< 1 Samuel 1 >

1 Efrayim dağlık bölgesindeki Ramatayim Kasabası'nda yaşayan, Efrayim oymağının Suf boyundan Yeroham oğlu Elihu oğlu Tohu oğlu Suf oğlu Elkana adında bir adam vardı.
Akwai wani mutum daga Ramatayim, mutumin Zuf daga ƙasar tuddan Efraim, sunansa Elkana, ɗan Yeroham, shi jikan Elihu ɗan Tohu, tattaɓa kunnen Zuf, mutumin Efraim.
2 Elkana'nın Hanna ve Peninna adında iki karısı vardı. Peninna'nın çocukları olduğu halde, Hanna'nın çocuğu olmuyordu.
Yana da mata biyu, ɗaya sunanta Hannatu, ɗayan kuwa ana kiranta Feninna. Ita Feninna tana da’ya’ya, amma Hannatu ba ta da’ya’ya.
3 Elkana Her Şeye Egemen RAB'be tapınıp kurban sunmak üzere her yıl kendi kentinden Şilo'ya giderdi. Eli'nin RAB'bin kâhinleri olan Hofni ve Pinehas adındaki iki oğlu da oradaydı.
Shekara-shekara wannan mutum yakan haura daga garinsa zuwa Shilo domin yin sujada da miƙa hadayu ga Ubangiji Maɗaukaki. A can kuwa’ya’yan Eli maza biyu, Hofni da Finehas su ne firistoci na Ubangiji.
4 Elkana kurban sunduğu gün karısı Peninna'ya ve oğullarıyla kızlarına etten birer pay verirken,
Duk sa’ad da rana ta kewayo don Elkana yă miƙa hadaya, yakan ba da kashin nama ga matarsa Feninna da dukan’ya’yanta maza da mata.
5 Hanna'ya iki pay verirdi. Çünkü RAB Hanna'nın rahmini kapamasına karşın, Elkana onu severdi.
Amma Hannatu kuwa sai yă ba ta babban rabo gama yana ƙaunarta ko da yake Ubangiji ya kulle mahaifarta.
6 Ama RAB Hanna'nın rahmini kapadığından, kuması Peninna Hanna'yı öfkelendirmek için ona sürekli sataşırdı.
Saboda Ubangiji ya kulle mahaifarta, sai kishiyarta ta dinga tsokanarta don tă ba ta haushi.
7 Bu yıllarca böyle sürdü. Hanna RAB'bin Tapınağı'na her gittiğinde kuması ona sataşırdı. Böylece Hanna ağlar, yemek yemezdi.
Wannan ya ci gaba shekara da shekaru. Duk lokacin da Hannatu ta haura zuwa haikalin Ubangiji, sai kishiyarta tă tsokane ta har tă yi ta kuka tă kuma ƙi cin abinci.
8 Kocası Elkana, “Hanna, neden ağlıyorsun, neden yemek yemiyorsun?” derdi, “Neden bu kadar üzgünsün? Ben senin için on oğuldan daha iyi değil miyim?”
Elkana mijinta kuwa yakan ce mata, “Hannatu don me kike kuka? Me ya sa ba za ki ci abinci ba? Don me kika karaya? Ashe, ban fi’ya’ya goma a gare ki ba?”
9 Bir gün onlar Şilo'da yiyip içtikten sonra, Hanna kalktı. Kâhin Eli RAB'bin Tapınağı'nın kapı sövesi yanındaki sandalyede oturuyordu.
Wata rana sa’ad da suka gama ci da sha a Shilo, Hannatu ta miƙe tsaye. Eli firist kuwa yana zaune a kujera a bakin ƙofar haikalin Ubangiji.
10 Hanna, gönlü buruk, acı acı ağlayarak RAB'be yakardı
A cikin baƙin ciki, Hannatu ta yi kuka mai zafi ta yi addu’a ga Ubangiji.
11 ve şu adağı adadı: “Ey Her Şeye Egemen RAB, kulunun üzüntüsüne gerçekten bakıp beni anımsar, kulunu unutmayıp bana bir erkek çocuk verirsen, yaşamı boyunca onu sana adayacağım. Onun başına hiç ustura değmeyecek.”
Ta yi ta cewa, “Ya Ubangiji Maɗaukaki. In har ka dubi baƙin cikin baiwarka, ka tuna da ni, ba ka kuma manta da baiwarka ba, amma ka ba ta ɗa, ni ma zan miƙa shi ga Ubangiji dukan rayuwarsa, aska kuwa ba za tă taɓa kansa ba.”
12 Hanna RAB'be yakarışını sürdürürken, Eli onun dudaklarını gözetliyordu.
Yayinda take addu’a ga Ubangiji, Eli ya lura da bakinta.
13 Hanna içinden yakarıyor, yalnız dudakları kımıldıyor, sesi duyulmuyordu. Bu yüzden Eli, Hanna'yı sarhoş sanarak,
Hannatu tana addu’a a zuci, ba a jin muryarta, sai leɓunanta ne kawai suna motsi. Eli kuwa ya yi tsammani ta bugu ne.
14 “Sarhoşluğunu ne zamana dek sürdüreceksin? Artık şarabı bırak” dedi.
Sai ya ce mata, “Har yaushe za ki ci gaba da maye? Ki daina shan ruwan inabi.”
15 Hanna, “Ah, öyle değil efendim!” diye yanıtladı, “Ben yüreği acılarla dolu bir kadınım. Ne şarap içtim, ne de başka bir içki. Sadece yüreğimi RAB'be döküyordum.
Hannatu ta ce, “Ba haka ba ne, ranka yă daɗe, ni mace ce da take cikin matsala ƙwarai da gaske. Ban sha ruwan inabi ba, ko wani abu mai sa maye, ina dai faɗa wa Ubangiji abin da yake damuna ne.
16 Kulunu kötü bir kadın sanma. Yakarışımı şimdiye dek sürdürmemin nedeni çok kaygılı, üzüntülü olmamdır.”
Kada ka yi zato baiwarka’yar iska ce. Ina addu’a a nan saboda yawan azaba da baƙin cikin da nake ciki.”
17 Eli, “Öyleyse esenlikle git” dedi, “İsrail'in Tanrısı dileğini yerine getirsin.”
Eli ya ce, “In haka ne, to, ki sauka lafiya, Allah na Isra’ila kuma yă ba ki abin da kika roƙa daga gare shi.”
18 Hanna, “Senin gözünde lütuf bulayım” deyip yoluna gitti. Sonra yemek yedi. Artık üzgün değildi.
Ta ce, bari baiwarka tă sami tagomashi a idonka. Sai ta yi tafiyarta ta je ta ci wani abu, fuskarta kuwa ba tă ƙara kasance da baƙin ciki ba.
19 Ertesi sabah erkenden kalkıp RAB'be tapındılar. Ondan sonra Rama'daki evlerine döndüler. Elkana karısı Hanna'yla birleşti ve RAB Hanna'yı anımsadı.
Kashegari da sassafe suka tashi suka yi sujada a gaban Ubangiji, sai suka koma garinsu a Rama. Elkana kuwa ya kwana da matarsa Hannatu, Ubangiji kuma ya tuna da ita.
20 Zamanı gelince Hanna gebe kaldı ve bir erkek çocuk doğurdu. “Onu RAB'den diledim” diyerek adını Samuel koydu.
Ana nan sai Hannatu ta yi ciki, ta kuma haifi ɗa. Ta ba shi suna Sama’ila; tana cewa, “Domin na roƙe shi daga wurin Ubangiji.”
21 Elkana RAB'be yıllık kurbanını ve adağını sunmak üzere ev halkıyla birlikte Şilo'ya gitti.
Da shekara ta kewayo, sai Elkana da iyalinsa suka sāke tafi Shilo domin su yi hadaya ga Ubangiji, yă kuma cika alkawarin da ya yi.
22 Ama Hanna gitmedi. Kocasına, “Çocuk sütten kesildikten sonra onu RAB'bin hizmetinde bulunmak üzere götüreceğim. Yaşamı boyunca orada kalacak” dedi.
Hannatu kuwa ba tă bi su ba. Ta gaya wa mijinta cewa, “Sai bayan na yaye yaron, zan kai shi in miƙa shi a gaban Ubangiji, yă kuma kasance a wurin koyaushe.”
23 Kocası Elkana, “Nasıl istersen öyle yap” diye karşılık verdi, “Çocuk sütten kesilinceye dek burada kal. RAB sözünü yerine getirsin.” Böylece Hanna oğlu sütten kesilinceye dek evde kalıp onu emzirdi.
Elkana mijinta ya ce mata, “Ki yi abin da kika ga ya fi miki kyau. Ki jira har sai bayan kin yaye shi. Ubangiji dai ya cika maganarsa.” Saboda haka matar ta tsaya a gida, ta yi ta renon ɗanta har ta yaye shi.
24 Küçük çocuk sütten kesildikten sonra Hanna üç yaşında bir boğa, bir efa un ve bir tulum şarap alarak onu kendisiyle birlikte RAB'bin Şilo'daki tapınağına götürdü.
Bayan ta yaye shi, sai ta ɗauki yaron tare da bijimi bana uku, da mudun gari, da salkan ruwan inabi, ta kawo su a gidan Ubangiji a Shilo.
25 Boğayı kestikten sonra çocuğu Eli'ye getirdiler.
Bayan an yanka bijimin, sai suka kawo yaron wurin Eli.
26 Hanna, “Ey efendim, yaşamın hakkı için derim ki, burada yanında durup RAB'be yakaran kadınım ben” dedi,
Sai ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ba ka gane ni ba? Ai, ni ce matar da ta taɓa tsayawa a gabanka, tana addu’a ga Ubangiji.
27 “Bu çocuk için yakarmıştım; RAB dileğimi yerine getirdi.
Wannan yaron ne na roƙa daga wurin Ubangiji, ya kuwa ba ni abin da na roƙa daga gare shi.
28 Ben de onu RAB'be adıyorum. Yaşamı boyunca RAB'be adanmış kalacaktır.” Sonra orada RAB'be tapındılar.
Saboda haka, na ba da shi ga Ubangiji muddin ransa, zai zama na Ubangiji.” A can kuwa ya yi wa Ubangiji sujada.

< 1 Samuel 1 >