< Psaltaren 132 >
1 En vallfartssång. Tänk, HERRE, David till godo, på allt vad han fick lida,
Waƙar haurawa. Ya Ubangiji, ka tuna da Dawuda da kuma dukan irin wuyan da ya jimre.
2 han som svor HERREN en ed och gjorde ett löfte åt den Starke i Jakob;
Ya yi rantsuwa ga Ubangiji ya kuma yi alkawari ga Maɗaukaki na Yaƙub cewa,
3 "Jag skall icke gå in i den hydda där jag bor, ej heller bestiga mitt viloläger,
“Ba zan shiga gidana ko in kwanta a gado ba,
4 jag skall icke unna mina ögon sömn eller mina ögonlock slummer,
ba zan ba wa idanuna barci ba, ba gyangyaɗi wa idanuna,
5 förrän jag har funnit en plats åt HERREN, en boning åt den Starke i Jakob."
sai na sami wuri wa Ubangiji, mazauni domin Maɗaukaki na Yaƙub.”
6 Ja, vi hörde därom i Efrata, vi förnummo det i skogsbygden.
Mun ji haka a Efrata, muka yi ƙaro da shi a filayen Ya’ar,
7 Låtom oss gå in i hans boning, tillbedja vid hans fotapall.
“Bari mu tafi wurin zamansa; bari mu yi sujada a wurin sa ƙafafunsa,
8 Stå upp, HERRE, och kom till din vilostad, du och din makts ark.
ka tashi, ya Ubangiji, ka kuma zo wurin hutunka, kai da akwatin alkawarin ƙarfinka.
9 Dina präster vare klädda i rättfärdighet, och dina fromma juble.
Bari a suturta firistocinka da adalci; bari tsarkakanka su rera don farin ciki.”
10 För din tjänare Davids skull må du icke visa tillbaka din smorde.
Saboda Dawuda bawanka, kada ka ƙi shafaffenka.
11 HERREN har svurit David en osviklig ed, som han icke skall rygga: "Av ditt livs frukt skall jag sätta konungar på din tron.
Ubangiji ya rantse wa Dawuda tabbataccen rantsuwa cewa ba zai janye ba cewa, “Ɗaya daga cikin zuriyarka zan sa a kan kursiyinka,
12 Om dina barn hålla mitt förbund och hålla mitt vittnesbörd, som jag skall lära dem, så skola ock deras barn till evig tid få sitta på din tron.
in’ya’yanka maza za su kiyaye alkawari da farillan da na koya musu, to’ya’yansu maza za su zauna a kan kursiyinka har abada abadin.”
13 Ty HERREN har utvalt Sion, där vill han hava sin boning.
Gama Ubangiji ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa,
14 Detta är min vilostad till evig tid; här skall jag bo, ty till detta ställe har jag lust.
“Wannan shi ne wurin hutuna har abada abadin; a nan zan zauna ina mulki gama ina son ta,
15 Dess förråd skall jag rikligen välsigna, åt dess fattiga skall jag giva bröd till fyllest.
zan albarkace ta da tanade-tanade masu yawa; matalautanta za su ƙoshi da abinci.
16 Dess präster skall jag kläda i frälsning, och dess fromma skola jubla högt.
Zan suturta firistocinta da ceto, tsarkakanta kuma kullum za su rera don farin ciki.
17 Där skall jag låta ett horn skjuta upp åt David; där har jag rett till en lampa åt min smorde.
“A nan zan sa ƙaho ya yi girma wa Dawuda in kuma kafa fitila saboda shafaffena.
18 Hans fiender skall jag kläda i skam, men på honom skall hans krona glänsa."
Zan suturta abokan gābansa da kunya, amma rawanin da yake a kansa zai yi ta walƙiya.”