< 1 Samuel 12 >
1 Bundan sonra Samuel İsrail halkına şöyle dedi: “Bana söylediğiniz her şeye kulak verdim: Size bir kral atadım.
Sama’ila ya ce wa Isra’ilawa duka, “Na saurari abubuwan da kuka faɗa mini, na kuma naɗa muku sarki.
2 Şimdi size önderlik yapan bir kralınız var. Bense yaşlandım, saçım ağardı. Oğullarım da sizlerle birlikte. Gençliğimden bu güne dek size önderlik yaptım.
Yanzu kuna da sarki a matsayin shugaba, ni kuwa na tsufa har da furfura, yarana maza kuma suna tare da ku. Na yi shugabancinku tun ina yaro.
3 İşte karşınızda duruyorum. Hanginizin öküzünü aldım? Kimin eşeğine el koydum? Kimi dolandırdım? Kime baskı yaptım? Göz yummak için kimden rüşvet aldım? RAB'bin ve O'nun meshettiğinin önünde bana karşı tanıklık edin de size karşılığını vereyim.”
Ga ni a gabanku. Idan na yi wani abin da ba daidai ba sai ku faɗa a gaban Ubangiji, da gaban sarkin da ya keɓe. Ko na taɓa ƙwace saniya ko jakin wani? Ko na taɓa cuce wani, ko in danne hakkinsa? Ko na taɓa cin hanci daga hannun ɗayanku? Idan na taɓa yi ɗaya daga cikin waɗannan, sai ku faɗa mini, zan kuwa mayar masa.”
4 Halk, “Bizi dolandırmadın” diye karşılık verdi, “Bize baskı da yapmadın. Kimsenin elinden hiçbir şey almadın.”
Suka ce, “Ba ka cuci ko danne hakkin kowa ba, ba ka ƙwace kome daga hannun kowa ba.”
5 Samuel, “Bana karşı bir şey bulamadığınıza bugün hem RAB, hem de O'nun meshettiği kral tanıktır” dedi. “Evet, tanıktır” dediler.
Sama’ila ya ce musu, “Ubangiji yă zama shaida a kanku, shafaffensa kuma yă zama shaida a wannan rana cewa ba ku same ni da wani laifin kome ba.” Suka ce, “I, shi ne shaida.”
6 Samuel konuşmasını şöyle sürdürdü: “Musa ile Harun'u görevlendiren, atalarınızı Mısır'dan çıkaran RAB'dir.
Sa’an nan Sama’ila ya ce wa mutane, Ubangiji ne ya naɗa Musa da Haruna suka fitar da kakanninku daga Masar.
7 Şimdi burada durun, RAB'bin önünde, O'nun sizi ve atalarınızı tekrar tekrar nasıl kurtardığına dair kanıtlar göstereyim size.
Yanzu ku tsaya nan zan yi fito-na-fito da ku da shaida a gaban Ubangiji kan dukan ayyuka masu alherin da Ubangiji ya aikata saboda ku da kakanninku.
8 “Yakup Mısır'a gittikten sonra, atalarınız RAB'be yakardı. O da atalarınızı Mısır'dan çıkarıp burada yerleşmelerini sağlayan Musa ile Harun'u gönderdi.
Bayan da Yaƙub da’ya’yansa suka shiga Masar suka yi kukan neman taimako daga Ubangiji, Ubangiji kuwa ya aika musu da Musa da Haruna. Su ne suka kawo kakanni-kakanninku daga Masar suka zauna a nan.
9 Ama atalarınız Tanrıları RAB'bi unuttular. Bu yüzden RAB onları Hasor ordusunun komutanı Sisera'nın, Filistliler'in ve Moav Kralı'nın eline teslim etti. Bunlar atalarınıza karşı savaştılar.
Amma suka manta da Ubangiji Allahnsu, shi kuma ya bashe su a hannun Sisera shugaban rundunar Hazor da kuma hannun Filistiyawa da sarkin Mowab wanda suka yi yaƙi da su.
10 Atalarınız RAB'be, ‘Günah işledik; RAB'bi bırakıp Baal'ın ve Aştoret'in putlarına kulluk ettik. Ama şimdi bizi düşmanlarımızın elinden kurtar, sana kulluk edeceğiz’ diye seslendiler.
Suka yi kuka a gaban Ubangiji suka ce, “Mun yi zunubi mun bar Ubangiji, muka bauta wa Ba’al da Ashtarot. Amma ka cece mu yanzu daga hannun abokan gābanmu, mu kuwa za mu bauta maka.”
11 RAB de Yerubbaal'ı, Bedan'ı, Yiftah'ı ve ben Samuel'i gönderdi. Güvenlik içinde yaşamanız için sizi saran düşmanlarınızın elinden kurtardı.
Sai Ubangiji ya aiki Yerub-Ba’al da Bedan da Yefta da Sama’ila, ya cece ku daga hannun abokan gābanku a kowane gefe domin ku sami cikakken zaman lafiya.
12 “Ama siz Ammon Kralı Nahaş'ın üzerinize yürüdüğünü görünce, Tanrınız RAB kralınız olduğu halde bana, ‘Hayır, bize bir kral önderlik yapacak’ dediniz.
Amma da kuka ga Nahash sarkin Ammonawa yana matsowa yă yaƙe, sai kuka ce mini, “Sam, muna so sarki yă shugabance mu.” Ko da yake Ubangiji Allahnku ne yake mulkinku.
13 İşte seçtiğiniz, dilediğiniz kral! Evet, RAB size bir kral verdi.
Yanzu ga sarkinku da kuka zaɓa wanda kuka nema, ga shi Ubangiji ya naɗa muku sarki.
14 Eğer RAB'den korkar, O'na kulluk ederseniz, O'nun sözünü dinleyip buyruklarına karşı gelmezseniz, hem siz hem de önderiniz olacak kral Tanrınız RAB'bin ardınca giderseniz, ne âlâ!
In kuka ji tsoron Ubangiji, kuka bauta masa, kuka yi masa biyayya, ba ku kuwa ƙi bin umarninsa ba, in kuma ku da sarkin da yake mulkinku kun bi Ubangiji Allahnku, to, za ku zauna lafiya.
15 Ama RAB'bin sözünü dinlemez, buyruklarına karşı gelirseniz, RAB kralınızı cezalandırdığı gibi sizi de cezalandıracaktır.
Amma in ba ku yi biyayya ga Ubangiji ba, in kuma kuka ƙi bin umarnansa, fushinsa zai zauna a kanku.
16 “Şimdi olduğunuz yerde durun ve RAB'bin gözlerinizin önünde yapacağı şu olağanüstü olayı görün.
Yanzu ku tsaya tsit ku ga abin da Ubangiji ke dab da yi a gabanku.
17 Bugün buğday biçme zamanı değil mi? Göğü gürletsin, yağmur yağdırsın diye RAB'be yalvaracağım. Böylece bir kral istemekle yaptığınız kötülüğün RAB'bin gözünde ne denli büyük olduğunu iyice anlayacaksınız.”
Ba lokacin yankan alkama ke nan ba? Zan roƙi Ubangiji yă aiko da tsawa da ruwan sama, za ku kuwa gane wace irin mugunta kuka yi a gaban Ubangiji sa’ad da kuka roƙa a ba ku sarki.
18 Samuel RAB'be yalvardı ve RAB o gün göğü gürletti, yağmur yağdırdı. Halk RAB'den de Samuel'den de çok korktu.
Sai Sama’ila ya roƙi Ubangiji, a ranar kuwa Ubangiji ya aiko da tsawa da ruwan sama. Dukan mutane suka ji tsoron Ubangiji da kuma Sama’ila.
19 Bunun üzerine Samuel'e, “Yok olmayalım diye, biz kulların için Tanrın RAB'be yakar” dediler, “Çünkü bütün günahlarımıza kendimize bir kral istemek kötülüğünü de ekledik.”
Dukan mutane suka ce wa Sama’ila, “Ka yi addu’a ga Ubangiji Allahnka saboda bayinka, domin kada mu mutu, gama mun ƙara wa kanmu zunubi da muka roƙa a yi mana sarki.”
20 Samuel halka, “Korkmayın” dedi, “Siz bu büyük kötülüğü yaptınız, ama yine de RAB'bin ardınca gitmekten vazgeçmeyin; tersine, bütün yüreğinizle RAB'be kulluk edin.
Sama’ila ya ce, “Kada ku ji tsoro.” Kun yi waɗannan mugunta duk da haka kada ku bar bin Ubangiji, amma ku bauta wa Ubangiji da dukan zuciyarku.
21 Kimseyi kurtaramayan yararsız putların ardınca gitmeyin; çünkü onlar değersizdir.
Kada ku bi alloli marasa amfani. Ba za su iya yi muku kome nagari ba, ba kuwa za su iya cece ku ba, gama ba su da amfani.
22 RAB görkemli adının hatırına halkını bırakmayacak. Çünkü sizi kendi halkı kılmaktan hoşnut kaldı.
Saboda suna mai girma da Ubangiji yake da shi, ba zai taɓa ƙin mutanensa ba. Gama Ubangiji ya ji daɗi da ya yi ku mutanensa.
23 Bana gelince, sizin için RAB'be yalvarmaktan vazgeçip O'na karşı günah işlemek benden uzak olsun! Ancak size iyi ve doğru yolu öğreteceğim.
Ni kam ba zai taɓa yiwu in yi wa Ubangiji zunubi ta wurin ƙin yin addu’a dominku ba. Zan koya muku hanyar da tana da kyau da ta kuma cancanta.
24 Yalnız RAB'den korkun, O'na bağlılıkla ve bütün yüreğinizle kulluk edin. O'nun sizler için ne görkemli işler yaptığını bir düşünün!
Amma ku amince za ku ji tsoron Ubangiji, ku bauta masa da aniya da dukan zuciyarku, kuna da manyan abubuwan da ya yi muku.
25 Ama kötülük yapmayı sürdürürseniz, hem siz yok olacaksınız, hem de kralınız.”
Amma in kuka duƙufa cikin aikin mugunta da ku da sarkinku za a hallaka ku.