< Psaltaren 17 >
1 En bön av David. Hör, o HERRE, en rättfärdig sak, akta på mitt rop, lyssna till min bön; den kommer icke ifrån falska läppar.
Addu’a ce ta Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, roƙona na adalci; ka saurari kukata. Ka kasa kunne ga addu’ata, ba ta fitowa daga leɓuna masu ƙarya.
2 Av dig må jag få min rätt; dina ögon må skåda vad rättvist är.
Bari fiffitawata tă zo daga gare ka; bari idanunka su ga abin da yake daidai.
3 Du prövar mitt hjärta, du utrannsakar mig, men du finner intet; ingen ond tanke går ut ur min mun.
Ko ka duba zuciyata, ka kuma bincike ni da dare, ko ka gwada ni, ba za ka sami kome ba; na yanke shawara cewa bakina ba zai yi zunubi ba.
4 Efter dina läppars ord, och vad människor än må göra, tager jag mig till vara för våldsverkares stigar.
Game da ayyukan mutane kuwa, ta wurin maganar leɓunanka na kiyaye kaina daga hanyoyin tashin hankali.
5 Mina steg hålla sig stadigt på dina vägar, mina fötter vackla icke.
Sawuna sun kama hanyoyinka ƙafafu kuwa ba za su yi santsi ba.
6 Så åkallar jag nu dig, ty du, Gud, skall svara mig; böj ditt öra till mig, hör mitt tal.
Na kira gare ka, ya Allah, gama za ka amsa mini; ka kasa kunne ka kuma ji addu’ata.
7 Bevisa din underbara nåd, du som frälsar undan motståndarna dem som taga sin tillflykt till din högra hand.
Ka nuna mini girmar ƙaunarka mai banmamaki, kai da kake ceton waɗanda suke neman mafaka daga abokan gābansu da hannunka na dama.
8 Bevara mig såsom en ögonsten, beskärma mig under dina vingars skugga
Ka kiyaye ni yadda ake kiyaye ido; ka ɓoye ni cikin inuwar fikafikanka
9 för de ogudaktiga, som vilja fördärva mig, för mina dödsfiender, som omringa mig.
daga mugaye waɗanda suke kai mini hari, daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.
10 Sitt hjärta förstocka de; med sin mun tala de stora ord.
Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
11 Nu äro de omkring mig, var vi gå, deras ögon speja efter huru de skola böja mig till jorden.
Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
12 Ja, denne är lik ett lejon som längtar efter rov, lik ett ungt lejon som ligger i försåt.
Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.
13 Stå upp, HERRE; träd emot honom, slå honom ned, rädda med ditt svärd min själ från den ogudaktige,
Ka tashi, ya Ubangiji, ka yi arangama da su, ka durƙusar da su; ka cece ni daga mugaye ta wurin takobinka.
14 ja, med din hand, från människorna, HERRE, från denna världens människor, som hava sin del i detta livet, och vilkas buk du fyller med dina håvor, som hava söner i mängd och lämna sitt överflöd åt sina barn.
Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so;’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa’ya’yansu.
15 Men jag skall skåda ditt ansikte i rättfärdighet; när jag uppvaknar, vill jag mätta mig av din åsyn.
Amma ni, cikin adalci zan ga fuskarka; sa’ad da na farka, zan gamsu da ganin kamanninka.