< 2 Samuel 24 >
1 RAB İsrail halkına yine öfkelendi. Davut'u onlara karşı kışkırtarak, “Git, İsrail ve Yahuda halkını say” dedi.
Fushin Ubangiji ya sāke ƙuna a kan Isra’ila, sai ya zuga Dawuda, yana cewa, “Je ka ƙidaya Isra’ila da Yahuda.”
2 Kral, yanında bulunan ordu komutanı Yoav'a şu buyruğu verdi: “Dan'dan Beer-Şeva'ya dek İsrail'in bütün oymaklarına gidip halkı sayın ki, halkın sayısını bileyim.”
Saboda haka sarki ya ce wa Yowab da komandodin da suke tare da shi, “Tafi cikin dukan kabilan Isra’ila, daga Dan har zuwa Beyersheba, ku ƙidaya mayaƙa don in san yawansu.”
3 Ama Yoav, “RAB Tanrın halkını yüz kat daha çoğaltsın, efendim kralım da bunu görsün!” diye karşılık verdi, “Ancak, efendim kralım neden bunu istiyor?”
Amma Yowab ya ce wa sarki, “Ubangiji Allahnka ya sa mayaƙan su ƙaru sau ɗari fiye da yadda suke, har ranka yă daɗe, sarki yă gani da idonsa. Me ya sa ranka yă daɗe, sarki yake so yă yi abu haka?”
4 Gelgelelim kralın sözü Yoav'la birlik komutanlarının sözünden baskın çıktı. Böylece kralın yanından ayrılıp İsrail'de sayım yapmaya gittiler.
Duk da haka, maganar sarki ya rinjayi Yowab da komandodin soja, sai suka tashi daga gaban sarki, suka tafi su ƙirga mayaƙan Isra’ila.
5 Şeria Irmağı'ndan geçerek Aroer yakınında, vadinin ortasındaki kentin güneyinde konakladılar. Oradan Gat'ı, Yazer'i, Gilat'ı, Tahtim-Hodşi topraklarını, Dan-Yaan'ı geçip Sayda'ya vardılar.
Bayan suka ƙetare Urdun, sai suka yi sansani kusa da Arower, kudu da garin da yake cikin kwari, sa’an nan suka ratsa ta wajen Gad, suka ci gaba zuwa Yazer.
Suka tafi Gileyad ta yankin Tatim Hodshi, sa’an nan suka tafi Dan Ya’an, suka kuma yi wajen kewaye Sidon.
7 Sonra Sur Kalesi'ne, Hivliler'le Kenanlılar'ın bütün kentlerine uğradılar. Sonunda Yahuda ülkesinin Negev bölgesindeki Beer-Şeva'ya ulaştılar.
Sa’an nan suka yi ta wajen kagarar Taya da dukan garuruwan Hiwiyawa da Kan’aniyawa. A ƙarshe, suka ci gaba zuwa Beyersheba a Negeb na Yahuda.
8 Dokuz ay yirmi gün ülkeyi baştan başa dolaştıktan sonra Yeruşalim'e döndüler.
Bayan suka ratsa dukan ƙasashen, a ƙarshe suka koma Urushalima, bayan wata tara da kwana ashirin.
9 Yoav sayımın sonucunu krala bildirdi: İsrail'de kılıç kuşanabilen sekiz yüz bin, Yahuda'daysa beş yüz bin kişi vardı.
Yowab ya ba wa sarki jimillar yawan mayaƙan. A Isra’ila akwai mutum dubu ɗari takwas da za su iya riƙe takobi. A Yahuda kuwa mutum dubu ɗari biyar.
10 Davut sayım yaptıktan sonra kendisini suçlu buldu ve RAB'be, “Bunu yapmakla büyük günah işledim!” dedi, “Ya RAB, lütfen kulunun suçunu bağışla. Çünkü çok akılsızca davrandım.”
Bayan Dawuda ya ƙidaya mayaƙan, lamirinsa ya kāshe shi, sai ya ce wa Ubangiji, “Ya Ubangiji na yi laifi ƙwarai a kan abin da na yi. Ina roƙonka ka gafarta wa bawanka. Na yi wauta ƙwarai.”
11 Ertesi sabah Davut uyandığında, RAB Davut'un bilicisi Peygamber Gad'a şöyle dedi: “Gidip Davut'a de ki, ‘RAB şöyle diyor: Önüne üç seçenek koyuyorum. Bunlardan birini seç de sana onu yapayım.’”
Kafin Dawuda yă tashi da safe kashegari, maganar Ubangiji ta riga ta zo wa annabin nan Gad, mai duban nan na Dawuda. Ubangiji ya ce,
“Je ka faɗa wa Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, ina ba ka zaɓi uku. Ka zaɓi ɗaya daga cikinsu don in aikata maka shi.’”
13 Gad Davut'a gidip durumu anlattı ve şöyle dedi: “Ülkende yedi yıl kıtlık mı olsun? Yoksa seni kovalayan düşmanlarının önünden üç ay kaçmak mı istersin? Ya da ülkende üç gün salgın hastalık mı olsun? Beni gönderene ne yanıt vereyim, şimdi iyice düşün.”
Sai Gad ya zo wurin Dawuda ya ce masa, “Kana so a yi yunwa shekara uku a ƙasarka? Ko kana so ka yi ta gudu a gaban abokan gābanka har wata uku? Ko kuwa ka fi so a yi annoba kwana uku a ƙasarka? Yanzu, sai ka yi tunani, ka yanke shawarar game da amsar da zan mayar wa wanda ya aiko ni.”
14 Davut, “Sıkıntım büyük” diye yanıtladı, “İnsan eline düşmektense, RAB'bin eline düşelim. Çünkü O'nun acıması büyüktür.”
Dawuda ya ce wa Gad, “Na shiga uku. Gara mu fāɗa a hannuwan Ubangiji gama alherinsa da girma yake. Amma fa kada ka bar ni in fāɗa a hannun mutane.”
15 Bunun üzerine RAB o sabahtan belirlenen zamana dek İsrail ülkesine salgın hastalık gönderdi. Dan'dan Beer-Şeva'ya dek halktan yetmiş bin kişi öldü.
Saboda haka Ubangiji ya aika da annoba a kan Isra’ila tun daga safe har zuwa lokacin da aka ƙayyade, mutum dubu saba’in kuwa daga Dan zuwa Beyersheba suka mutu.
16 Melek Yeruşalim'i yok etmek için elini uzatınca, RAB göndereceği yıkımdan vazgeçti. Halkı yok eden meleğe, “Yeter artık! Elini çek” dedi. RAB'bin meleği Yevuslu Aravna'nın harman yerinde duruyordu.
Da mala’ikan Ubangiji ya miƙa hannunsa wajen Urushalima, don yă hallaka ta, sai Ubangiji ya tsai da masifar, ya ce wa mala’ikan da yake wahal da mutane, “Ya isa, ka janye hannunka.” A lokacin kuwa Mala’ikan Ubangiji yana tsaye a masussukar Arauna, mutumin Yebus.
17 Davut, halkı öldüren meleği görünce, RAB'be, “Günah işleyen benim, ben suç işledim” dedi, “Bu koyunlar ne yaptı ki? Ne olur beni ve babamın soyunu cezalandır.”
Da Dawuda ya ga mala’ikan da ya bubbugi mutane, sai ya ce wa Ubangiji, “Ni ne na yi zunubi, na kuma yi abin da ba daidai ba. Waɗannan tumaki ne kawai. Me suka yi? Bari hukuncinka yă sauko a kaina da iyalina.”
18 O gün Gad Davut'a gitti. Ona, “Gidip Yevuslu Aravna'nın harman yerinde RAB'be bir sunak kur” dedi.
A ranar, Gad ya koma wurin Dawuda ya ce, “Ka tashi, ka tafi ka gina wa Ubangiji bagade a masussukar Arauna, mutumin Yebus.”
19 Davut Gad'ın sözü uyarınca RAB'bin buyurduğu gibi gitti.
Saboda haka Dawuda ya haura, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Gad.
20 Aravna bakınca kralla görevlilerinin kendisine doğru yaklaştıklarını gördü. Varıp kralın önünde yüzüstü yere kapandı.
Da Arauna ya hangi Dawuda da mutanensa suna zuwa wajensa, sai ya fita a guje, ya je ya rusuna a gaban sarki.
21 Sonra, “Efendim kral niçin kulunun yanına geldi?” diye sordu. Davut, “RAB'be bir sunak kurmak üzere harman yerini senden satın almak için” diye yanıtladı, “Öyle ki, salgın hastalık halkın üzerinden kalksın.”
Arauna ya ce, “Me ya sa ranka yă daɗe, sarki ya zo wajen bawansa?” Dawuda ya ce, “Don in saya masussukarka, saboda in gina wa Ubangiji bagade don a tsayar da annoban da suke a bisa mutane.”
22 Aravna, “Efendim kral uygun gördüğünü alıp RAB'be sunsun” dedi, “İşte yakmalık sunu için öküzler ve odun için düvenlerle öküzlerin takımları!
Arauna ya ce wa Dawuda, “Bari ranka yă daɗe, sarki yă ɗauki duk abin da ya ga dama yă miƙa shi. Ga shanu, don hadaya ta ƙonawa, ga kuma kayan masussuka da itacen shanu, don itace.”
23 Ey kral, Aravna bütün bunları sana veriyor.” Sonra ekledi: “RAB Tanrın senden hoşnut olsun!”
Dukan wannan, ranka yă daɗe, Arauna ya ba wa sarki. Arauna ya kuma ce, “Bari Ubangiji Allahnka yă karɓa.”
24 Ne var ki kral, “Olmaz!” dedi, “Senden malını kesinlikle bir ücret karşılığında satın alacağım. Çünkü Tanrım RAB'be karşılığını ödemeden yakmalık sunular sunmam.” Böylece Davut harman yerini ve öküzleri elli şekel gümüş karşılığında satın aldı.
Amma sarki ya ce wa Arauna, “A’a, dole in biya ka saboda waɗannan. Ba yadda zan miƙa wa Ubangiji Allahna hadayun ƙonawa da bai ci mini kome ba.” Sai Dawuda ya saya, ya kuma biya masussukar, da shanun a bakin shekel hamsin na azurfa.
25 Davut orada RAB'be bir sunak kurup yakmalık sunuları ve esenlik sunularını sundu. RAB de ülkeyle ilgili yakarıyı yanıtladı ve salgın hastalık İsrail'den kaldırıldı.
Dawuda ya gina wa Ubangiji bagade a wurin, ya kuma miƙa masa hadaya ta ƙonawa, da hadaya ta salama. Sa’an nan Ubangiji ya amsa addu’o’in a madadin ƙasar, aka kuma kawar wa Isra’ila annoban.