< Amos 4 >

1 Ey sizler, Samiriye Dağı'ndaki Başan inekleri, Yoksula baskı yapan, Mazlumu ezen, Beylerine, “Getir de içelim!” diyen hanımlar! Kulak verin şu sözlere:
Ku kasa kunne ga wannan, ya ku shanun Bashan a kan Dutsen Samariya, ku matan da kuke cin zalin matalauta, kuke kuma danne matalauta, kuna kuma ce wa mazanku, “Ku kawo mana abin sha!”
2 Egemen RAB kutsallığı üstüne ant içerek şöyle dedi: “İşte geliyor o günler; Sizi et kancalarıyla, En son kalanlarınızı balık çengelleriyle götürecekleri günler.
Ubangiji Mai Iko Duka ya rantse da tsarkinsa. “Tabbatacce lokaci yana zuwa da za a jawo ku da ƙugiyoyi, na ƙarshenku za a kama da ƙugiyar kifi.
3 Her biriniz karşınızdaki gedikten çıkacak, Harmon'a atılacaksınız.” RAB böyle diyor.
Dukanku za ku wuce ta kai tsaye ta inda katangar ta tsage, za a jefar da ku a Harmon,” in ji Ubangiji.
4 “Beytel'e gelip günah işleyin, Gilgal'a gelip daha da günah işleyin! Her sabah kurbanlarınızı, Üç günde bir de ondalıklarınızı getirin.
“Ku tafi Betel ku yi ta aikata zunubi; ku je Gilgal ku ƙara yin zunubi. Ku kawo hadayunku kowace safiya, zakkarku kowace shekara uku.
5 Şükran sunusu olarak mayalı ekmek yakın, Gönülden verdiğiniz sunuları açıklayıp duyurun! Çünkü bundan hoşlanıyorsunuz, ey İsrailliler.” Egemen RAB böyle diyor.
Ku ƙona burodinku mai yisti kamar hadaya ta godiya, ku yi fariya game da hadayunku na yarda rai, ku yi taƙama game da su, ya ku Isra’ilawa, gama abin da kuke jin daɗin aikata ke nan,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
6 “Bütün kentlerinizde açlıktan nefesiniz koktu, Bulunduğunuz her yerde size kıtlık verdim, Yine de bana dönmediniz.” RAB böyle diyor.
“Na bar ku da yunwa a kowace birni, da kuma rashin abinci a kowane gari, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,” in ji Ubangiji.
7 “Hasat mevsimine daha üç ay varken, Sizden yağmuru da esirgedim. Bir kente yağmur yağdırdım, Öbürüne yağdırmadım. Bir tarla yağmur aldı, Öteki almayıp kurudu.
“Na kuma hana muku ruwan sama tun shuke-shuken suna wata uku kafin lokacin girbi. Na sa aka yi ruwan sama a wani gari, sai na hana a yi a wani gari. Wata gona ta sami ruwan sama; wata gona kuma ta bushe.
8 Su bulmak için Kent kent sersemce dolaştınız; Suya doyamadınız, Yine de bana dönmediniz.” RAB böyle diyor.
Mutane suna tangaɗi daga gari zuwa gari suna neman ruwa amma ba su sami isashen ruwan sha ba, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,” in ji Ubangiji.
9 “Samyeli ve küfle sizi cezalandırdım, Mahvettim bağlarınızı, bahçelerinizi, İncir ve zeytin ağaçlarınızı çekirge yedi, Yine de bana dönmediniz.” RAB böyle diyor.
“Sau da yawa na ɓata gonakinku da fumfuna da kuma cuta. Fāri suka cinye itatuwanku na inabi da na ɓaure, da na zaitun duk da haka ba ku juyo gare ni ba,” in ji Ubangiji.
10 “Mısır'da olduğu gibi Aranıza salgın hastalık gönderdim, Kılıçtan geçirdim yiğitlerinizi, Atlarınızı düşmanlarınıza verdim, Ordugahınızın pis kokusunu burunlarınıza doldurdum; Yine de bana dönmediniz.” RAB böyle diyor.
“Na aiko muku annoba yadda na yi a Masar. Na karkashe samarinku da takobi, tare da kamammun dawakanku. Na cika hancinku da warin sansaninku, duk da haka ba ku juyo gare ni ba” in ji Ubangiji.
11 “Sodom ve Gomora'yı altüst ettiğim gibi, Altüst ettim içinizden bazılarını. Ateşten kurtarılan yanık odun parçasına döndünüz, Yine de yönelmediniz bana.” RAB böyle diyor.
“Na hallaka waɗansunku kamar yadda na hallaka Sodom da Gomorra. Kuna kama da itace mai cin wutar da na cire daga cikin wuta, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,” in ji Ubangiji.
12 “Bu yüzden sana şunu yapacağım, ey İsrail. Yapacaklarım için Tanrın'ı karşılamaya hazırlan, ey İsrail!”
“Saboda haka ga abin da zan yi da ku, ya Isra’ila, don kuwa zan yi muku haka, sai ku yi shirin gamuwa da Allahnku, ya Isra’ila.”
13 Çünkü dağlara biçim veren, Rüzgarı yaratan, düşüncelerini insana bildiren, Şafağı karanlığa çeviren, Dünyanın yüksek yerlerine ayak basan işte O'dur, O'nun adı RAB, Her Şeye Egemen Tanrı'dır.
Shi wanda ya yi duwatsu, ya halicci iska, ya kuma bayyana wa mutum tunaninsa, shi wanda ya juya safiya ta zama duhu yana takawa a wurare masu tsawo na duniya, Ubangiji Allah Maɗaukaki ne sunansa.

< Amos 4 >