< Habackuk 3 >

1 En bön av profeten Habackuk; till Sigjonót.
Addu’ar annabi Habakkuk. A kan shigiyont.
2 HERRE, jag har hört om dig och häpnat. HERRE, förnya i dessa år dina gärningar, låt oss förnimma dem i dessa år. Mitt i din vrede må du tänka på förbarmande.
Ya Ubangiji, na ji irin shaharar da ka yi; na yi al’ajabi game da ayyukanka, ya Ubangiji. Ka maimaita su a kwanakinmu, ka sanar da su a lokacinmu; ka yi jinƙai ko a lokacin da kake fushi.
3 Gud kommer från Teman, den helige från berget Paran. (Sela) Hans majestät övertäcker himmelen, och av hans lov är jorden full.
Allah ya zo daga Teman, Mai Tsarkin nan daga Dutsen Faran. (Sela) Ɗaukakarsa ta rufe sammai yabonsa kuma ya cika duniya.
4 Då uppstår en glans såsom av solljus, strålar gå ut ifrån honom, och han höljer i dem sin makt.
Darajarsa ta yi kamar fitowar rana; ƙyalƙyali ya wulga daga hannunsa, inda ikonsa yake a ɓoye.
5 Framför honom går pest, och feberglöd följer i hans spår.
Annoba ta sha gabansa; cuta kuma tana bin bayansa.
6 Han träder fram -- därmed kommer han jorden att darra; en blick -- och han kommer folken att bäva. De uråldriga bergen splittras, de eviga höjderna sjunka ned. Han vandrar de vägar han fordom gick.
Ya tsaya, ya kuwa girgiza duniya; ya duba, sai ya sa al’ummai suka yi rawan jiki. Tsofaffin duwatsu sun wargaje daɗaɗɗun tuddai kuma suka rurrushe. Hanyoyinsa dawwammamu ne.
7 Jag ser Kusans hyddor hemsökta av fördärv; tälten darra i Midjans land.
Na ga tentin Kushan cikin azaba; wuraren zaman Midiyan cikin damuwa.
8 Harmas då HERREN på strömmar? Ja, är din vrede upptänd mot strömmarna eller din förgrymmelse mot havet, eftersom du så färdas fram med dina hästar, med dina segerrika vagnar?
Ka ji haushin koguna ne, ya Ubangiji? Ko kuwa ka hasala da rafuffuka ne? Ko ka yi fushi da teku ne sa’ad da ka hau dawakanka da kuma kekunan yaƙinka masu nasara?
9 Framtagen och blottad är din båge, ditt besvurna ords pilar. (Sela) Till strömfåror klyver du jorden.
Ka ja bakanka, ka nemi a ba ka kibiyoyi masu yawa. (Sela) Ka raba duniya da koguna;
10 Bergen se dig och bäva; såsom en störtskur far vattnet ned. Djupet låter höra sin röst, mot höjden lyfter det sina händer.
duwatsu sun gan ka sai suka ƙame. Ruwaye masu hauka sun yi ta fantsamawa; zurfafa suka yi ruri suka tā da raƙuman ruwansu sama.
11 Sol och måne stanna i sin boning för skenet av dina farande pilar, för glansen av ditt blixtrande spjut.
Rana da wata suka tsaya cik a sammai da ganin kibiyoyinka masu wucewa fyu, da ganin hasken māshinka mai walƙiya.
12 I förgrymmelse går du fram över jorden, i vrede tröskar du sönder folken.
Cikin hasala ka ratsa duniya cikin fushi kuma ka tattake ƙasashe.
13 Du drager ut för att frälsa ditt folk, för att bereda frälsning åt din smorde. Du krossar taket på de ogudaktigas hus, du bryter ned huset, från grunden till tinnarna. (Sela)
Ka fito don ka fanshi mutanenka, don ceci shafaffenka. Ka ragargaza shugaban ƙasar mugaye, ka tuɓe shi daga kai har ƙafa. (Sela)
14 Du genomborrar deras styresmans huvud med hans egna pilar, när de storma fram till att förskingra oss, under fröjd, såsom gällde det att i lönndom äta upp en betryckt.
Da māshinsa ka soki kansa sa’ad da jarumawansa suka fito don su tarwatse mu, suna farin ciki sai ka ce masu shirin cinye matalautan da suke a ɓoye.
15 Du far med dina hästar fram över havet, över de stora vattnens svall.
Ka tattake teku da dawakanka, kana kaɗa manyan ruwaye.
16 Jag hör det och darrar i mitt innersta, vid dånet skälva mina läppar; maktlöshet griper benen i min kropp, jag darrar på platsen där jag står. Ty jag måste ju stilla uthärda nödens tid, medan det kommer, som skall tränga folket.
Na ji sai zuciyata ta buga, leɓunana sun yi rawa da jin murya; ƙasusuwana suka ruɓe, ƙafafuna kuma sun yi rawa. Duk da haka zan jira da haƙuri ga ranar bala’i ta zo a kan al’umman nan mai kawo mana hari.
17 Ja, fikonträdet blomstrar icke mer, och vinträden giva ingen skörd, olivträdets frukt slår fel och fälten alstra ingen äring, fåren ryckas bort ur fållorna, och inga oxar finnas mer i stallen.
Ko da yake itace ɓaure bai tohu ba, ba kuma’ya’ya a kuringar inabi, ko da yake zaitun bai ba da amfani ba, gonaki kuma ba su ba da abinci ba, ko da yake babu tumaki a garke, ba kuma shanu a turaku,
18 Likväl vill jag glädja mig i HERREN och fröjda mig i min frälsnings Gud.
duk da haka zan yi farin ciki da Ubangiji, zan yi murna da Allah Mai Cetona.
19 HERREN, Herren är min starkhet; han gör mina fötter såsom hindens och låter mig gå fram över mina höjder. För sångmästaren, med mitt strängaspel.
Ubangiji Mai Iko Duka shi ne ƙarfina; yakan mai da ƙafafuna kamar na barewa, yakan sa in yi tafiya a wurare masu tsayi. Domin mai bi da kaɗe-kaɗe. A kan kayan kiɗi masu tsirkiyata.

< Habackuk 3 >