< Amos 7 >

1 Följande syn lät Herren, HERREN mig se; Jag såg gräshoppor skapas, när sommargräset begynte växa upp; och det var sommargräset efter kungsslåttern.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji yana shirya cincirindon fāri bayan da aka ƙarasa yankan rabon hatsin da yake na sarki, hatsi na biyu kuma yake tohuwa.
2 När så dessa hade ätit upp alla markens örter, sade jag: "Herre, HERRE, förlåt. Huru skall Jakob kunna bestå, han som är så ringa?"
Sa’ad da suka cinye kome, sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ka gafarta! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
3 Då ångrade HERREN detta. "Det skall icke ske", sade HERREN.
Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ba zai faru ba,” in ji Ubangiji.
4 Följande syn lät Herren, HERREN mig se: Jag såg Herren, HERREN nalkas för att utföra sin sak genom eld; och elden förtärde det stora djupet och höll på att förtära arvedelslandet.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji Mai Iko Duka yana shirin hukunta da wuta; wutar ta ƙone teku ta kuma ƙone ƙasa.
5 Då sade jag: "Herre, HERRE, håll upp. Huru skall Jakob kunna bestå, han som är så ringa?"
Sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ina roƙonka ka dakata! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
6 Då ångrade HERREN detta. "Icke heller detta skall ske", sade Herren, HERREN.
Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ma ba zai faru ba,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
7 Följande syn lät han mig se: Jag såg Herren stå på en mur, uppförd efter sänklod, och i sin hand höll han ett sänklod.
Ga abin da ya nuna mini. Ubangiji yana tsaye kusa da bangon da aka gina, bisa ga awon igiyar gwada gini, da kuma magwaji a hannunsa.
8 Och HERREN sade till mig: "Vad ser du, Amos?" Jag svarade: "Ett sänklod." Då sade Herren: "Se, jag skall hänga upp ett sänklod mitt ibland mitt folk Israel; jag kan icke vidare tillgiva dem.
Sai Ubangiji ya tambaye ni, “Me kake gani, Amos?” Sai na amsa, “Igiyar gwada gini.” Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Duba, zan sa igiyan nan a cikin mutanena Isra’ila; ba zan ƙara barinsu ba.
9 Isaks offerhöjder skola bliva ödelagda och Israels helgedomar förstörda, och mot Jerobeams hus skall jag uppresa mig med svärdet."
“Za a hallakar da wuraren sujada na Ishaku kuma tsarkakan wurare na Isra’ila za su zama kango; da takobina zan tayar wa gidan Yerobowam.”
10 Men Amasja, prästen i Betel, sände till Jerobeam, Israels konung, och lät säga: "Amos förehar en sammansvärjning mot dig, mitt i Israels hus. Landet kan icke härda ut med allt hans ordande.
Sai Amaziya firist na Betel ya aika da saƙo zuwa wurin Yerobowam sarkin Isra’ila. “Amos yana shirya maka maƙarƙashiya a tsakiyar Isra’ila. Ƙasar ba za tă iya ɗauka abubuwan da yake faɗi ba.
11 Ty så har Amos sagt: 'Jerobeam skall dö för svärd, och Israel skall föras bort i fångenskap ur sitt land.'"
Gama ga abin da Amos yake cewa, “‘Yerobowam zai mutu ta wurin takobi, kuma tabbatacce Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
12 Och Amasja sade till Amos: "Du siare, gå din väg och sök din tillflykt i Juda land; där må du äta ditt bröd, och där må du profetera.
Sai Amaziya ya ce wa Amos, “Tafi daga nan, mai duba kawai! Koma ƙasar Yahuda. Ka nemi abin zaman garinka a can ka kuma yi annabcinka a can.
13 Men i Betel får du icke vidare profetera, ty det är en konungslig helgedom och ett rikets tempel."
Kada ka ƙara yin annabci a Betel, gama nan wuri mai tsarki ne na sarki da kuma haikalin ƙasar.”
14 Då svarade Amos och sade till Amasja: "Jag är varken en profet eller en profetlärljunge, jag är en boskapsherde, som lever av mullbärsfikon.
Amos ya amsa wa Amaziya, “Ni ba annabi ba ne ko ɗan annabi, amma ni makiyayi ne, kuma ina lura da itatuwan al’ul.
15 Men HERREN tog mig från hjorden; HERREN sade till mig: 'Gå åstad och profetera för mitt folk Israel.'
Amma Ubangiji ya ɗauke ni daga kiwon dabbobi ya ce mini, ‘Je ka, ka yi wa mutanena Isra’ila annabci.’
16 Så hör nu HERRENS ord. Du säger: 'Profetera icke mot Israel och predika icke mot Isaks hus.'
Yanzu fa, sai ka ji maganar Ubangiji. Ka ce, “‘Kada in yi annabci a kan Isra’ila, kuma in daina yin wa’azi a kan gidan Ishaku.’
17 Därför säger HERREN så: Din hustru skall bliva en sköka i staden, dina söner och döttrar skola falla för svärd, ditt land skall bliva utskiftat med mätsnöre, själv skall du dö i ett orent land, och Israel skall föras bort i fångenskap ur sitt land."
“Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce, “‘Matarka za tă zama karuwa a cikin birni, kuma da takobi za a kashe’ya’yanka maza da mata. Za a auna ƙasarka a kuma raba ta, kai kuma za ka mutu a ƙasar arna. Ba shakka Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”

< Amos 7 >