< Jesaja 13 >

1 Detta är en utsaga om Babel, vad som uppenbarades för Jesaja, Amos' son.
Abubuwan da Allah ya yi magana a kai game da Babilon da Ishaya ɗan Amoz ya gani.
2 Resen upp ett baner på ett kalt berg, ropen högt till dem; viften med handen att de må draga in genom de mäktiges portar.
A tā da tuta a kan tudun da yake mai fili, ka tā da murya gare su; ka ɗaga hannu ka ba su alama don su shiga ƙofofi masu alfarma.
3 Jag själv har bådat upp mina invigda, ja, kallat mina hjältar till mitt vredesverk, min stolta skara, som jublar.
Na umarci tsarkakana; na umarci jarumawan yaƙina su gamsar da fushina, waɗanda suke farin ciki a nasarata.
4 Hör, det larmar på bergen såsom av ett stort folk. Hör, det sorlar av riken med hopade hednafolk. HERREN Sebaot mönstrar sin krigarskara.
Ka saurara, akwai surutu a kan duwatsu, sai ka ce na babban taron jama’a! Ka saurara, akwai hayaniya a cikin mulkoki, sai ka ce al’ummai ne suna ta tattaruwa! Ubangiji Maɗaukaki yana shirya mayaƙa don yaƙi.
5 Ifrån fjärran land komma de, ifrån himmelens ända, HERREN och hans vredes redskap, för att fördärva hela jorden.
Suna zuwa daga ƙasashe masu nesa, daga iyakokin duniya, Ubangiji da kuma fushinsa, zai hallaka dukan ƙasar.
6 Jämren eder, ty nära är HERRENS dag; såsom våld från den Allsvåldige kommer den.
Ku yi ihu, gama ranar Ubangiji ta yi kusa za tă zo kamar hallaka daga Maɗaukaki.
7 Därför sjunka alla händer ned, och alla människohjärtan förfäras.
Saboda wannan, hannun kowane mutum zai yi rauni, ƙarfin halin kowane mutum zai kāsa.
8 Man förskräckes, man gripes av ångest och kval, ja, våndas såsom en barnaföderska. Häpen stirrar den ene på den andre; röda såsom eldslågor äro deras ansikten.
Tsoro zai kama su, zafi da azaba za su ci ƙarfinsu; za su yi ta murɗewa kamar mace mai naƙuda. Za su dubi juna a tsorace, fuskokinsu a ɓace.
9 Se, HERRENS dag kommer, gruvlig och med förgrymmelse och med vredesglöd, för att göra jorden till en ödemark och utrota syndarna som där bo.
Duba, ranar Ubangiji tana zuwa, muguwar rana, mai hasala da zafin fushi, don ta mai da ƙasar kango ta kuma hallakar da masu zunubi da suke cikinta.
10 Ty himmelens stjärnor och stjärnbilder sända ej mer ut sitt ljus, solen går mörk upp, och månens ljus skiner icke.
Taurarin sama da ƙungiyoyinsu ba za su ba da haskensu ba. Rana za tă yi duhu wata kuma ba zai ba da haskensa ba.
11 Jag skall hemsöka jordens krets för dess ondska och de ogudaktiga för deras missgärning; jag skall göra slut på de fräckas övermod och slå ned våldsverkarnas högmod.
Zan hukunta duniya saboda muguntarta, mugaye saboda zunubansu. Zan kawo ƙarshe ga girman kan masu taƙama in kuma ƙasƙantar da ɗaga kan marasa tausayi.
12 Jag skall göra en man mer sällsynt än fint guld, en människa mer sällsynt än guld från Ofir.
Zan sa mutum yă fi zinariya zalla wuyar samuwa, fiye da zinariyar Ofir wuyan gani.
13 Därför skall jag komma himmelen att darra, och jorden skall bäva och vika från sin plats -- genom HERREN Sebaots förgrymmelse, på hans glödande vredes dag.
Saboda haka zan sa sammai su yi rawar jiki; duniya kuma za tă girgiza daga inda take a fushin Ubangiji Maɗaukaki, a ranar fushinsa mai ƙuna.
14 Och likasom jagade gaseller och en hjord som ingen samlar vända de då hem, var och en till sitt folk, och fly, var och en till sitt land.
Kamar barewar da ake farautarta kamar tumaki marasa makiyayi, haka nan kowane mutum zai koma ga mutanensa, kowane mutum zai gudu zuwa ƙasarsa.
15 Men envar som upphinnes bliver genomborrad, och envar som gripes faller för svärd.
Duk wanda aka kama za a soke shi yă mutu; dukan waɗanda aka kama za su mutu ta takobi.
16 Deras späda barn krossas inför deras ögon, deras hus plundras, och deras kvinnor skändas.
Za a fyaɗa’ya’yansu a ƙasa su yi kucu-kucu a idanunsu; za a washe gidajensu, a kuma kwana da matansu.
17 Ty se, jag vill uppväcka mot dem mederna, som akta silver för intet och icke fråga efter guld.
Duba, zan zuga mutanen Medes su yi gāba da su, su da ba su kula da azurfa ba kuma ba sa damuwa da zinariya.
18 Deras bågar skola fälla de unga männen, med frukten i moderlivet hava de intet förbarmande, och barnen skona de icke.
Bakkunansu za su kashe samari; ba za su ji tausayin jarirai ba ba za su kuwa nuna jinƙai ga’yan yara ba.
19 Och det skall gå med Babel, rikenas krona, kaldéernas ära och stolthet, likasom när Gud omstörtade Sodom och Gomorra.
Babilon, kayan daraja na mulkoki, abin fariyar Babiloniyawa, Allah zai kaɓantar da ita kamar yadda ya yi da Sodom da Gomorra.
20 Aldrig mer skall det bliva bebyggt, från släkte till släkte skall det ligga obebott; ingen arab skall där slå upp sitt tält, ingen herde lägra sig där med sin hjord.
Ba za ƙara kasance da mazauna kuma ba ko a yi zama a cikinta dukan zamanai; Ba wani mutumin Arab da zai kafa tentinsa a can, ba makiyayin da zai taɓa kiwon garkensa a can.
21 Nej, öknens djur skola lägra sig där, och dess hus skola fyllas av uvar; strutsar skola bo där, och gastar skola hoppa där.
Amma halittun hamada za su kwanta a can, diloli za su cika gidajenta; a can mujiyoyi za su zauna, a can kuma awakin jeji za su yi ta tsalle.
22 Schakaler skola tjuta i dess palatser och ökenhundar i praktbyggnaderna. Snart kommer dess tid; dess dagar skola ej fördröjas.
Kuraye za su yi ta kuka a kagarorinta, diloli kuma a cikin fadodinta masu alfarma. Lokacinta ya yi kusa, kwanakinta kuma ba za su yi tsawo ba.

< Jesaja 13 >