< Matta 12 >
1 Mane gahıl, I'sa Şabbatne yiğıl suk qevhuyne çolbışile k'ena ı'lğəə eyxhe. Mang'un telebabı mıssıba vuxhal-alla, manbışe gıt'y (sunbul) qoodu abna suk opxhan giviyğal.
A wannan lokaci, Yesu ya tafi a ranar Asabaci, ya bi cikin gonar hatsi. Almajiransa na jin yunwa, sai suka fara zagar hatsi suna ci.
2 Fariseyaaşik'le man g'acu, Mang'uk'le eyhen: – İlekkende, Yiğne telebabışe Şabbatne yiğıl hidya'asın işbı vod ha'a!
Amma da Farisawa suka gan su, sai su ka ce wa Yesu. “Duba, almajiranka su na yin abin da doka ta haramta a ranar Asabaci.”
3 I'see manbışik'le inəxüd eyhe: – Nya'a şu qətqı' dişde, Davudıy cukanbı mıs qeepxhayng'a, mang'vee hucooyiy hı'ıva?
Amma Yesu ya ce masu, “Baku karanta abin da Dauda ya yi ba, lokacin da ya ke jin yunwa, tare da mazan da ke tare da shi?
4 Mana Allahne xaaqa ikkeç'u, muq'addasın gıney alyaat'u, cukanbışika sacigee oyxhanan. Man gıney kaahinaaşile ğayrı şavuscad oxhanas ıkkan deşdiy.
Yadda ya shiga gidan Allah, ya ci gurasar alfarwa da doka ta hana shi ko mazan da ke tare da shi su ci, sai dai Firistoci ne kawai doka ta basu damar ci?
5 Şu Q'aanune qətqı' dişde, kaahinaaşe Şabbatne yiğıl Allahne Xaa iş hav'eeyib, manbışil taxsir axva deş?
Sa'annan ba ku karanta cikin shari'a cewa, a ranar Asabaci, Firistoci da ke cikin haikali na sabawa ranar Asabaci, amma kamar ba su yi laifi ba?
6 Zı şok'le eyhen, Allahne Xaaler Doyukana inyaa vor.
Amma ina tabbatar maku da cewa, wani wanda ya fi haikali girma yana nan.
7 Şok'le «Zas q'urban deş, rəhı'm vukkan» cuvab hucoo eyhen ıxhay atsts'axhanxhiy, şu taxsir deşinbışilqa bınah qaa'as deşdiy.
In da kun san ma'anar wannan 'Na fi son jinkai fiye da hadaya,' da baku shari'anta wa marar laifi ba.
8 İnsanna Dix, Zı Şabbatne yiğınar Xərna vorna.
Gama Dan mutum shine Ubangijin Asabaci.”
9 I'sa mançe sinagogeeqa qarayle.
Sa'annan Yesu ya bar wannan wuri, ya shiga majami'ar su.
10 Maa'arır xıl qeqquna sa insan eyxhe. Fariseyaaşe I'salqa taxsir qaa'asın kar t'abal ha'a ıxhayke, manbışe Mang'uke qiyghanan: – Nya'a, Q'aanunun Şabbatne yiğıl yug qaa'as havaysaranbıne?
Sai ga wani mutum wanda hannun sa ya shanye, sai Farisawa suka tambayi Yesu, cewa, “Doka ta halarta a yi warkarwa a ranar Asabaci?” Domin su zarge shi a kan zunubi.
11 I'see manbışis inəxdun alidghıniy qele: – Vuşde neng'ukamecab sa vəq'ə vuxheene, vucub Şabbatne yiğıl g'uyeeqa g'a'aybxheene, nya'a, şu mana mançe alqaahas dişde?
Yesu ya ce masu, “Wanene a cikin ku, wanda idan ya na da tunkiya guda, sa'annan tunkiyar nan ta fada a rami mai zurfi a ranar Asabaci ba zai kamo ta ya fitar da ita ba?
12 İnsan vəq'əyle nimeexheyir gıranra vor! Mançil-allab Şabbatne yiğıl yugvalla haa'as havaysarna.
Yaya za a kwatanta darajar mutum da tunkiya! Saboda haka ya halarta a yi alheri ranar Asabaci.”
13 Mançile qiyğa Mang'vee ık'arang'uk'le eyhen: – Xıl hotke! Mang'veeyid xıl hotkumee, xıl yug qexhe, mansa xıl xhinne qexhe.
Sai Yesu ya ce wa mutumin nan “Mika hannun ka.” Ya mike hannunsa, sai hannun nan ya dawo lafiyaye kamar dayan hannunsa.
14 Fariseyar sinagogeençe qığeepç'ı, I'saykın nəxüdne ha'asva gaf haa'a.
Amma Farisawa su ka fita waje su ka fara mugun shiri domin sa. Su na neman hanyar da za su kashe shi.
15 I'sayk'le man ats'axhxha mançe ayk'anna. Mang'uqab qihna geeb insanar avayk'an, Mang'vee manbışin gırgınbı yug qaa'anbı.
Da Yesu ya fahimci wannan, sai ya janye kan sa daga nan. Mutane da dama su ka bi shi, ya warkar da su duka.
16 I'see Cune hək'ee neng'uk'lecad eyhes ixhes deşva uvhu.
Ya dokace su da kada su bayyana shi ga kowa,
17 Məxüd Rəbbine mizele yuşan ha'ane Yeşaya peyğambaree otk'unin xhinne eyxhe:
domin ya zama gaskiyar abin da aka fada ta wurin annabi Ishaya, cewa,
18 «Haane Zı g'əyxı'na G'ul! Zas Mana geer ıkkan, Yizde yik'es ıkkanəxrına Mana vor. Zı Yizın Rı'h Mang'us heles. Mang'vee milletbışis qotkuyne məhkamayne hək'ee yuşan haa'as.
“Dubi, bawa na zababbe; kaunatacce na, wanda ya ke faranta mani raina sosai. Zan sa Ruhu na bisan sa, za ya furta hukunci zuwa al'ummai.
19 Mang'vee ts'irıb haa'as deş, hı'ccatıd ha'as deş, Mang'un sesid şahrabışee g'ayxhes deş.
Ba za ya yi jayayya ko tada murya ba, babu wanda za ya ji muryar sa a karabku.
20 Mang'un qotkuyn məhkama ğamdexha, Mang'vee hoççunin q'amışid haq'var ha'as deş, K'ətqəs qexhen pelyted k'ətqə'əs deş.
Ba zai karya kara da ya tankwashe ba; ba zai kashe fitilar da ta kusa mutuwa ba; sai ya kawo hukunci ga nasara.
21 Milletbışda umud Mang'une doyulqa vuxhes».
Sa'annan al'ummai za su dogara a ga sunansa.
22 Mançile qiyğa I'sayne k'anyaqa cinaaşe aqqına bı'rq'ı'na, miz avquna sa insan arayle. I'see mana yug qa'ana. Mang'uk'le g'ecenıd, yuşanır ha'ana.
Sa'annan wani mutum, makaho ne, kurma kuma, aljannu kuma na cikinsa, an kawo shi wurin Yesu. Ya warkar da shi, ya sami ganin gari ya kuma yi magana.
23 Gırgın insanar mançile mattepxha sana-sang'uke qiyghanan: – Deşxhee, inane vor Davudna Dix, Masixh?
Jama'a su ka yi mamaki kwarai, su na cewa, “Ko wannan ne Dan Dawuda?”
24 Fariseyaaşik'le man g'ayxhı eyhen: – Mang'vee cinar, cinaaşine xərıng'une Ba'al-Zevulne gucuka qığa'a.
Amma da Farisawa su ka ji wannan al'ajibi, sai su ka ce, “Mutumin nan yana fitar da aljannu ta wurin Bahalzabuba sarkin aljannu ne.”
25 Fariseyaaşine ək'leençe ı'lğəən I'sayk'le ats'axhxha, Mang'vee manbışik'le eyhen: – Sa ölka q'öne cigeeqa quvxhaxhee mana q'əra quvxhes, q'öne cigeeqa quvxhana şaharıb, xavıd geed aaxvas deş.
Amma Yesu ya san tunanin su, sai ya ce. “Duk mulkin da ya rabu gaba da kan sa, ba zaya tsaya ba, duk wani birni da ya rabu ba zai tsaya ba, ko gida da ya tsage, za ya rushe.
26 Şeyt'anın şeyt'an qığayhexheene, man adğançe q'öna qıxhava eyhen vodun. Məxüdxheene, nəxübne mançina paççahiyvalla aaxvas?
Idan Shaidan ya fitar da Shaidan, ya rabu gaba da kansa. Yaya mulkin sa za ya tsaya?
27 Zı cinar Ba'al-Zevulne gucuka qığa'axheene, manke vuşde telebabışe şavne gucukane qığa'a? Mançil-allab manbı şos haakimara vuxhes.
Idan Ina fitar da aljannu da ikon Ba'alzabuba, ta wurin wa masu bin ku su ke fitar da su? Saboda haka, su za su shari'anta ku.
28 De'eş, Zı cinar Allahne Rı'hı'ka qığa'axheene, Allahna Paççahiyvalla şolqa qabınava eyhen vodun.
Amma idan ina fitar da aljannu da Ruhun Allah ne, hakika mulkin Allah ya zo gare ku.
29 Şavusse gucnane insanne xaaqa ikkeç'u, mang'un g'el-xıl idiyt'ıl sixbı ha'as əxəyee? Məxrıng'un ts'etta g'el-xıl ayt'alas ıkkan, qiyğad sixbı ha'as.
Kuma ta yaya mutum za ya shiga gidan mai karfi ya kwashe masa kaya ba tare da ya fara daure shi ba? Sa'annan ne za ya iya satar masa kaya daga gidansa.
30 Yizın sura ıqdyaqqına, Zaka parxaçra vor, Zaka sidya'ang'veeyid dağa'anxhe.
Wanda baya tare da ni yana gaba da ni ke nan, wanda kuma baya tarawa tare da ni, yana watsarwa ne.
31 Mançil-allad Zı şok'le eyhen, insanaaşine gırgıne bınahbışileyiy kufurıle ılyheepç'esınbı, saccu Allahne Rı'hı's hı'iyne kufurıle ılyhıdeepç'es.
Saboda haka ina ce maku, kowanne zunubi da sabo, za a gafarta wa mutum, amma sabon Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta shi ba.
32 Şavaayiy İnsanne Duxayk'le cuvab uvhu mang'une bınahıle ılyheepç'esınbı, Muq'addas Rı'hı'k'le cuvab uvhuyng'unemee bınahıle ine dyunyeylib şene dyunyeylib ılyheepç'es deş. (aiōn )
Duk wanda yayi batanci ga Dan Mutum, za a gafarta masa. Amma duk wanda yayi batanci game da Ruhu Mai Tsarki ba za a gafarta masa ba, a nan duniya da har abada. (aiōn )
33 Yivek'le yugnava eyhexhee, mançine şagavık'led yugnava eyhe. De'eş, yivek'le qüvçunava eyhexhee, mançine şagavık'led qüvçunava eyhe. Yiv çine şagavıkexhe vaats'a vooxhena.
Ko dai a mai da itace mai kyau 'ya'yansa kuma su yi kyau, ko a mai da itace marar kyau 'ya'yansa kuma marasa kyau, gama ana sanin itace ta wurin 'ya'yansa.
34 Xoçebışda nasıl, şu pisınbınang'a, vuşde ghalyaqa yugun qayleyee? İnsanne yik'eedın mizelyxhe eyxhen.
Ku 'ya'yan macizai, tun da ku miyagu ne, yaya za ku iya fadin abubuwa nagari? Gama daga cikar zuciya baki ke magana.
35 Yugne insanee yugvaline xazineençe yugun karbıxhe qığa'anbı, pisıng'veeyid pisde xazineençe pisınbıxhe qığa'anbı.
Mutumin kirki daga ajiyar zuciyarsa ya kan fitar da abubuwa masu kyau, mugun mutum kuma daga mummunar ajiyar zuciyarsa ya kan fitar da abubuwan mugunta.
36 Zı şok'le eyhen, Q'iyaamatne yiğıl nişil-alla qadiy uvhuyne cuvabıl-alla, insanaaşe cuvab qeles.
Sa'annan ina ce maku a ranar shari'a, mutane za su bada lissafin abubuwan banza da su ka fadi.
37 Ghaleençe qığeç'uyne sa cuvabıl-alla vak'le qorkunavad eyhesın, menne cuvabıl-alla valqa taxsirıd gixhxhesın!
Gama ta wurin maganganun ku, za a 'yantar da ku, ta wurin maganganun ku kuma za a kashe ku.”
38 Manke Q'aanunne mə'əllimaaşeyiy fariseyaaşe I'sayk'le eyhen: – Mə'əllim, şas Ğu əlaamat hagu ıkkan.
Sa'annan wadansu Malaman Attaura, da Farisawa suka amsa suka ce wa Yesu, “Mallam, muna so mu ga wata alama daga gare ka.”
39 I'see manbışis inəxdun alidghıniy qele: – Allahne yəqqı'le qıkk'epç'iyne, ine gahıne pisde insanaaşe əlaamat t'abal ha'a. Manbışis Yunus peyğambarne əlaamatıle ğayrı nencad əlaamat heles deş.
Amma Yesu ya amsa ya ce masu, “Mugun zamani da mazinaciyar tsara, su na bukutar alama. Amma babu alamar da za a ba su, sai dai alamar annabi Yunusa.
40 Nəxüriy Yunus peyğambar xhebılle yiğnayiy xheyible xəmna xənne baluğne vuxhne axu, həməxürur İnsanna Dix, Zı xhebılle yiğnayiy xheyible xəmna ç'iyene k'oralybışee axvas.
Gama yadda Yunusa ya yi kwana uku da dare uku a cikin babban kifi, haka ma Dan Mutum zaya yi kwana uku da dare uku a cikin zuciyar kasa.
41 Ninevayne milletın Yunus peyğambarne cuvabıl k'ırı alixhxhıva, bınahbışike xıl ts'ıts'av'uva, Allahne yəqqı'lqa satk'ılva, Q'iyaamatne yiğıl manbı oza qeepxha mane insanaaşilqa taxsir gixhxhes. Həşdemee inyaa Yunusuler Xərna vor.
Mutanen Nineba za su tsaya a ranar shari'a da wannan zamani sannan su kashe su. Domin sun tuba da suka ji wa'azin Yunusa, amma duba wanda ya fi Yunusa yana nan.
42 Canubne kraliçeeyid dyunyeyne şene q'omançe arı Sıleymanne k'orane ək'elil k'ırı alixhxhıva, məng'eeyid Q'iyaamatne yiğıl oza qiyxha mane insanaaşilqa taxsir gixhxhes. Həşdemee inyaa Sıleymanıler Xərna vor.
Sarauniyar Kudu za ta tashi da mutanen wannan zamani ta kuma kashe su. Ta zo daga karshen duniya domin ta ji hikimar Sulaimanu, kuma duba, wanda ya fi Sulaimanu yana nan.
43 Cin insanne adğançe qığeç'uyle qiyğa xhyanbı deşde cigabışee iliyk'ar axva, çisın manzil haa'asın ciga t'abal ha'a, yicıd iveeke deş.
Idan kazamin ruhu ya rabu da mutum, ya kan wuce ya nemi wuraren da ruwa yake domin ya huta, amma bai samu ba.
44 Mane gahıl mançin eyhen: «Zı dorala, qığeç'uynecar xaaqa sak'alas». Mane xaaqa sak'ımee, mançik'le xav qatxhu, vuşucar dena, məttıda g'aces.
Sai ya ce, 'zan koma gidana inda na fito'. Bayan ya dawo, sai ya tarar da gidan nan an share shi ya zama da tsabta.
45 Manke man atk'ın çikasana yighılle çiled pisın cinar qott'ul qales. Manbıd maqa adı, maayıd axvasınbı. Məxrune insanıs qiyğa ıxhayn, ts'etta ıxhaynçile pisda qales. İne gahıne pisde insanaaşine vuk'lelqad man qales.
Sai ya koma ya kawo wadansu ruhohi guda bakwai, wadanda su ka fi shi mugunta, sa'annan dukan su su zo su zauna a nan. Sa'annan yanayin mutumin nan na karshe ya fi na farko muni. Haka zaya kasance ga wannan mugun zamani.
46 I'sa cəmə'ətıka yuşan ha'amee, Mang'una yediy Mang'un çocar Mang'uka yuşan haa'asva abı, g'ab ulyoozar.
Sa'adda Yesu ya ke yi wa Jama'a jawabi, sai mahaifiyarsa da 'yan'uwansa su ka zo su ka tsaya a waje, suna neman su yi magana da shi.
47 Şavaamee Mang'uk'le eyhen: – Yiğna yediy Yiğın çocar g'abıb ulyobzur, Vakavub yuşan haa'as vukkan.
Sai wani ya ce masa, “Duba, mahaifiyarka da 'yan'uwanka suna tsaye a waje, suna so su yi magana da kai”.
48 I'see mane insanıs inəxdun alidghıniy qele: – Yizda yediy Yizın çocar vuşbıne?
Amma Yesu ya amsa ya ce wa shi wanda ya gaya masa, “Wacece mahaifiyata? Kuma su wanene 'yan'uwana?”
49 Mang'vee xıleka Cun telebabı haagu eyhen: – Yizda yedir, Yizın çocar inbı vob.
Sai ya mika hannu ya nuna almajiransa ya ce, “Duba, ga mahaifiyata da 'yan'uwana!
50 Şavaayiy Yizde Xəybışeene Dekkıs ıkkanan ha'a, manar Yizda çoc, Yizda yiçu, Yizda yed yeexhe.
Gama duk wanda yake aikata nufin Ubana wanda ya ke cikin sama, shine dan'uwana, da 'yar'uwata da mahaifiyata.”