< Jesaja 24 >

1 Se, HERREN ödelägger jorden och föröder den; han omvälver, vad därpå är, och förströr dess inbyggare.
Duba, Ubangiji zai wofinta duniya ya kuma yi kaca-kaca da ita; zai ɓata fuskarta ya watsar da mazaunanta,
2 Och det går prästen såsom folket, husbonden såsom tjänaren, husfrun såsom tjänarinnan, säljaren såsom köparen, låntagaren såsom långivaren, gäldenären såsom borgenären.
zai zama abu ɗaya ga firist kamar yadda yake ga mutane, ga maigida kamar yadda yake ga bawa, ga uwargijiya kamar yadda yake ga baiwa, ga mai sayarwa kamar yadda yake ga mai saya, ga mai karɓan rance kamar yadda yake ga mai ba da rance, ga mai karɓan bashi kamar yadda yake ga mai ba da bashi.
3 Jorden bliver i grund ödelagd och i grund utplundrad; ty HERREN har talat detta ord.
Za a wofinta duniya ƙaƙaf a kuma washe ta sarai. Ubangiji ne ya faɗa haka.
4 Jorden sörjer och tvinar bort, jordkretsen försmäktar och tvinar bort, vad högt är bland jordens folk försmäktar.
Duniya ta bushe ta kuma yanƙwane, duniya tana shan azaba ta kuma raunana, masu daraja na duniya suna shan azaba.
5 Ty jorden har blivit ohelgad under sina inbyggare; de hava överträtt lagarna, de hava förvandlat rätten, brutit det eviga förbundet.
Duniya ta ƙazantu ta wurin mutanenta sun ƙi yin biyayya da dokoki, sun keta farillai suka kuma karya madawwamin alkawari.
6 Därför uppfräter förbannelse jorden, och de som bo där måste lida, vad de hava förskyllt; därför förtäras jordens inbyggare av hetta, så att ej många människor finnas kvar.
Saboda haka la’ana za tă auko wa duniya; dole mutanenta su ɗauki hakkin laifinsu. Saboda haka aka ƙone mazaunan duniya, kuma kaɗan ne kurum suka rage.
7 Vinmusten sörjer, vinträdet försmäktar; de som voro så hjärteglada sucka nu alla.
Sabon ruwan inabi ya bushe kuringar inabi kuma sun yanƙwane; dukan masu farin ciki suna nishi.
8 Det är förbi med fröjden vid pukornas ljud, de gladas larm ha tystnat; det är förbi med fröjden vid harpans klang.
Kaɗe-kaɗen garayu sun yi shiru, surutun masu murna ya daina, garayan farin ciki ya yi shiru.
9 Vin dricker man icke mer under sång, rusdrycken kännes bitter för dem som dricka den.
Babu sauran shan ruwan inabi suna rera waƙa; barasa ya zama da ɗaci ga masu shanta.
10 Nedbruten ligger den öde staden; vart hus är stängt, så att ingen kommer därin.
Birnin da aka birkice ta zama kango; an kulle ƙofar shiga kowane gida.
11 Därute höres klagorop över vinet; all glädje är såsom en nedgången sol, all jordens fröjd har flyktat.
A tituna suna kukan neman ruwan inabi; dukan farin ciki ya dawo baƙin ciki, an hana dukan kaɗe-kaɗe a duniya.
12 Ödeläggelse allenast är kvar i staden, och porten är slagen i spillror.
An bar birnin kango, aka yi kaca-kaca da ƙofofinta.
13 Ty det måste så gå på jorden bland folken, såsom det går, när man slår ned oliver, såsom när man gör en efterskörd, sedan vinbärgningen är slut.
Haka zai zama a duniya da kuma a cikin al’ummai, kamar sa’ad da akan karkaɗe itacen zaitun, ko kuma kamar sa’ad da ake barin kala bayan an girbe inabi.
14 Dessa häva då upp sin röst och jubla; fröjderop över HERRENS höghet ljuda borta i väster:
Sun daga muryoyinsu, sun yi sowa ta farin ciki; daga yamma sun furta darajar Ubangiji.
15 "Ären därför HERREN i österns bygder, även i havsländerna HERRENS, Israels Guds, namn."
Saboda haka a gabas sun ɗaukaka Ubangiji, a ɗaukaka sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, a cikin tsibiran teku.
16 Från jordens ända höra vi lovsånger: "En härlig lott får den rättfärdige!" Men jag säger: Jag arme, jag arme, ve mig! Härjare härja, ja härjande fara härjare fram.
Daga iyakokin duniya mun ji waƙoƙi, “Ɗaukaka ga Mai Adalcin nan.” Amma na ce, “Na lalace, na lalace! Kaitona! Munafukai sun ci amana! Da munafunci munafukai sun ci amana!”
17 Faror, fallgropar och fällor vänta eder, I jordens inbyggare.
Razana da rami da tarko suna jiranku, Ya mutanen duniya.
18 Och om någon flyr undan farlighetsropen, så störtar han i fallgropen, och om han kommer upp ur fallgropen, så fångas han i fällan. Ty fönstren i höjden äro öppnade, och jordens grundvalar bäva.
Duk wanda ya yi ƙoƙarin tserewa daga ƙarar razana zai fāɗa cikin rami; wanda kuma ya tsere daga rami za a kama shi a tarko. An buɗe ƙofofin ambaliyar ruwan sama, harsashen ginin duniya suna rawa.
19 Jorden brister, ja, den brister; jorden rämnar, ja, den rämnar; jorden vacklar, ja, den vacklar;
An tsage duniya, duniya ta farfashe ta wage, an girgiza duniya ƙwarai.
20 jorden raglar, ja, den raglar såsom en drucken; den gungar såsom vaktskjulet i trädets topp. Dess överträdelse vilar tung på den, och den faller och kan icke mer stå upp.
Duniya tana tangaɗi kamar mashayi, tana lilo kamar rumfa a cikin iska; laifin tayarwarta ya yi nauyi sosai har ta fāɗi ba kuwa za tă ƙara tashi ba.
21 På den tiden skall HERREN hemsöka höjdens här uppe i höjden och jordens konungar nere på jorden.
A wannan rana Ubangiji zai hukunta ikokin da suke cikin sama da kuma sarakunan da suke a duniya.
22 Och de skola samlas tillhopa, såsom fångar hopsamlas i fånggropen, och skola inneslutas i fängelse; sent omsider når dem hemsökelsen.
Za a tattara su tare kamar ɗaurarru a kurkuku; za a rufe su a kurkuku a kuma hukunta su bayan kwanaki masu yawa.
23 Då skall månen blygas och solen skämmas; ty HERREN Sebaot skall då vara konung på Sions berg och i Jerusalem, och hans äldste skola skåda härlighet.
Sa’an nan wata zai ruɗe, rana ta ji kunya; gama Ubangiji Maɗaukaki zai yi mulki a kan Dutsen Sihiyona da kuma a cikin Urushalima, da kuma a gaban dattawanta, da ɗaukaka.

< Jesaja 24 >