< Jesaja 40 >
1 Trösten, trösten mitt folk, säger eder Gud.
Ta’aziyya, ku ta’azantu mutanena, in ji Allahnku.
2 Talen ljuvligt till Jerusalem och prediken för det, att dess vedermöda är slut, att dess missgärning är försonad och att det har fått dubbelt igen av HERRENS hand för all sina synder.
Yi magana mai kwantar da rai ga Urushalima, ku kuma furta mata cewa aiki mai zafinta ya isa, cewa an fanshi zunubinta, cewa ta karɓi daga hannun Ubangiji ninki biyu saboda dukan zunubanta.
3 Hör, man ropar; »Bereden väg för HERREN i öknen, banen på hedmarken en jämn väg för vår Gud.
Muryar wani tana kira cewa, “A cikin hamada ku shirya hanya saboda Ubangiji; ku miƙe manyan hanyoyi domin Allahnmu a cikin jeji.
4 Alla dalar skola höjas och alla berg och höjder sänkas; vad ojämnt är skall jämnas, och vad oländigt är skall bliva slät mark.
Za a cike kowane kwari, a baje kowane dutse da kowane tudu; za a mayar da karkatattun wurare su zama sumul, munanan wurare kuma su zama da kyau.
5 HERRENS härlighet skall varda uppenbarad, och allt kött skall tillsammans se den. Ty så har HERRENS mun talat.»
Za a kuma bayyana ɗaukakar Ubangiji, dukan mutane kuwa za su gan ta. Gama Ubangiji da kansa ne ya yi magana.”
6 Hör, någon talar: »Predika!», och en annan svarar: »Vad skall jag predika?» »Allt kött är gräs och all dess härlighet såsom ett blomster på marken.
Muryar tana cewa, “Ka yi shela.” Na kuwa ce, “Me zan yi shelar?” “Dukan mutane kamar ciyawa suke, kuma dukan ɗaukakarsu kamar furannin jeji ne.
7 Gräset torkar bort, blomstret förvissnar, när HERRENS andedräkt blåser därpå.
Ciyawa takan yanƙwane, furanni kuma su yi yaushi, domin Ubangiji ya hura iska a kansu. Tabbatacce mutane ciyawa ne.
8 Gräset torkar bort, blomstret förvissnar, men vår Guds ord förbliver evinnerligen.»
Hakika ciyawa takan yanƙwane, furanni kuma su yi yaushi, amma maganar Allahnmu tana nan daram har abada.”
9 Stig upp på ett högt berg, Sion, du glädjens budbärarinna; häv upp din röst med kraft, Jerusalem, du glädjens budbärarinna: häv upp den utan fruktan, säg till Juda stöder: »Se, där är eder Gud!»
Kai da ka kawo labari mai daɗi wa Sihiyona, ka haura a bisa dutse. Kai da ka kawo labari mai daɗi wa Urushalima, ka tā da muryarka ka yi ihu, ka ɗaga ta, kada ka ji tsoro; faɗa wa garuruwan Yahuda, “Ga Allahnku!”
10 Ja, Herren, HERREN kommer med väldighet, och hans arm visar sin makt. Se, han har med sig sin lön, och hans segerbyte går framför honom.
Duba, Ubangiji Mai Iko Duka yana zuwa da iko, hannunsa kuma yana yin mulki dominsa. Duba, ladarsa tana tare da shi, sakamakonsa kuma na rakiyarsa.
11 Han för sin hjord i bet såsom en herde, han samlar lammen i sin famn och bär dem i sitt sköte och sakta för han moderfåren fram.
Yakan lura da garkensa kamar makiyayi. Yakan tattara tumaki wuri ɗaya yă riƙe su kurkusa da ƙirjinsa; a hankali kuma yakan bi da masu ba da mama.
12 Vem är det, som mäter upp havens vatten i sin hand och märker ut himmelens vidd med sina utspända fingrar? Vem mäter upp stoftet på jorden med ett tredingsmått? Vem väger bergen på en våg och höjderna på en viktskål?
Wane ne ya auna ruwaye a tafin hannunsa, ko kuwa ya gwada tsawon sammai da fāɗin tafin hannunsa? Wane ne ya riƙe ƙurar ƙasa a kwando, ko kuwa ya auna nauyin duwatsu a magwaji, tuddai kuma a ma’auni?
13 Vem kan utrannsaka HERRENS Ande, och vem kan giva honom råd och undervisa honom?
Wane ne ya fahimci zuciyarUbangiji, ko kuwa ya koya masa a matsayin mashawarcinsa?
14 Går han till råds med någon, för att denne skall giva honom förstånd och lära honom den rätta stigen, lära honom kunskap och visa honom förståndets väg?
Wane ne Ubangiji ya nemi shawararsa don yă ganar da shi, wane ne kuma ya koya masa hanyar da ta dace? Wane ne ya koya masa sani ko ya nuna masa hanyar fahimta?
15 Nej, folken äro att akta såsom en droppe ur ämbaret och såsom ett grand på vågskålen; se, havsländerna lyfter han såsom ett stoftkorn.
Tabbatacce al’ummai suna kama da ɗigon ruwa a cikin bokiti an ɗauke su a matsayin ƙura a kan magwaji; yakan auna tsibirai sai ka ce ƙura mai laushi.
16 Libanons skog vore icke nog till offerved och dess djur icke nog till brännoffer.
Itatuwan Lebanon ba su isa a yi wutar bagade da su ba, balle dabbobinsa su isa yin hadayun ƙonawa.
17 Folken äro allasammans såsom ett intet inför honom; såsom alls intet och idel tomhet aktas de av honom.
A gabansa dukan al’ummai ba kome ba ne; ya ɗauke su ba a bakin kome ba kuma banza ne kurum.
18 Vid vem viljen I då likna Gud, och vad finnes honom likt att ställa vid hans sida?
To, ga wane ne za ka kwatanta Allah? Wace siffa za ka kwatanta shi da ita?
19 Månne ett avgudabeläte? -- det gjutes av någon konstnär, och guldsmeden överdrager det sedan med guld, och med silverkedjor pryder så guldsmeden det.
Gunki dai, maƙeri kan yi zubinsa, maƙerin zinariya kuma yă ƙera shi da zinariya yă kuma sarrafa masa sarƙoƙin azurfa.
20 Den som icke har råd att offra så mycket, han väljer ut ett stycke trä, som icke ruttnar, och söker sig en förfaren konstnär, som kan förfärdiga ett beläte, som ej faller omkull.
Mutumin da talauci ya sha kansa da ba zai iya miƙa irin hadayar nan ba kan zaɓi itacen da ba zai ruɓe ba. Yakan nemi gwanin sassaƙa don yă sassaƙa masa gunkin da ba zai fāɗi ba.
21 Haven I då intet förstånd? Hören I då intet? Blev detta icke förkunnat för eder från begynnelsen? Haven I icke förstått, vad jordens grundvalar säga?
Ba ku sani ba? Ba ku taɓa ji ba? Ba a faɗa muku daga farko ba? Ba ku fahimta ba tun kafawar duniya?
22 Han är den som tronar över jordens rund, och dess inbyggare äro såsom gräshoppor; han är den som utbreder himmelen såsom ett flor och spänner ut den såsom ett tält att bo inunder.
Yana zaune a kursiyi a bisa iyakar duniya, kuma mutanenta suna kama da fāra. Ya miƙa sammai kamar rumfa, ya kuma shimfiɗa su kamar tentin da za a zauna a ciki.
23 Han är den som gör furstarna till intet, förvandlar domarna på jorden till idel tomhet.
Yakan mai da sarakuna ba kome ba yă mai da masu mulkin wannan duniya wofi.
24 Knappt äro de planterade, knappt äro de sådda, knappt har deras stam slagit rot i jorden, så blåser han på dem, och de förtorka, och en stormvind för dem bort såsom strå.
Ba da jimawa ba bayan an shuka su, ba da jimawa ba bayan an dasa su, ba da jimawa ba bayan sun yi saiwa a ƙasa, sai yă hura musu iska su yanƙwane, guguwa kuma ta kwashe su kamar yayi.
25 Vid vem viljen I då likna mig, så att jag skulle vara såsom han? säger den Helige.
“Ga wa za ku kwatanta ni? Ko kuwa wa yake daidai da ni?” In ji Mai Tsarkin nan.
26 Lyften upp edra ögon mot höjden och sen: vem har skapat allt detta? Det har han som för härskaran däruppe fram i räknade hopar; han nämner dem alla vid namn. Så stor är hans makt, så väldig hans kraft, att icke en enda utebliver.
Ku ɗaga idanunku ku duba sammai. Wane ne ya halicce dukan waɗannan? Wane ne ya fitar da rundunar taurari ɗaya-ɗaya, yana kiransu, kowanne da sunansa. Saboda ikonsa mai girma da kuma ƙarfinsa mai girma, babu ko ɗayansu da ya ɓace.
27 Huru kan du säga sådant, du Jakob, och tala så, du Israel: »Min väg är fördold för HERREN, och min rätt är försvunnen för min Gud»?
Ya Yaƙub, ya Isra’ila, me ya sa kake ce kana kuma gunaguni cewa, “Hanyata tana a ɓoye daga Ubangiji; Allah bai kula da abin da yake damuna ba”?
28 Vet du då icke, har du ej hört det, att HERREN är en evig Gud, han som har skapat jordens ändar? Han bliver ej trött och uppgives icke, hans förstånd är outrannsakligt.
Ba ku sani ba? Ba ku ji ba? Ubangiji madawwamin Allah ne, Mahaliccin iyakokin duniya. Ba zai taɓa gaji ko yă kasala ba, kuma fahimtarsa ya wuce gaban ganewar mutum.
29 Han giver den trötte kraft och förökar den maktlöses styrka.
Yakan ba da ƙarfi ga waɗanda suka gaji yă kuma ƙara ƙarfi ga marasa ƙarfi.
30 Ynglingar kunna bliva trötta och uppgivas, och unga män kunna falla;
Ko matasa ma kan gaji su kuma kasala, samari kuma kan yi tuntuɓe su fāɗi;
31 men de som bida efter HERREN hämta ny kraft, de få nya vingfjädrar såsom örnarna. Så hasta de åstad utan att uppgivas, de färdas framåt utan att bliva trötta.
amma waɗanda suka dogara ga Ubangiji za su sabunta ƙarfinsu. Za su yi firiya da fikafikai kamar gaggafa; za su kuma yi gudu ba kuwa za su gaji ba, za su yi tafiya ba kuwa za su kasala ba.