< 1 Samuel 7 >
1 Bunun üzerine Kiryat-Yearim halkı varıp RAB'bin Sandığı'nı aldı. Onu Avinadav'ın tepedeki evine götürdüler. RAB'bin Antlaşma Sandığı'na bakması için Avinadav oğlu Elazar'ı görevlendirdiler.
Mutanen Kiriyat Yeyarim suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji. Suka kai a gidan Abinadab da ke kan tudu, suka keɓe Eleyazar ɗansa yă lura da akwatin alkawarin Ubangiji.
2 Sandık uzun bir süre, yirmi yıl boyunca Kiryat-Yearim'de kaldı. Bu arada bütün İsrail halkı RAB'bin özlemini çekti.
Akwatin Alkawarin ya daɗe a Kiriyat Yeyarim ya kai shekara ashirin cif. Sai dukan mutanen Isra’ila suka yi makoki suka nemi Ubangiji.
3 Samuel İsrail halkına şöyle dedi: “Eğer bütün yüreğinizle RAB'be dönmeye istekliyseniz, yabancı ilahları ve Aştoret'in putlarını aranızdan kaldırın. Kendinizi RAB'be adayıp yalnız O'na kulluk edin. RAB de sizi Filistliler'in elinden kurtaracaktır.”
Saboda haka Sama’ila ya yi magana da dukan gidan Isra’ila ya ce, in har da zuciya ɗaya kuke juyowa ga Ubangiji sai ku raba kanku da baƙin alloli da gunkin nan Ashtarot, ku ba da kanku ga Ubangiji. Ku yi masa bauta shi kaɗai, zai kuɓutar da ku daga hannun Filistiyawa.
4 Bunun üzerine İsrailliler Baal'ın ve Aştoret'in putlarını atıp yalnızca RAB'be kulluk etmeye başladılar.
Sai Isra’ilawa suka rabu da gumakan Ba’al da Ashtarot suka bauta wa Ubangiji kaɗai.
5 O zaman Samuel, “Bütün İsrail halkını Mispa'da toplayın, ben de sizin için RAB'be yakaracağım” dedi.
Sama’ila ya ce, “Ku tattara dukan Isra’ila a Mizfa, ni kuwa zan yi addu’a ga Ubangiji dominku.”
6 Mispa'da toplanan İsrailliler kuyudan su çekip RAB'bin önüne döktüler. O gün oruç tuttular ve, “RAB'be karşı günah işledik” dediler. Samuel Mispa'da İsrail halkına önderlik etti.
Sa’ad da suka taru a Mizfa, suka kawo ruwa suka zuba a gaban Ubangiji. A wannan rana suka yi azumi suka tuba, suka ce, “Mun yi wa Ubangiji zunubi!” Sama’ila kuwa ya zauna a Mizfa ya yi mulkin Isra’ilawa.
7 Filistliler İsrail halkının Mispa'da toplandığını duydular. Filist beyleri İsrailliler'e karşı savaşmaya çıktılar. İsrailliler bunu duyunca Filistliler'den korktular.
Da Filistiyawa suka ji cewa Isra’ila sun taru a Mizfa, sai shugabanninsu suka zo don su yaƙe Isra’ila. Da Isra’ilawa suka ji labarin, sai suka tsorata saboda Filistiyawa.
8 Samuel'e, “Bizi Filistliler'in elinden kurtarması için Tanrımız RAB'be yakarmayı bırakma” dediler.
Suka ce wa Sama’ila, “Kada ka fasa kai kukanmu ga Ubangiji Allahnmu saboda mu, don yă cece mu daga hannun Filistiyawa.”
9 Bunun üzerine Samuel bir süt kuzusu alıp RAB'be tümüyle yakmalık sunu olarak sundu ve İsrailliler adına RAB'be yakardı. RAB de ona karşılık verdi.
Sama’ila ya kama ɗan rago ya miƙa shi ɗungum hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji. Ya yi roƙo ga Ubangiji a madadin Isra’ila, Ubangiji kuwa ya amsa addu’arsa.
10 Samuel yakmalık sunuyu sunarken, Filistliler, İsrailliler'e saldırmak üzere yaklaşmışlardı. Ama RAB o an korkunç bir sesle gürleyerek Filistliler'i öyle şaşkına çevirdi ki, İsrailliler'in önünde bozguna uğradılar.
Lokacin da Sama’ila yana miƙa hadaya ta ƙonawa, Filistiyawa suka matso kusa don su yi yaƙi da Isra’ila. A ranar Ubangiji ya sa babban tsawa ya ruɗar da Filistiyawa har suka gudu a gaban Isra’ilawa.
11 Mispa'dan çıkan İsrailliler Filistliler'i Beytkar'ın altına kadar kovalayıp öldürdüler.
Isra’ilawa suka fito a guje daga Mizfa suka fafari Filistiyawa suka yi ta karkashe su a hanya har kwarin Bet-Kar.
12 Samuel bir taş alıp Mispa ile Şen arasına dikti. “RAB buraya kadar bize yardım etmiştir” diyerek taşa Even-Ezer adını verdi.
Sa’an nan Sama’ila ya ɗauki dutse ya kafa tsakanin Mizfa da Shen, ya sa masa suna, Ebenezer ma’ana, “Har zuwa wannan lokaci Ubangiji ya taimake mu.”
13 Yenilgiye uğrayan Filistliler bir daha İsrail topraklarına saldırmadılar. Samuel yaşadığı sürece RAB Filistliler'in saldırmasını engelledi.
Ta haka Isra’ilawa suka ci Filistiyawa. Daga ranan Filistiyawa ba su ƙara yin nasara a kan Isra’ila ba. Ubangiji ya yi gāba da Filistiyawa har ƙarshen zamanin Sama’ila.
14 Ekron'dan Gat'a kadar Filistliler'in ele geçirdiği kentler İsrail'e geri verildi. Bunun yanısıra İsrail'in sınır toprakları da Filistliler'in elinden kurtarıldı. İsrailliler'le Amorlular arasında ise barış vardı.
Filistiyawa suka mayar wa Isra’ila da garuruwan da suka ƙwato, wato, daga Ekron zuwa Gat, dukan yankin ƙasarsu da yake ƙarƙashin ikon Filistiyawa. Aka kuma sami zaman lafiya tsakanin Isra’ilawa da Amoriyawa.
15 Samuel yaşadığı sürece İsrail'e önderlik yaptı.
Sama’ila kuwa ya ci gaba da mulkin Isra’ila dukan rayuwarsa.
16 Her yıl gidip Beytel'i, Gilgal'ı, Mispa'yı dolaşır, bu kentlerden İsrail'i yönetirdi.
Shekara-shekara Sama’ila yakan fita rangadi zuwa Betel, da Gilgal da Mizfa inda yakan yi musu shari’a.
17 Sonra Rama'daki evine döner, İsrail'i oradan yönetirdi. Orada RAB'be bir sunak yaptı.
Amma yakan komo Rama inda gidansa yake, a nan yakan yi wa Isra’ila shari’a. A nan ne kuma ya gina wa Ubangiji bagade.