< 1 Samuel 19 >

1 Saul, oğlu Yonatan'a ve bütün görevlilerine Davut'u öldürmeleri için buyruk verdi. Ama Davut'u çok seven Yonatan ona, “Babam Saul seni öldürmek için fırsat kolluyor” diye haber verdi, “Lütfen yarın sabah dikkatli ol; gizlenebileceğin bir yere gidip saklan.
Shawulu ya gaya wa ɗansa Yonatan da ma’aikatansa su kashe Dawuda. Amma Yonatan yana son Dawuda sosai.
2
Sai ya gargaɗe shi ya ce, “Mahaifina Shawulu yana neman hanyar da zai kashe ka. Ka kula da kanka gobe da safe, ka tafi wani wuri ka ɓuya.
3 Ben de saklandığın tarlaya gidip babamın yanında duracağım ve onunla senin hakkında konuşacağım. Bir şey öğrenirsem, sana bildiririm.”
Zan je in tsaya da mahaifina a fili inda kake, zan yi masa magana game da kai. Zan kuma gaya maka abin da na ji.”
4 Yonatan babası Saul'a Davut'u överek şunları söyledi: “Kral kulu Davut'a haksızlık etmesin. Çünkü o sana hiç haksızlık etmedi ve yaptığı her şeyde sana büyük yararı dokundu.
Yonatan ya yi magana mai kyau a kan Dawuda a wajen mahaifinsa ya ce, “Kada sarki yă yi wani mummunan abu wa bawansa Dawuda, gama bai yi maka wani abu marar kyau ba. Abin da ya yi ya amfane ka ƙwarai da gaske.
5 Yaşamını tehlikeye atarak Filistli'yi öldürdü. RAB de bütün İsrail'i büyük bir zafere ulaştırdı. Sen de bunu görüp sevindin. Öyleyse neden Davut'u yok yere öldürerek suçsuz birine haksızlık edesin?”
Ya yi kasai da ransa sa’ad da ya kashe Bafilistin nan. Ubangiji ya ba wa dukan Isra’ila babban nasara, ka gani, ka kuma yi farin ciki. Don me za ka ci mutuncin amintaccen mutum kamar Dawuda ta wurin kashe shi ba tare da wani dalili ba?”
6 Saul Yonatan'ın söylediklerinden etkilenerek ant içti: “Yaşayan RAB'bin adıyla derim ki, Davut öldürülmeyecektir.”
Shawulu ya saurari Yonatan sai ya rantse ya ce, “Muddin Ubangiji yana a raye, ba za a kashe Dawuda ba.”
7 Bunun üzerine Yonatan Davut'u çağırıp ona her şeyi anlattı. Sonra Davut'u Saul'un yanına getirdi. Davut da önceden olduğu gibi kralın hizmetine girdi.
Ta haka Yonatan ya kira Dawuda ya gaya masa dukan maganarsu. Ya kawo shi wurin Shawulu, Dawuda kuwa ya zauna tare da Shawulu kamar dā.
8 Savaş yine patlak verdi. Davut gidip Filistliler'e karşı savaştı. Onları öyle büyük bir bozguna uğrattı ki, önünden kaçtılar.
Wani yaƙi ya sāke tashi, Dawuda kuwa ya fita ya yaƙi Filistiyawa, ya kai musu hari mai tsanani, sai da suka gudu a gabansa.
9 Bir gün Saul, mızrağı elinde evinde oturuyor, Davut da lir çalıyordu. Derken RAB'bin gönderdiği kötü bir ruh Saul'u yakaladı.
Amma mugun ruhu daga Ubangiji ya sauko wa Shawulu yayinda yana zaune a cikin gidansa da māshi a hannunsa. Yayinda Dawuda yake bugan molo,
10 Saul mızrağıyla Davut'u duvara çakmaya çalıştı. Ancak Davut yana kaçınca Saul'un mızrağı duvara saplandı. O gece Davut kaçıp kurtuldu.
Shawulu ya yi ƙoƙari yă kafe shi da bango da māshinsa, amma Dawuda ya goce sa’ad da Shawulu jefa māshin a bango. A daren nan Dawuda ya nemi hanya ya gudu.
11 Saul, Davut'u gözetlemeleri, ertesi sabah da öldürmeleri için evine ulaklar gönderdi. Ama karısı Mikal Davut'a, “Bu gece kaçıp kurtulamazsan, yarın öldürüleceksin” dedi.
Shawulu ya aiki mutane zuwa gidan Dawuda su yi gadin gidan, su kuma kashe Dawuda. Amma Mikal matar Dawuda ta gargaɗe Dawuda, ta ce, “In ba ka gudu a daren nan ba, kashegari za a kashe ka.”
12 Sonra Davut'u pencereden aşağıya indirdi. Böylece Davut kaçıp kurtuldu.
Haka kuwa Mikal ta sauko da Dawuda ta taga ya gudu, ya tsere.
13 Mikal aile putunu alıp yatağa koydu, üstüne yorganı örttü, baş tarafına da keçi kılından bir yastık yerleştirdi.
Sai Mikal ta ɗauki gunki ta kwantar da shi a gādo, ta sa masa gashin akuya a kansa, sai ta rufe da mayafi.
14 Saul'un gönderdiği ulaklar Davut'u yakalamaya geldiğinde, Mikal, “Davut hasta” dedi.
Da Shawulu ya aiki mutane su kama Dawuda. Mikal ta ce, “Ba shi da lafiya.”
15 Saul Davut'u görmeleri için ulakları yeniden göndererek, “Onu yatağıyla buraya getirin de öldüreyim” diye buyurdu.
Sai Shawulu ya sāke aiki mutanen su ga Dawuda, ya ce musu, “Ku kawo shi a gādonsa domin in kashe shi.”
16 Ulaklar eve girince, yatakta başında keçi kılından yastık olan putu gördüler.
Amma da mutanen suka shiga sai suka ga gunkin a gadon, a wajen kan kuwa akwai gashin akuya.
17 Saul Mikal'a “Neden beni böyle kandırıp düşmanımın kaçmasını sağladın?” diye sordu. Mikal, “Davut bana, ‘Bırak beni gideyim, yoksa seni öldürürüm’ dedi” diye yanıtladı.
Shawulu ya ce wa Mikal, “Don me kika ruɗe ni har kika bar maƙiyina ya gudu ya tsere?” Mikal ta ce masa, “Ya ce mini, ‘Idan ban bar shi ya tafi ba, zai kashe ni?’”
18 Kaçıp kurtulan Davut, Rama'da yaşayan Samuel'in yanına gitti. Saul'un kendisine bütün yaptıklarını ona anlattı. Sonra Samuel'le birlikte Nayot Mahallesi'ne gidip orada kaldı.
Da Dawuda ya gudu ya tsere, sai ya tafi wurin Sama’ila a Rama ya gaya masa dukan abin da Shawulu ya yi masa. Da shi da Sama’ila suka tafi Nayiwot suka zauna a can.
19 Davut'un Rama'nın Nayot Mahallesi'nde olduğu haberi Saul'a ulaştırıldı.
Shawulu ya sami labari cewa, “Dawuda yana Nayiwot a Rama.”
20 Bunun üzerine Saul Davut'u yakalamaları için ulaklarını oraya gönderdi. Ulaklar Samuel'in önderliğinde bir peygamber topluluğunun oynayıp coştuğunu gördüler. İşte o zaman Tanrı'nın Ruhu Saul'un ulaklarının üzerine indi. Onlar da oynayıp coşmaya başladılar.
Sai ya aiki mutane su je su kamo Dawuda, amma da suka ga ƙungiyar annabawa suna annabci tare da Sama’ila shugabansu a tsaye, sai Ruhun Allah ya sauko wa mutanen Shawulu, su ma suka fara yin annabci.
21 Saul olup bitenleri duyunca, başka ulaklar gönderdi. Onlar da oynayıp coştular. Saul'un üçüncü kez gönderdiği ulaklar da öncekiler gibi yaptı.
Shawulu ya sami labari game da wannan, sai ya sāke aiken waɗansu da yawa. Su ma suka shiga yin annabci. Shawulu ya sāke aiken mutane sau na uku, su kuma suka shiga yin annabci.
22 Sonunda Saul kendisi Rama'ya doğru yola çıktı. Seku'daki büyük sarnıca varınca, “Samuel'le Davut neredeler?” diye sordu. Biri, “Rama'nın Nayot Mahallesi'nde” dedi.
A ƙarshe, shi da kansa ya tashi ya tafi Rama. Ya bi ta babban rijiyar ruwan Seku. A can ya yi tambaya ya ce, “Ina Sama’ila da Dawuda suke?” Suka ce, “Suna cikin Nayiwot a Rama.”
23 Saul Rama'daki Nayot'a doğru ilerlerken, Tanrı'nın Ruhu onun üzerine de indi. Nayot'a varıncaya dek yol boyunca oynayıp coştu.
Saboda haka Shawulu ya tafi Nayiwot a Rama, amma Ruhun Allah ya sauko masa, shi ma ya yi tafiya yana annabci har sai da ya isa Nayiwot.
24 Giysilerini de çıkarıp Samuel'in önünde oynayıp coştu. Bütün gün ve gece çıplak yattı. Halkın, “Saul da mı peygamber oldu?” demesi bundandır.
Ya tuttuɓe rigunarsa, ya kuma yi annabci a gaban Sama’ila. Ya kwanta tsirara dukan yini da dukan dare. Abin da ya sa ke nan mutane suke cewa, “Shawulu ma yana cikin annabawa ne?”

< 1 Samuel 19 >