< Amos 3 >
1 Hören följande ord, som HERREN har talat mot eder, I Israels barn, ja, mot hela det släkte som jag har fört upp ur Egyptens land. Så har han sagt:
Ku ji wannan maganar da Ubangiji ya yi game da ku, ya ku jama’ar Isra’ila, a kan dukan iyalin da na fitar daga Masar.
2 Eder allena har jag utvalt bland alla släkter på jorden; därför skall jag ock hemsöka på eder alla edra missgärningar.
“Ku ne kaɗai na zaɓa cikin dukan al’umman duniya; saboda haka zan hukunta ku saboda dukan zunubanku.”
3 Färdas väl två tillsammans, utan att de hava blivit ense därom?
Mutum biyu za su iya yin tafiya tare in ba su yarda su yi haka ba?
4 Ryter ett lejon i skogen, om det ej har funnit något rov? Upphäver ett ungt lejon sin röst i kulan, utan att det har tagit ett byte?
Zaki yakan yi ruri a jeji in bai sami kama nama ba? Zai yi gurnani a cikin kogonsa in bai kama kome ba?
5 Faller en fågel i snaran på marken, om intet garn har blivit utlagt för den? Springer snaran upp från marken, utom när den gör någon fångst?
Tsuntsu yakan fāɗa a tarko a ƙasa inda ba a sa tarko ba, ko tarko yakan zargu daga ƙasa in ba abin da ya taɓa shi?
6 Eller stöter man i basun i en stad, utan att folket förskräckes? Eller drabbas en stad av något ont, utan att HERREN har skickat det?
Idan aka busa ƙaho a ciki birni mutane ba sa yin rawar jiki? Sa’ad da bala’i ya auko wa birni, ba Ubangiji ne ya sa a kawo shi ba?
7 Sannerligen, Herren, HERREN gör alls intet utan att hava uppenbarat sitt råd för sina tjänare profeterna.
Ba shakka, Ubangiji Mai Iko Duka ba ya yin wani abu ba tare da ya sanar wa bayinsa annabawa ba.
8 När lejonet ryter, vem skulle då icke frukta? När Herren, HERREN talar, vem skulle då icke profetera?
Zaki ya yi ruri, wa ba zai tsorata ba? Ubangiji Mai Iko Duka ya yi magana, wa ba zai yi annabci ba?
9 Ropen ut över Asdods palatser och över palatsen i Egyptens land; sägen: Församlen eder till Samarias berg, och sen huru stor förvirring där råder, och huru man övar förtryck därinne.
Ku yi shela ga kagarun Ashdod da kuma ga kagarun Masar. “Ku tara kanku a tuddan Samariya; ku ga rashin jituwar da take a cikinta, da kuma zaluncin da ake yi a cikin mutanenta.”
10 Man förstår icke där att göra vad rätt är, säger HERREN; man hopar våld och fördärv i sina palats.
“Ba su ma san yadda za su yi abin da yake daidai ba,” in ji Ubangiji, “sun ɓoye ganima da abubuwan da suka washe a cikin kagarunsu.”
11 Därför säger Herren, HERREN så: Trångmål skall komma och omvärva landet, ditt starka fäste skall du mista, det skall störtas ned; och dina palats skola varda utplundrade.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Abokin gāba zai ƙwace ƙasar, zai saukar da mafakarku, zai washe kagarunku.”
12 Så säger HERREN: Likasom när en herde ur lejonets gap räddar allenast ett par benpipor eller snibben av ett öra, så skola Israels barn bliva räddade, desamma som nu i Samaria sitta i sina soffors hörn och på sina bäddars sidendamast.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Kamar yadda makiyayi yakan ceci daga bakin zaki ƙasusuwa ƙafafu biyu kawai ko kunne ɗaya, haka za a ceci Isra’ilawa, masu zama a Samariya da kan gado kawai da kuma a ɗan ƙyalle a kan dogayen kujerunsu.”
13 Hören och betygen inför Jakobs hus, säger Herren, HERREN, härskarornas Gud:
“Ku ji wannan ku kuma yi wa gidan Yaƙub gargaɗi,” in ji Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki.
14 Den dag då jag på Israel hemsöker dess överträdelser, då skall jag ock hemsöka Betels altaren, så att altarhornen bliva avhuggna och falla till jorden.
“A ranar da zan hukunta Isra’ila saboda zunubanta, zan hallaka bagadan Betel; za a yayyanka ƙahonin bagadan za su fāɗa ƙasa
15 Och jag skall slå ned både vinterhus och sommarhus, och elfenbenshusen skola bliva förstörda, ja, en myckenhet av hus skall då få en ände, säger HERREN.
Zan rushe gidan rani da na damina; gidajen da aka yi musu ado da hauren giwa za a rushe su haka ma duk za a rurrushe manyan gidaje,” in ji Ubangiji.