< 2 Krallar 16 >

1 İsrail Kralı Remalya oğlu Pekah'ın krallığının on yedinci yılında Yotam oğlu Ahaz Yahuda Kralı oldu.
A shekara ta goma sha bakwai ta mulkin Feka ɗan Remaliya, Ahaz ɗan Yotam sarkin Yahuda ya fara mulki.
2 Ahaz yirmi yaşında kral oldu ve Yeruşalim'de on altı yıl krallık yaptı. Tanrısı RAB'bin gözünde doğru olanı yapan atası Davut gibi davranmadı.
Ahaz ya zama sarki yana da shekara ashirin, ya kuma yi mulki shekara goma sha shida a Urushalima ba kamar Dawuda mahaifinsa ba. Ahaz bai yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji Allahnsa ba.
3 İsrail krallarının yolunu izledi; hatta RAB'bin İsrail halkının önünden kovmuş olduğu ulusların iğrenç törelerine uyarak oğlunu ateşte kurban etti.
Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila har ya miƙa ɗansa hadaya a wuta, yana bin hanyoyin banƙyama na al’ummai da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
4 Puta tapılan yerlerde, tepelerde, bol yapraklı her ağacın altında kurban kesip buhur yaktı.
Ya miƙa hadaya, ya kuma ƙona turare a masujadan tudu, da kan tuddai, da kuma a ƙarƙashin kowane babban itace.
5 Aram Kralı Resin'le İsrail Kralı Remalya oğlu Pekah Yeruşalim'e yürüdüler. Kenti kuşattılarsa da Ahaz'ı yenemediler.
Sai Rezin sarkin Aram, da Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila suka haura don su kai wa Urushalima hari, suka kuma kewaye Ahaz, amma ba su iya shan ƙarfinsa ba.
6 O sırada Aram Kralı Resin Eylat'ı geri alıp Yahudalılar'ı oradan sürdü. Edomlular Eylat'a yerleşti. Bugün de orada yaşıyorlar.
A wannan lokaci, Rezin sarkin Aram ya sāke ƙwato Elat wa Aram ta wurin korar Yahuda. Sa’an nan mutanen Edom suka mamaye Elat suna kuwa zaune a can har yau.
7 Ahaz, Asur Kralı Tiglat-Pileser'e: “Senin kulun kölenim; gel, bana saldıran Aram ve İsrail krallarının elinden beni kurtar” diye ulaklar gönderdi.
Ahaz ya aika a faɗa wa Tiglat-Fileser sarkin Assuriya cewa, “Ni abokin tarayyarka ne kuma mai dogara da kai. Ka haura ka cece ni daga hannun sarkin Aram da hannun sarkin Isra’ila waɗanda suke kawo mini hari.”
8 RAB'bin Tapınağı'nda ve sarayın hazinelerinde bulunan altın ve gümüşü armağan olarak Asur Kralı'na gönderdi.
Ahaz ya ɗauki azurfa da zinariyar da suke a haikalin Ubangiji da suke kuma a ma’ajin fada ya aika wa sarkin Assuriya kyauta.
9 Asur Kralı Ahaz'ın isteğini olumlu karşıladı, saldırıp Şam'ı ele geçirdi. Kent halkını Kîr'e sürüp Resin'i öldürdü.
Sai sarkin Assuriya ya ji roƙonsa. Ya tashi ya fāɗa wa Damaskus da hari ya kuma kame ta. Ya kwashi mazaunanta zuwa Kir, ya kuma kashe Rezin.
10 Kral Ahaz, Asur Kralı Tiglat-Pileser'i karşılamak için Şam'a gittiğinde, oradaki sunağı gördü. Aynısını yaptırmak için sunağın bütün ayrıntılarını gösteren bir planı ve maketi Kâhin Uriya'ya gönderdi.
Sa’an nan sarki Ahaz ya tafi Damaskus don yă sadu da Tiglat-Fileser sarkin Assuriya. Da ya kai can sai ya ga wani bagade a Damaskus, sai ya aika wa Uriya firist, da siffar bagaden, da fasalinsa, da cikakken bayanin bagaden.
11 Kâhin Uriya, Kral Ahaz Şam'dan dönünceye kadar, onun göndermiş olduğu maketin tıpkısı bir sunak yaptı.
Saboda haka Uriya firist ya gina bagaden bisa ga tsarin da Sarki Ahaz ya aika masa daga Damaskus, ya kuma gama shi kafin Sarki Ahaz yă dawo.
12 Kral Şam'dan dönünce sunağı gördü, yaklaşıp üzerinde sunular sundu.
Da sarki ya dawo daga Damaskus ya ga bagaden, sai ya tafi kusa da shi ya kuma miƙa hadaya a bisansa.
13 Yakmalık sunuları ve tahıl sunularını sundu, dökmelik sunuyu boşalttı, esenlik sunusunun kanını sunağın üzerine döktü.
Ya miƙa hadayarsa ta ƙonawa da ta hatsi, ya zuba hadayarsa ta sha, ya kuma yayyafa jinin hadayunsa ta zumunci a bisa bagaden.
14 RAB'bin huzurundaki tunç sunağı tapınağın önünden, yeni sunakla tapınağın arasındaki yerinden getirtip yeni sunağın kuzeyine yerleştirdi.
Sai ya cire bagaden tagulla wanda aka keɓe ga Ubangiji, ya sa shi a gaban haikalin wato, tsakanin ƙofar shiga haikalin Ubangiji da sabon bagaden. Ya ajiye shi a gefen arewa na sabon bagaden.
15 Kral Ahaz Kâhin Uriya'ya şu buyrukları verdi: “Sabahın yakmalık sunusuyla akşamın tahıl sunusunu, kralın yakmalık ve tahıl sunusunu, ayrıca ülke halkının yakmalık, tahıl ve dökmelik sunularını bu büyük sunağın üzerinde sun; yakmalık sunuların ve kurbanların kanını onun üzerine dök. Ama tunç sunağı geleceği bilmek için kendim kullanacağım.”
Sarkin Ahaz ya umarci Uriya cewa, “A kan babban sabon bagade, ka miƙa hadayar ƙonawa ta safe, da hadayar hatsi ta yamma, da hadayar sarki ta ƙonawa da hadayarsa ta hatsi, da hadaya ta dukan jama’ar ƙasar, tare da hadayan hatsinsu da kuma ta sha. Ka yayyafa jinin hadayun ƙonawa a kan bagade. Amma zan yi amfani da bagaden tagulla don neman bishewa.”
16 Kâhin Uriya Kral Ahaz'ın bütün buyruklarını yerine getirdi.
Uriya firist kuwa ya yi duk abin da Sarki Ahaz ya umarta.
17 Kral Ahaz tapınaktaki kazanların üzerine oturduğu ayaklıkların yan aynalıklarını söküp kazanları kaldırdı. Havuzu tunç boğaların üzerinden indirip taş bir döşeme üzerine yerleştirdi.
Sarkin Ahaz ya kawar da katakon ya kuma ɗauke tasoshin daga mazauninsu da ake iya matsarwa. Ya ɗauke ƙaton kwano mai suna Teku daga kan bijiman tagullar da ya tallafe su ya ajiye a kan mazaunin dutse.
18 Asur Kralı'nı hoşnut etmek için RAB'bin Tapınağı'na konan kral kürsüsünün setini kaldırıp kralın tapınağa girmek için kullandığı özel kapıyı kapattı.
Ya kawar da rumfa Asabbacin da aka gina a haikalin, ya kuma kawar da mashigin sarki na waje da haikalin Ubangiji, duk dai don yă gamshi sarkin Assuriya.
19 Ahaz'ın krallığı dönemindeki öteki olaylar ve yaptıkları Yahuda krallarının tarihinde yazılıdır.
Game da sauran ayyukan mulkin Ahaz, abubuwan da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
20 Ahaz ölüp atalarına kavuşunca, Davut Kenti'nde atalarının yanına gömüldü. Yerine oğlu Hizkiya kral oldu.
Ahaz ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi da su a Birnin Dawuda. Hezekiya ɗansa kuma ya gāje shi.

< 2 Krallar 16 >