın.
kada ka yarda da shi, kada ma ka saurare shi. Kada ka ji tausayinsa. Kada ka haƙura da shi, ko ka tsare shi.
9 Onu kesinlikle öldüreceksin. Onu önce sen, sonra bütün halk taşa tutsun.
Dole ka kashe shi. Dole hannunka yă zama na farko a kisansa, sa’an nan hannuwan sauran dukan mutane.
10 Taşlayarak öldürün onu. Çünkü Mısır'dan, köle olduğunuz ülkeden sizi çıkaran Tanrınız RAB'den sizi saptırmaya çalıştı.
Ku jajjefe shi da duwatsu har sai ya mutu, domin ya yi ƙoƙari yă juye ku daga Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta kuma.
11 Böylece bütün İsrail bunu duyup korkacak. Bir daha aranızda buna benzer kötü bir şey yapmayacaklar.
Sa’an nan dukan Isra’ila za su ji su kuma tsorata, babu kuma wani a cikinku da zai ƙara yin irin wannan mugun abu.
12 “Tanrınız RAB'bin yaşamanız için size vereceği kentlerin birinde, içinizden kötü kişiler çıktığını ve, ‘Haydi, bilmediğiniz başka ilahlara tapalım’ diyerek kentlerinde yaşayan halkı saptırdıklarını duyarsanız,
In kuka ji an yi magana a kan wani daga cikin biranen da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku zauna a ciki
cewa mugaye sun taso a cikinku, suna rikitar da mutane a birni, suna cewa, “Mu je mu yi wa waɗansu alloli sujada” (allolin da ba ku sani ba),
14 araştıracak, inceleyecek, iyice soruşturacaksınız. Duyduklarınız gerçekse ve bu iğrenç olayın aranızda yapıldığı kanıtlanırsa,
to, sai ku bincike labarin sosai a hankali. In kuwa gaskiya ne, an kuma tabbatar wannan abin ƙyama ya faru a cikinku,
15 o kentte yaşayanları kesinlikle kılıçtan geçireceksiniz. Kenti yok edip orada yaşayan bütün halkı ve hayvanları kılıçtan geçireceksiniz.
dole a karkashe dukan waɗanda suke zama a wannan birni da takobi. Ku hallaka su ƙaƙaf, ku karkashe mutanen birnin da kuma dabbobinsa.
16 Yağmalanan malların tümünü toplayıp meydanın ortasına yığın. Kenti ve malları Tanrınız RAB'be tümüyle yakmalık sunu olarak yakın. Kent sonsuza dek yıkıntı halinde bırakılacak. Yeniden onarılmayacak.
Ku tattara dukan ganimar birnin a tsakiyar gari, ku ƙone birnin da kuma ganimar ƙurmus a matsayin hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji Allahnku. Birnin zai kasance kufai har abada, kada a sāke gina shi.
17 Yok edilecek mallardan hiçbir şey almayın. Böylece RAB'bin kızgın öfkesi yatışacak ve RAB atalarınıza içtiği ant uyarınca size acıyacak, sevecenlik gösterecek, sizi çoğaltacaktır.
Ba za a iske wani daga cikin abubuwan nan da aka haramta a hannuwanku ba, saboda Ubangiji yă juya daga fushinsa mai ƙuna, yă nuna jinƙai, yă ji tausayinku, yă kuma ƙara yawanku, kamar yadda ya alkawarta da rantsuwa ga kakanninku,
18 Çünkü Tanrınız RAB'bin sözünü dinleyeceksiniz. Böylece bugün size bildirdiğim buyruklara uyup O'nun gözünde doğru olanı yapmış olacaksınız.”
domin kun yi biyayya da Ubangiji Allahnku, kuna kiyaye dukan umarnan da nake ba ku a yau, kuna kuma aikata abin da yake daidai a idanunsa.

< Yasa'Nin Tekrari 13 >