< 1 Tarihler 29 >
1 Kral Davut bütün topluluğa şöyle dedi: “Tanrı'nın seçtiği oğlum Süleyman genç ve deneyimsizdir. İş büyüktür. Çünkü bu tapınak insan için değil, RAB Tanrı içindir.
Sa’an nan Sarki Dawuda ya ce wa dukan taron, “Ɗana Solomon, wanda Allah ya zaɓa, matashi ne, kuma bai gogu ba. Aikin yana da yawa, domin wannan ƙasaitaccen ginin ba na mutum ba ne, na Ubangiji Allah ne.
2 Tanrım'ın Tapınağı'na gereç sağlamak için var gücümle çalıştım. Altın eşyalar için altın, gümüş için gümüş, tunç için tunç, demir için demir, ahşap için ağaç sağladım. Ayrıca oniks, kakma taşlar, süs taşları, çeşitli renklerde değerli taşlar ve çok miktarda mermer sağladım.
Na riga na tara dukan kayayyakin da na tanada saboda haikalin Allahna, zinariya saboda dukan ayyukan zinariya, azurfa saboda ayyukan azurfa, tagulla saboda ayyukan tagulla, ƙarfe saboda ayyukan ƙarfe da kuma katako saboda ayyukan katako, da onis don ado, turkuwoyis, duwatsu masu launi dabam-dabam, da kuma dukan duwatsu masu kyau da mabul, dukan waɗannan suna nan jingim.
3 Bu kutsal tapınak için sağladıklarımın yanısıra, Tanrım'ın Tapınağı'na sevgim yüzünden, kişisel servetimden de altın ve gümüş de veriyorum:
Ban da haka ma, cikin sa zuciyata ga haikalin Allahna, yanzu na ba da ma’ajina na zinariya da azurfa saboda haikalin Allahna, fiye da kome na tanada saboda wannan haikali,
4 Üç bin talant Ofir altını ve tapınağın duvarlarını kaplamak için yedi bin talant kaliteli gümüş.
talenti dubu uku na zinariya (zinariyar Ofir) da tacecciyar azurfa dubu bakwai; don adon bangon gine-ginen,
5 Bunları altın, gümüş gerektiren işlerde ve sanatkârların el işçiliğinde kullanılmak üzere veriyorum. Kim bugün kendini RAB'be adamak istiyor?”
don aikin zinariya da kuma aikin azurfa, don kuma dukan aikin da gwanaye za su yi. Yanzu fa wa yake da niyya yă miƙa kansa a yau don Ubangiji?”
6 Bunun üzerine boy başları, İsrail'in oymak önderleri, binbaşılar, yüzbaşılar ve saray yöneticileri gönülden armağanlar verdiler.
Sai shugabannin iyalai, shugabannin kabilan Isra’ila, manyan hafsoshin mayaƙa dubu-dubu da manyan hafsoshi mayaƙa ɗari-ɗari, da shugabannin lura da ayyukan sarki suka yi bayarwa da yardar rai.
7 Tanrı'nın Tapınağı'nın yapımı için beş bin talant, on bin darik altın, on bin talant gümüş, on sekiz bin talant tunç, yüz bin talant demir bağışladılar.
Suka bayar talenti dubu biyar na zinariya, talenti dubu goma na azurfa, talenti dubu goma sha takwas na tagulla da talenti dubu ɗari na ƙarfe don aiki a haikalin Allah.
8 Değerli taşları olanlar, Gerşonlu Yehiel'in denetiminde, bunları RAB'bin Tapınağı'nın hazinesine verdi.
Duk waɗanda suke da duwatsu masu daraja suka ba da su ga Yehiyel mutumin Gershon ma’ajin haikalin Ubangiji.
9 Halk verdiği armağanlar için seviniyordu. Çünkü herkes RAB'be içtenlikle ve gönülden vermişti. Kral Davut da çok sevinçliydi.
Mutane suka yi farin ciki ganin yadda shugabanninsu suke bayarwa da yardar rai, gama sun bayar hannu sake da kuma dukan zuciya ga Ubangiji. Dawuda sarki shi ma ya yi farin ciki ƙwarai.
10 Davut bütün topluluğun gözü önünde RAB'bi övdü. Şöyle dedi: “Ey atamız İsrail'in Tanrısı RAB, Sonsuzluk boyunca sana övgüler olsun!
Dawuda ya yabi Ubangiji a gaban dukan taron, yana cewa, “Yabo gare ka, ya Ubangiji, Allah na mahaifinmu Isra’ila, har abada abadin.
11 Ya RAB, büyüklük, güç, yücelik, Zafer ve görkem senindir. Gökte ve yerde olan her şey senindir. Egemenlik senindir, ya RAB! Sen her şeyden yücesin.
Girma da iko da ɗaukaka, da daraja da kuma nasara naka ne, ya Ubangiji, gama kome a sama da ƙasa naka ne. Mulki kuma naka ne, ya Ubangiji; an kuma ɗaukaka ka a matsayin kai a bisa duka.
12 Zenginlik ve onur senden gelir. Her şeye egemensin. Güç ve yetki senin elindedir. Birini yükseltmek ve güçlendirmek Senin elindedir.
Wadata da girma daga gare ka suke; kai ne mai mulkin dukan abubuwa. A hannuwanka ne ƙarfi da iko suke don ka ɗaukaka da kuma ba da ƙarfi ga duka.
13 Şimdi, ey Tanrımız, sana şükrederiz, Görkemli adını överiz.
Yanzu fa, Allahnmu, muna gode maka, muna kuma yabon ɗaukakar sunanka.
14 “Ama ben kimim, halkım kim ki, böyle gönülden armağanlar verebilelim? Her şey sendendir. Biz ancak senin elinden aldıklarımızı sana verdik.
“Amma wane ni, kuma wace ce jama’ata da za mu iya ba ka a yalwace kamar haka? Kome daga gare ka suka fito, kuma mun ba ka abin da kawai ya fito daga hannunka ne.
15 Senin önünde garibiz, yabancıyız atalarımız gibi. Yeryüzündeki günlerimiz bir gölge gibidir, kalıcı değildir.
Mu bare ne kuma baƙi a gabanka, kamar yadda dukan kakanninmu suke. Kwanakinmu a duniya suna kamar inuwa ne, ba sa zuciya.
16 Ya RAB Tanrımız, kutsal adına bir tapınak yapmak için sağladığımız bu büyük servet senin elindendir, hepsi senindir.
Ya Ubangiji Allahnmu, game da dukan wannan yalwar da ka tanada saboda ginin haikali saboda Sunanka Mai Tsarki, sun fito daga hannunka ne, kuma dukan naka ne.
17 Yüreği sınadığını, doğruluktan hoşlandığını bilirim. Her şeyi içtenlikle, gönülden verdim. Şimdi burada olan halkının sana nasıl istekle bağışlar verdiğini sevinçle gördüm.
Na sani, Allahna, cewa kakan gwada zuciya, kakan kuma gamsu da mutunci. Dukan waɗannan abubuwa na bayar da yardar rai da kuma kyakkyawar niyya. Yanzu kuma da farin ciki na ga yadda mutanenka waɗanda suke a nan da yardar rai suka ba ka.
18 Ya RAB, atalarımız İbrahim'in, İshak'ın, İsrail'in Tanrısı, bu isteği sonsuza dek halkının yüreğinde ve düşüncesinde tut, onların sana bağlı kalmalarını sağla.
Ya Ubangiji Allah na kakanninmu Ibrahim, Ishaku da Isra’ila, ka sa wannan sha’awa a cikin zukatan mutanenka har abada, ka kuma bar zukatansu su yi maka biyayya.
19 Oğlum Süleyman'a bütün buyruklarına, uyarılarına, kurallarına uymak, hazırlığını yaptığım tapınağı kurmak için istekli bir yürek ver.”
Ka kuma ba ɗana Solomon cikakkiyar zuciya don yă kiyaye umarnanka, farillanka da ƙa’idodinka yă kuma yi kome don yă gina ƙasaitaccen gini wanda na riga na yi tanadi dominsa.”
20 Sonra Davut bütün topluluğa, “Tanrınız RAB'bi övün!” dedi. Böylece hepsi atalarının Tanrısı RAB'bi övdü; Tanrı'nın ve kralın önünde başlarını eğip yere kapandı.
Sa’an nan Dawuda ya ce wa dukan taron, “Ku yabi Ubangiji Allahnku.” Saboda haka suka yabi Ubangiji Allah na kakanninsu; suka rusuna suka kuma fāɗi rubda ciki a gaban Ubangiji da kuma sarki.
21 Ertesi gün halk RAB'be kurbanlar kesip yakmalık sunular sundu: Bin boğa, bin koç, bin kuzunun yanısıra, bütün İsrailliler için dökmelik sunular ve birçok başka kurban.
Kashegari suka miƙa hadayu ga Ubangiji suka kuma miƙa hadayu bijimai dubu, raguna dubu da kuma’yan raguna dubu na ƙonawa gare shi, tare da hadayunsu na sha da sauran hadayu a yalwace saboda dukan Isra’ila.
22 O gün İsrailliler büyük bir sevinçle RAB'bin önünde yiyip içtiler. Bundan sonra Davut oğlu Süleyman'ı ikinci kez kral olarak onayladılar. Süleyman'ı RAB'bin önünde önder, Sadok'u da kâhin olarak meshettiler.
Suka ci suka sha da farin ciki mai girma a gaban Ubangiji a wannan rana. Sa’an nan suka yarda da Solomon ɗan Dawuda a matsayin sarki sau na biyu, suka shafe shi a gaban Ubangiji don yă zama mai mulki, Zadok kuwa ya zama firist.
23 Böylece Süleyman babası Davut'un yerine RAB'bin tahtına oturdu. Başarılı oldu. Bütün İsrail halkı onun sözüne uydu.
Saboda haka Solomon ya zauna a kujerar sarautar Ubangiji a matsayin sarki a maimakon mahaifinsa Dawuda. Ya yi nasara, dukan Isra’ila kuwa suka yi masa biyayya.
24 Yöneticilerin, güçlü kişilerin ve Davut'un oğullarının tümü Kral Süleyman'a bağlı kalacaklarına söz verdiler.
Dukan shugabanni da jarumawa, har ma da dukan’ya’yan Sarki Dawuda maza, suka yi alkawari za su yi wa Sarki Solomon biyayya.
25 RAB bütün İsrailliler'in gözünde Süleyman'ı çok yükseltti ve daha önce İsrail'de hiçbir kralın erişemediği bir krallık görkemiyle donattı.
Ubangiji ya ɗaukaka Solomon sosai a idon dukan Isra’ila, ya kuma ba shi darajar sarauta yadda babu sarki a Isra’ilan da ya taɓa samu.
26 İşay oğlu Davut bütün İsrail'de krallık yaptı.
Dawuda ɗan Yesse ya zama sarki a bisa dukan Isra’ila.
27 Yedi yıl Hevron'da, otuz üç yıl Yeruşalim'de olmak üzere toplam kırk yıl İsrail'de krallık yaptı.
Ya yi mulki a bisa Isra’ila shekaru arba’in, shekaru bakwai a Hebron da kuma shekaru talatin da uku a Urushalima.
28 Güzel bir yaşlılık döneminde öldü. Zenginlik ve onur dolu günler yaşadı. Yerine oğlu Süleyman kral oldu.
Ya mutu a kyakkyawar tsufa, bayan ya more dogon rai, wadata da girma. Ɗansa Solomon ya gāje shi a matsayin sarki.
29 Kral Davut'un krallığı dönemindeki öteki olaylar, başından sonuna dek Bilici Samuel'in, Peygamber Natan'ın, Bilici Gad'ın tarihinde yazılıdır.
Game da ayyukan mulkin Sarki Dawuda, daga farko har ƙarshe, an rubuta su a cikin tarihin Sama’ila mai duba, tarihin annabi Natan da kuma tarihin Gad mai duba,
30 Krallığı dönemindeki bütün ayrıntılar, ne denli güçlü olduğu, başından geçen olaylar, İsrail'de ve çevredeki ülkelerde olup bitenler bu tarihte yazılıdır.
tare da yadda mulkinsa da ikonsa da yanayin da suka kewaye shi da Isra’ila da kuma dukan masarautai na dukan sauran ƙasashe.