< 1 Tarihler 21 >

1 Şeytan İsrailliler'e karşı çıkıp İsrail'de sayım yapması için Davut'u kışkırttı.
Sai Shaiɗan ya tashi gāba da Isra’ila, ya zuga Dawuda ya ƙidaya Isra’ila.
2 Davut Yoav'la halkın önderlerine, “Gidin, Beer-Şeva'dan Dan'a dek İsrailliler'i sayın” dedi, “Sonra bana bilgi verin ki, halkın sayısını bileyim.”
Saboda haka Dawuda ya ce wa Yowab da shugabannin mayaƙa, “Ku tafi ku ƙidaya Isra’ilawa daga Beyersheba zuwa Dan. Ku kawo mini labarin saboda in san su nawa ne.”
3 Ama Yoav, “RAB halkını yüz kat daha çoğaltsın” diye karşılık verdi, “Ey efendim kral, bunlar hepsi senin kulların değil mi? Efendim neden bunu istiyor? Neden İsrail'i suça sürüklüyor?”
Amma Yowab ya amsa ya ce, “Ubangiji ya riɓaɓɓanya mayaƙansa fiye da sau ɗari. Ranka yă daɗe sarki, dukansu ba bayin shugabana ba ne? Me ya sa ranka yă daɗe yake so yă yi haka? Me zai sa ka kawo laifi a kan Isra’ila?”
4 Gelgelelim kralın sözü Yoav'ın sözünden baskın çıktı. Böylece Yoav kralın yanından ayrılıp İsrail'in her yanını dolaşmaya gitti. Sonra Yeruşalim'e dönerek
Amma sarki ya nace a kan maganar da ya yi wa Yowab. Sai Yowab ya tashi ya tafi cikin dukan Isra’ila, ya kewaye sa’an nan ya dawo Urushalima.
5 sayımın sonucunu Davut'a bildirdi: İsrail'de kılıç kuşanabilen bir milyon yüz bin, Yahuda'daysa dört yüz yetmiş bin kişi vardı.
Yowab ya ba labarin yawan mayaƙan wa Dawuda. A cikin Isra’ila akwai mutum miliyon da dubu ɗari ɗaya waɗanda za su iya riƙe takobi, haɗe da dubu ɗari huɗu da saba’in a Yahuda.
6 Yoav Levililer'le Benyaminliler'i saymadı; çünkü kralın bu konudaki buyruğunu benimsememişti.
Amma Yowab bai haɗa da mutanen Lawi da na Benyamin a ƙidayar ba, domin bai ji daɗin umarnin sarki ba.
7 Tanrı da yapılanı uygun görmedi ve bu yüzden İsrailliler'i cezalandırdı.
Wannan umarnin mugu ne a gaban Allah; saboda haka ya hukunta Isra’ila.
8 Davut Tanrı'ya, “Bunu yapmakla büyük günah işledim!” dedi, “Lütfen kulunun suçunu bağışla. Çünkü çok akılsızca davrandım.”
Sai Dawuda ya ce wa Allah, “Na yi zunubi ƙwarai ta wurin yin wannan. Yanzu, na roƙe ka, ka ɗauke laifin bawanka. Na yi wauta sosai.”
9 RAB Davut'un bilicisi Gad'a şöyle dedi:
Sai Ubangiji ya ce wa Gad, mai duba na Dawuda,
10 “Gidip Davut'a de ki, ‘RAB şöyle diyor: Önüne üç seçenek koyuyorum. Bunlardan birini seç de sana onu yapayım.’”
“Tafi ka faɗa wa Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ina ba ka abubuwa uku. Ka zaɓi ɗaya daga cikinsu don in aikata a kanka.’”
11 Gad Davut'a gidip şöyle dedi: “RAB diyor ki, ‘Hangisini istiyorsun?
Saboda haka Gad ya tafi wurin Dawuda ya ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka yi zaɓi,
12 Üç yıl kıtlık mı? Yoksa kılıçla seni kovalayan düşmanlarının önünde üç ay kaçıp yok olmak mı? Ya da RAB'bin kılıcının ve RAB'bin meleğinin bütün İsrail ülkesine üç gün salgın hastalık salmasını mı?’ Beni gönderene ne yanıt vereyim, şimdi iyice düşün.”
shekara uku na yunwa, wata uku na shan ɗibga a gaban abokan gābanka, sa’ad da za su bi suna kakkashe ku, ko kuwa kwana uku na takobin Ubangiji, ranakun annoba a cikin ƙasar, mala’ikan Ubangiji zai hallaka kowane sashe na Isra’ila.’ Yanzu sai ka yanke shawara yadda zan amsa wa wanda ya aiko ni.”
13 Davut, “Sıkıntım büyük” diye yanıtladı, “İnsan eline düşmektense, RAB'bin eline düşeyim. Çünkü O'nun acıması çok büyüktür.”
Dawuda ya ce wa Gad, “Na shiga uku. Bari in fāɗa a hannuwan Ubangiji, gama jinƙansa yana da girma sosai; amma kada ka bari in fāɗa a hannuwan mutane.”
14 Bunun üzerine RAB İsrail ülkesine salgın hastalık gönderdi. Yetmiş bin İsrailli öldü.
Sai Ubangiji ya aiko da annoba a kan Isra’ila, mutane duba saba’in na Isra’ila suka mutu.
15 Tanrı Yeruşalim'i yok etmek için bir melek gönderdi. Ama melek yıkıma başlayacağı sırada RAB onu gördü. Göndereceği yıkımdan vazgeçerek halkı yok eden meleğe, “Yeter artık! Elini çek” dedi. RAB'bin meleği Yevuslu Ornan'ın harman yerinde duruyordu.
Allah kuwa ya aiki mala’ika yă hallaka Urushalima. Amma yayinda mala’ikan yana gab da yin haka, sai Ubangiji ya gani ya kuma yi nadama saboda masifar, sai ya ce wa mala’ikan wanda yake hallaka mutane, “Ya isa! Janye hannunka.” Mala’ikan Ubangiji kuwa yana tsaye a masussukar Ornan mutumin Yebus.
16 Davut başını kaldırıp baktı. Elinde yalın bir kılıç olan RAB'bin meleğini gördü. Melek elini Yeruşalim'in üzerine uzatmış, yerle gök arasında duruyordu. Çula sarınmış Davut'la halkın ileri gelenleri yüzüstü yere kapandılar.
Sai Dawuda ya ɗaga ido ya ga mala’ikan Ubangiji tsaye tsakanin sama da duniya, da takobi a zāre a hannunsa ya miƙa a kan Urushalima. Sai Dawuda da dattawa, saye da rigunan makoki suka fāɗi rubda jiki.
17 Davut Tanrı'ya şöyle seslendi: “Halkın sayılmasını buyuran ben değil miydim? Günah işleyen benim, kötülük yapan benim. Ama bu koyunlar ne yaptı ki? Ya RAB Tanrım, ne olur beni ve babamın soyunu cezalandır. Bu salgın hastalığı halkın üzerinden kaldır.”
Dawuda ya ce wa Allah, “Ba ni ba ne na umarta a ƙidaya mayaƙan? Ni ne wanda ya yi zunubin da kuma abin da ba daidai ba. Waɗannan dai tumaki ne. Me suka yi? Ya Ubangiji Allahna, bari hannunka ya fāɗi a kaina da kuma iyalina, amma kada ka bar wannan annoba ya kasance a kan mutanenka.”
18 RAB'bin meleği Gad'a, Davut'un Yevuslu Ornan'ın harman yerine gidip RAB'be bir sunak kurmasını buyurdu.
Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya umarci Gad yă faɗa wa Dawuda yă haura yă gina bagade wa Ubangiji a masussukar Ornan mutumin Yebus.
19 Davut RAB'bin adıyla konuşan Gad'ın sözü uyarınca oraya gitti.
Saboda haka Dawuda ya haura cikin biyayya ga maganar da Allah ya yi da sunan Ubangiji.
20 Harman yerinde buğday döverken, Ornan arkasına dönüp meleği gördü. Yanındaki dört oğlu gizlendi.
Yayinda Ornan yake sussukar alkama, sai ya juya ya ga mala’ika;’ya’yansa maza guda huɗu da suke tare da shi suka ɓuya.
21 Davut'un yaklaştığını gören Ornan, harman yerinden çıktı, varıp Davut'un önünde yüzüstü yere kapandı.
Sai Dawuda ya kusato, sa’ad da Ornan ya duba sai ya gan shi, ya bar masussukar ya rusuna a gaban Dawuda da fuskarsa har ƙasa.
22 Davut Ornan'a, “RAB'be bir sunak kurmak üzere harman yerini bana sat” dedi, “Öyle ki, salgın hastalık halkın üzerinden kalksın. Harman yerini bana tam değerine satacaksın.”
Dawuda ya ce wa Ornan, “Ka ba ni masussukarka saboda in gina bagade wa Ubangiji, don annobar da take kan mutane tă daina. Ka sayar mini ita a cikakken kuɗinta.”
23 Ornan, “Senin olsun!” diye karşılık verdi, “Efendim kral uygun gördüğünü yapsın. İşte yakmalık sunular için öküzleri, odun olarak düvenleri, tahıl sunusu olarak buğday veriyorum. Hepsini veriyorum.”
Ornan ya ce wa Dawuda, “Ka karɓa! Bari ranka yă daɗe, sarki yă yi duk abin da ya ga ya yi masa kyau. Duba, zan ba da shanu domin hadaya ta ƙonawa, da itacen sussuka, da kuma alkama domin hadaya ta gari. Zan ba da dukan wannan.”
24 Ne var ki, Kral Davut, “Olmaz!” dedi, “Tam değerini ödeyip alacağım. Çünkü senin olanı RAB'be vermem. Karşılığını ödemeden yakmalık sunu sunmam.”
Amma Sarki Dawuda ya amsa wa Ornan ya ce, “A’a, na nace zan biya cikakken kuɗinta. Ba zan karɓi abinka kawai don Ubangiji ba, ko in miƙa hadaya ta ƙonawar da ba tă ci mini wani abu ba.”
25 Böylece Davut harman yeri için Ornan'a altı yüz şekel altın ödedi.
Saboda haka Dawuda ya biya Ornan shekel ɗari shida na zinariya saboda wurin.
26 Davut orada RAB'be bir sunak kurup yakmalık sunuları ve esenlik sunularını sundu. RAB'be yakardı. RAB yakmalık sunu sunağında gökten gönderdiği ateşle onu yanıtladı.
Dawuda ya gina bagade wa Ubangiji a can ya kuma miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, Ubangiji kuwa ya amsa masa ta wurin wuta daga sama a kan bagaden hadaya ta ƙonawa.
27 Bundan sonra RAB meleğe kılıcını kınına koymasını buyurdu. Melek buyruğa uydu.
Sa’an nan Ubangiji ya yi magana ga mala’ikan, ya kuma mayar da takobinsa a kube.
28 RAB'bin kendisine Yevuslu Ornan'ın harman yerinde yanıt verdiğini gören Davut, orada kurbanlar kesti.
A lokacin, sa’ad da Dawuda ya ga cewa Ubangiji ya amsa masa a masussukar Ornan mutumin Yebus, sai ya miƙa hadayu a can.
29 Musa'nın çölde RAB için yaptığı çadırla yakmalık sunu sunağı o sırada Givon'daki tapınma yerindeydi.
Tabanakul na Ubangiji da Musa ya yi a hamada, da kuma bagaden hadaya ta ƙonawa a lokacin suna a tudun Gibeyon.
30 Ama Davut Tanrı'ya danışmak için oraya gidemedi. Çünkü RAB'bin meleğinin kılıcından korkuyordu.
Amma Dawuda bai iya zuwa gabansa don yă yi tambaya ga Allah ba, gama yana jin tsoron takobin mala’ikan Ubangiji.

< 1 Tarihler 21 >