< Jesaja 41 >
1 Tigen, I havsländer, och lyssnen till mig, och må folken hämta ny kraft; må de så komma fram och tala, ja, låt oss med varandra träda inför rätta.
“Ku yi shiru a gabana, ku tsibirai! Bari al’ummai su sabunta ƙarfinsu! Bari su zo gaba su yi magana; bari mu sadu a wurin shari’a.
2 Vem har i öster låtit denne uppstå, som mötes av seger, var han går fram? Vem giver folkslag i hans våld och gör honom till härskare över konungar? Vem gör deras svärd till stoft och deras bågar till strå som föres bort av vinden?
“Wa ya zuga wannan daga gabas, yana kiransa cikin adalci ga yin hidima? Ya miƙa masa al’ummai ya kuma yi nasara da sarakuna a gabansa. Ya mai da su ƙura da takobinsa, zuwa inda iska ke hurawa ta wurin bugun da ya yi musu.
3 Han förjagar dem, där han går lyckosam fram, vanliga vägar trampar icke hans fot.
Ya fafare su ya kuma yi tafiyarsa lafiya ƙalau, a hanyar da ƙafafunsa ba su taɓa bi ba.
4 Vem har verkat och utfört detta? Det har han som från begynnelsen kallade människors släkten fram: jag, HERREN, som är den förste och som intill det sista är densamme.
Wane ne ya taɓa yin haka ya kuma sa ya faru, yana kira ga tsararraki daga farko? Ni, Ubangiji ina can tun farkonsu ni kuma ina can har ƙarshe, Ni ne shi.”
5 Havsländerna se det och frukta, och jordens ändar förskräckas. Man närmar sig till varandra och kommer tillhopa.
Tsibirai sun gan shi suka kuma ji tsoro; iyakokin duniya sun yi rawar jiki. Suka kusato suka kuma zo gaba;
6 Den ene vill hjälpa den andre; han säger till den andre: »Fatta mod!»
kowa na taimakon wani yana ce wa ɗan’uwansa, “Ka ƙarfafa!”
7 Träsnidaren sätter mod i guldsmeden, bleckslagaren i den som hamrar på städ. Han säger om lödningen: »Den är god» och fäster bilden med spikar, så att den ej faller omkull.
Masassaƙi yakan ƙarfafa maƙerin zinariya, kuma shi mai gyara da guduma ya yi sumul yakan ƙarfafa mai harhaɗawa. Ya ce game da haɗin, “Ya yi kyau.” Yakan buga ƙusoshi su riƙe gunkin don kada yă fāɗi.
8 Men du Israel, min tjänare, du Jakob, som jag har utvalt, du ättling av Abraham, min vän,
“Amma kai, ya Isra’ila, bawana, Yaƙub, wanda na zaɓa, zuriyar Ibrahim abokina,
9 du som jag har hämtat från jordens ändar och kallat hit från dess yttersta hörn och till vilken jag har sagt: »Du är min tjänare, dig har jag utvalt och icke försmått»,
na ɗauke ka daga iyakar duniya, daga kusurwoyi masu nesa na kira ka. Na ce, ‘Kai bawana ne’; na zaɓe ka ban kuwa ƙi ka ba.
10 frukta icke, ty jag är med dig; var ej försagd, ty jag är din Gud. Jag styrker dig, jag hjälper dig ock, jag uppehåller dig med min rättfärdighets högra hand.
Saboda haka kada ka ji tsoro, gama ina tare da kai; kada ka karai, gama ni ne Allahnka. Zan ƙarfafa ka in kuma taimake ka; zan riƙe ka da hannun damana mai adalci.
11 Se, alla som äro dig hätska skola komma på skam och blygas; dina motståndare skola bliva till intet och skola förgås.
“Duk wanda ya yi fushi da kai tabbatacce zai sha kunya da ƙasƙanci; waɗanda suka yi hamayya da kai za su zama kamar ba kome ba su kuma hallaka.
12 Du skall söka efter dina vedersakare, men icke finna dem; ja, de som strida mot dig skola bliva till intet och få en ände.
Ko ka nemi abokan gābanka, ba za ka same su ba. Waɗanda suke yaƙi da kai za su zama kamar ba kome ba.
13 Ty jag är HERREN, din Gud, som håller dig vid din högra hand och som säger till dig: Frukta icke, jag hjälper dig.
Gama ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya riƙe ka da hannun damana ya kuma ce maka, Kada ka ji tsoro; zan taimake ka.
14 Så frukta nu icke, du mask Jakob, du Israels lilla hop. Jag hjälper dig, säger HERREN; din förlossare är Israels Helige.
Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub marar ƙarfi, ya ƙaramin Isra’ila, gama ni kaina zan taimake ka,” in ji Ubangiji, Mai Fansarka, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
15 Se, jag gör dig till en tröskvagn, ny och med skarpa taggar, så att du skall söndertröska berg och krossa dem till stoft och göra höjder lika agnar.
“Duba, zan sa ka cikin abin sussuka, saboda kuma mai kaifi mai haƙora da yawa. Za ka yi sussukar duwatsu ka ragargaza su, ka kuma farfashe tuddai su zama kamar yayi.
16 Du skall kasta dem med kastskovel, och vinden skall föra dem bort och stormen förskingra dem; men du själv skall fröjda dig i HERREN och berömma dig av Israels Helige.
Za ka tankaɗe su, iska kuma ta kwashe su, guguwa kuma za tă warwatsa su. Amma za ka yi farin ciki a cikin Ubangiji ka kuma ɗaukaka a cikin Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
17 De betryckta och fattiga söka förgäves efter vatten, deras tunga försmäktar av törst; men jag, HERREN, skall bönhöra dem, jag, Israels Gud, skall icke övergiva dem.
“Matalauta da mabukata suna neman ruwa, amma babu kome; harsunansu sun bushe saboda ƙishi. Amma Ni Ubangiji zan amsa musu; Ni, Allah na Isra’ila, ba zan yashe su ba.
18 Jag skall låta strömmar rinna upp på höjderna och källor i dalarna; jag skall göra öknen till en vattenrik sjö och torrt land till källsprång.
Zan sa koguna su malalo a ƙeƙasassun tuddai, maɓulɓulan ruwa kuma a kwaruruka. Zan mai da hamada tafkunan ruwa, busasshiyar ƙasa kuma ta zama maɓulɓulan ruwa.
19 Och jag skall låta cedrar och akacieträd växa upp i öknen jämte myrten och olivträd och skall på hedmarken plantera cypress tillsammans med alm och buxbom,
Zan sa a hamada ta tsiro da al’ul da itacen ƙirya, da itacen ci-zaƙi, da zaitun. Zan sa itace mai girma a ƙasashe masu sanyi ya tsiro a ƙeƙasasshiyar ƙasa, tare da fir da kuma saifires,
20 för att man skall både se och veta och akta på och förstå, att HERRENS hand har gjort detta, att Israels Helige har skapat det.
don mutane su gani su kuma sani, su lura su kuma fahimci, cewa hannun Ubangiji ne ya aikata haka, cewa Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya sa abin ya faru.
21 Så träden nu fram med eder sak, säger HERREN; kommen med edra bevis, säger Jakobs konung.
“Ka gabatar da damuwarka,” in ji Ubangiji. “Ka kawo gardandaminka,” in ji Sarki na Yaƙub.
22 Ja, må man komma med dem och förkunna för oss, vad som skall ske. Var äro edra forna utsagor? Läggen fram dem, för att vi må akta på dem och se till, huru de hava gått i fullbordan. Eller låten oss höra, vad som nu skall komma,
“Ka shigar da gumakanka don su faɗa mana abin da zai faru. Faɗa mana abubuwan da suka riga suka faru, domin mu lura da su mu kuma san abin da zai faru a ƙarshe. Ko kuwa ku furta mana abubuwan da za su faru,
23 förkunnen, vad framdeles skall hända, för att vi må se, att I ären gudar. Ja, gören någonting, vad det nu vara må, så att vi alla häpna, när vi se det.
faɗa mana abin da nan gaba ta ƙunsa, don mu san cewa ku alloli ne. Ku yi wani abu, mai kyau ko mummuna, don mu ji tsoro da fargaba.
24 Men se, I ären ett intet, och edert verk är alls intet; den som utväljer eder är en styggelse.
Amma ku ba kome ba ne kuma ayyukanku banza da wofi ne; duk wanda ya zaɓe ku abin ƙyama ne.
25 Jag lät i norr en man uppstå, och han kom, ja, i öster en som skulle åkalla mitt namn; och han skulle gå fram över landsherrarna, såsom vore de lerjord, lik en krukmakare, som trampar lera.
“Na zuga wani daga arewa, ya kuwa zo, wani daga inda rana ke fitowa wanda yake kira bisa sunana. Yana takawa a kan masu mulki kamar da taɓarya, sai ka ce maginin tukwane yana taka laka.
26 Vem förkunnade detta förut, så att vi fingo veta det, eller i förväg, så att vi kunde säga: »Du hade rätt»? Ingen fanns, som förkunnade det, ingen, som lät oss höra det, ingen, som hörde eder tala därom.
Wa ya faɗi wannan tun daga farko, don mu sani, ko kafin ya faru, don mu ce, ‘Ya faɗi daidai’? Ba wanda ya faɗa wannan, ba wanda ya riga faɗe shi, ba wanda ya ji wata magana daga gare ku.
27 Jag är den förste, som säger till Sion: »Se, se där äro de», den förste, som bringar Jerusalem detta glädjens budskap.
Ni ne na farkon da ya ce wa Sihiyona, ‘Duba, ga su nan!’ Na ba wa Urushalima saƙon labari mai daɗi.
28 Jag ser mig om, men här finnes ingen, ingen bland dessa, som kan giva besked; ingen som kan giva ett svar på min fråga.
Na duba amma ba kowa ba wani a cikinsu da zai ba da shawara, ba wani da zai ba da amsa sa’ad da na tambaye su.
29 Se, de äro allasammans fåfänglighet, deras verk äro ett intet, deras beläten vind och tomhet.
Duba, dukansu masu ƙarya ne! Ayyukansu ba su da riba; siffofinsu iska ne kawai da ruɗami.