< 1 Mosebok 38 >
1 Vid den tiden begav sig Juda åstad bort ifrån sina bröder och slöt sig till en man i Adullam, som hette Hira.
A wannan lokaci, Yahuda ya bar’yan’uwansa ya gangara don yă zauna da mutumin Adullam, mai suna Hira.
2 Där fick Juda se dottern till en kananeisk man som hette Sua, och han tog henne till sig och gick in till henne.
A can Yahuda ya sadu da’yar wani Bakan’ane, mai suna Shuwa. Ya aure ta, ya kuma kwana da ita;
3 Och hon blev havande och födde en son, och han fick namnet Er.
ta yi ciki, ta kuma haifi ɗa, wanda aka kira Er.
4 Åter blev hon havande och födde en son och gav honom namnet Onan.
Ta sāke yin ciki, ta haifi wani ɗa, ta kira shi Onan.
5 Och hon födde ännu en son, och åt denne gav hon namnet Sela; och när han föddes, var Juda i Kesib.
Ta kuma haifi wani ɗa har yanzu, aka kuwa ba shi suna Shela. A Kezib ne ta haife shi.
6 Och Juda tog åt Er, sin förstfödde, en hustru som hette Tamar.
Sai Yahuda ya auro wa Er mata, ɗansa na fari, sunanta Tamar.
7 Men Er, Judas förstfödde, misshagade HERREN; därför dödade HERREN honom.
Amma Er, ɗan farin Yahuda mugu ne a fuskar Ubangiji, saboda haka Ubangiji ya kashe shi.
8 Då sade Juda till Onan: »Gå in till din broders hustru, äkta henne i din broders ställe och skaffa avkomma åt din broder.»
Sa’an nan Yahuda ya ce wa Onan, “Ka kwana da matar ɗan’uwanka ka cika wajibinka gare ta a matsayin ɗan’uwan miji, don ka samar wa ɗan’uwanka’ya’ya.”
9 Men eftersom Onan visste att avkomman icke skulle bliva hans egen, lät han, när han gick in till sin broders hustru, det spillas på jorden, för att icke giva avkomma åt sin broder.
Amma Onan ya san cewa’ya’yan ba za su zama nasa ba; saboda haka a duk sa’ad da ya kwana da matar ɗan’uwansa, sai yă zub da maniyyinsa a ƙasa don kada yă samar wa ɗan’uwansa’ya’ya.
10 Men det misshagade HERREN att han gjorde så; därför dödade han också honom.
Abin nan da ya yi mugunta ce a gaban Ubangiji, saboda haka Ubangiji ya kashe shi, shi ma.
11 Då sade Juda till sin sonhustru Tamar: »Stanna såsom änka i din faders hus, till dess min son Sela bliver fullvuxen.» Han fruktade nämligen att annars också denne skulle dö, likasom hans bröder. Så gick Tamar bort och stannade i sin faders hus.
Sai Yahuda ya ce wa surukarsa Tamar, “Ki yi zama kamar gwauruwa a gidan mahaifinki sai ɗana Shela ya yi girma.” Gama ya yi tunani, “Shi ma zai mutu, kamar’yan’uwansa.” Saboda haka Tamar ta je ta zauna a gidan mahaifinta.
12 En lång tid därefter dog Suas dotter, Judas hustru. Och efter sorgetidens slut gick Juda med sin vän adullamiten Hira upp till Timna, för att se efter dem som klippte hans får.
Bayan an daɗe sai matar Yahuda,’yar Shuwa ta rasu. Sa’ad da Yahuda ya gama makoki, sai ya haura zuwa Timna, zuwa wurin mutanen da suke askin tumakinsa, abokinsa Hira mutumin Adullam kuwa ya tafi tare da shi.
13 När man nu berättade för Tamar att hennes svärfader gick upp till Timna för att klippa sina får,
Sa’ad da aka faɗa wa Tamar cewa, “Surukinki yana kan hanyarsa zuwa Timna don askin tumakinsa,”
14 lade hon av sig sina änkekläder och betäckte sig med en slöja och höljde in sig och satte sig vid porten till Enaim på vägen till Timna. Ty hon såg, att fastän Sela var fullvuxen, blev hon likväl icke given åt honom till hustru.
sai ta tuɓe rigunan gwaurancinta ta rufe kanta da lulluɓi don ta ɓad da kamanninta, sa’an nan ta je ta zauna a ƙofar shigar Enayim, wadda take a hanyar zuwa Timna. Gama ta lura cewa ko da yake Shela yanzu ya yi girma, ba a ba da ita gare shi ta zama matarsa ba.
15 Då nu Juda fick se henne, trodde han att hon var en sköka; hon hade ju nämligen sitt ansikte betäckt.
Sa’ad da Yahuda ya gan ta, ya yi tsammani karuwa ce, gama ta lulluɓe fuskarta.
16 Och han vek av till henne, där hon satt vid vägen, och sade: »Kom, låt mig gå in till dig.» Ty han visste icke att det var hans sonhustru. Hon svarade: »Vad vill du giva mig för att få gå in till mig?»
Bai san cewa ita surukarsa ce ba, sai ya ratse zuwa wurinta a gefen hanya ya ce, “Zo mana, in kwana da ke.” Sai ta ce, “Me za ka ba ni in na kwana da kai?”
17 Han sade: »Jag vill sända dig en killing ur min hjord.» Hon svarade: »Ja, om du giver mig pant, till dess du sänder den.»
Ya ce, “Zan aika miki da ɗan akuya daga garkena.” Sai ta ce, “Za ka ba ni wani abu jingina, kafin ka aika da shi?”
18 Han sade: »Vad skall jag då giva dig i pant?» Hon svarade: »Din signetring, din snodd och staven som du har i din hand.» Då gav han henne detta och gick in till henne, och hon blev havande genom honom.
Ya ce, “Wace jingina zan ba ki?” Sai ta amsa, “Hatiminka da ka rataye a wuya da kuma sandan da yake a hannunka.” Ya ba da su gare ta, ya kuma kwana da ita, sai ta yi ciki.
19 Och hon stod upp och gick därifrån och lade av sin slöja och klädde sig åter i sina änkekläder.
Bayan ta tafi, sai ta tuɓe lulluɓin, ta sāke sa tufafin gwaurancinta.
20 Och Juda sände killingen med sin vän adullamiten, för att få igen panten av kvinnan; men denne fann henne icke.
Ana cikin haka sai Yahuda ya aika da ɗan akuya ta hannun abokinsa mutumin Adullam don yă karɓo masa jinginar daga wurin macen, amma bai same ta a can ba.
21 Och han frågade folket där på orten och sade: »Var är tempeltärnan, hon som satt i Enaim vid vägen?» De svarade: »Här har ingen tempeltärna varit.»
Ya tambayi mutanen da suke zama a can ya ce, “Ina karuwar haikalin da take a bakin hanya a Enayim?” Sai suka ce, “Ba a taɓa kasance da karuwar haikali a nan ba.”
22 Och han kom tillbaka till Juda och sade: »Jag har icke funnit henne; därtill säger folket på orten att ingen tempeltärna har varit där.»
Saboda haka sai ya koma zuwa wurin Yahuda ya ce, “Ban same ta ba. Ban da haka ma, mutanen da suke zama a can, sun ce, ‘Ba a taɓa kasance da wata karuwar haikali a nan ba.’”
23 Då sade Juda: »Må hon då behålla det, så att vi icke draga smälek över oss. Jag har nu sänt killingen, men du har icke funnit henne.»
Sa’an nan Yahuda ya ce, “Bari tă riƙe kayan kiɗa garin nema mu zama abin dariya. Ni kam, na aika da tunkiyar amma ba a same ta ba.”
24 Vid pass tre månader därefter blev så berättat för Juda: »Din sonhustru Tamar har bedrivit otukt, och i otukt har hon blivit havande.» Juda sade: »Fören ut henne till att brännas.»
Bayan misalin wata uku sai aka faɗa wa Yahuda cewa, “Tamar, surukarka ta yi laifin karuwanci, a sakamakon haka yanzu ta yi ciki.” Yahuda ya ce, “A fid da ita, a ƙone!”
25 Men när hon fördes ut, sände hon bud till sin svärfader och lät säga: »Genom en man som är ägare till detta har jag blivit havande.» Och hon lät säga: »Se efter, vem denna signetring, dessa snodder och denna stav tillhöra.»
Yayinda ake fitar da ita, sai ta aika saƙo zuwa wurin surukinta, ta ce, “Mutumin da yake da waɗannan kayan ne ya yi mini ciki.” Ta kuma ƙara da cewa, “Duba ko za ka gane da hatimin nan, da abin ɗamaran nan, da kuma sandan nan, ko na wane ne?”
26 Och Juda kände igen dem och sade: »Hon är i sin rätt mot mig, eftersom jag icke har givit henne åt min son Sela.» Men han kom icke mer vid henne.
Yahuda ya gane su, sai ya ce, “Ai, ta fi ni gaskiya, da yake ban ba da ita ga ɗana Shela ba.” Bai kuwa ƙara kwana da ita ba.
27 När hon nu skulle föda, se, då funnos tvillingar i hennes liv.
Sa’ad da lokaci ya yi da za tă haihu, ashe, tagwaye’yan maza ne suke cikinta.
28 Och i födslostunden stack den ene fram en hand; då tog hjälpkvinnan en röd tråd och band den om hans hand och sade: »Denne kom först fram.»
Yayinda take haihuwa, ɗaya daga cikinsu ya fid da hannunsa; sai ungonzomar ta ɗauki jan zare ta ɗaura a hannun, ta ce, “Wannan ne ya fito da farko.”
29 Men när han därefter åter drog sin hand tillbaka, se, då kom hans broder fram; och hon sade: »Varför har du trängt dig fram?» Och han fick namnet Peres.
Amma sa’ad da ya janye hannunsa, sai ɗan’uwansa ya fito, sai ta ce, “Wato, haka ne ka keta ka fito!” Sai aka ba shi suna Ferez.
30 Därefter kom hans broder fram, han som hade den röda tråden om sin hand, och han fick namnet Sera. D. ä. framträngande.
Sa’an nan ɗan’uwansa wanda yake da jan zare a hannunsa ya fito, aka kuma ba shi suna Zera.