< 1 Samuelsboken 23 >
1 Och man berättade för David: »Filistéerna hålla nu på att belägra Kegila, och de plundra logarna.»
Sa’ad da aka ce wa Dawuda, “Duba ga Filistiyawa suna yaƙi da mutanen Keyila, suna kwashe musu hatsi a masussukai.”
2 Då frågade David HERREN: »Skall jag draga åstad och slå dessa filistéer?» HERREN svarade David: »Drag åstad och slå filistéerna och fräls Kegila.»
Sai Dawuda ya nemi nufin Ubangiji, ya ce, “In tafi in fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi?” Ubangiji kuwa ya ce masa, “Jeka ka yi yaƙi da Filistiyawa, ka ceci Keyila.”
3 Men Davids män sade till honom: »Vi leva ju i fruktan redan här i Juda. Och nu skulla vi därtill draga åstad till Kegila, mot filistéernas här!»
Amma mutanen Dawuda suka ce masa, “Ga shi, a nan ma a Yahuda muna jin tsoro, balle mu tafi Keyila mu yi yaƙi da sojojin Filistiyawa!”
4 Då frågade David HERREN ännu en gång, och HERREN svarade honom och sade: »Stå upp och drag ned till Kegila; ty jag vill giva filistéerna i din hand.»
Dawuda ya sāke nemi nufin Ubangiji, sai Ubangiji ya ce masa, “Tashi ka gangara zuwa Keyila, gama zan ba da Filistiyawa a hannunka.”
5 Då drog David med sina män till Kegila och stridde mot filistéerna och förde bort deras boskap och tillfogade dem ett stort nederlag. Så frälste David invånarna i Kegila.
Sa’an nan Dawuda da mutanensa suka tafi Keyila, suka yi yaƙi da Filistiyawa, suka kwashe musu shanunsu, suka jijji wa Filistiyawa ƙwarai, suka cece mutanen Keyila daga hannunsu.
6 När Ebjatar, Ahimeleks son, flydde till David i Kegila, förde han efoden med sig ditned.
(Abiyatar ɗan Ahimelek ya zo da efod sa’ad da ya gudo zuwa wurin Dawuda a Keyila.)
7 Och det blev berättat för Saul att David hade dragit in i Kegila. Då sade Saul: »Gud har förkastat honom och givit honom i min hand, ty han har själv stängt in sig genom att gå in i en stad med portar och bommar.»
Shawulu ya sami labari cewa Dawuda ya tafi Keyila, sai ya ce, “Allah ya bashe shi a hannuna, domin Dawuda ya kulle kansa ke nan da ya shiga birnin da yake da ƙofofin da ake kulle da ƙarafa.”
8 Därefter bådade Saul upp allt folket till strid, för att draga ned till Kegila och där innesluta David och hans man.
Shawulu ya kira dukan sojojinsa don yaƙi, su gangaro zuwa Keyila su mamaye Dawuda da mutanensa.
9 Men när David fick veta att Saul stämplade ont mot honom, sade han till prästen Ebjatar: »Bär hit efoden.»
Da Dawuda ya ji labari Shawulu yana shirya hanyar da zai kashe shi, sai ya ce wa Abiyatar firist, “Kawo mini efod a nan.”
10 Och David sade: »HERRE, Israels Gud, din tjänare har hört att Saul har i sinnet att komma mot Kegila och fördärva staden för min skull.
Dawuda ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bawanka ya sami labari cewa tabbatacce Shawulu yana shirin zuwa Keyila yă hallaka garin saboda ni.
11 Skola Kegilas borgare då utlämna mig åt honom? Skall Saul komma hitned, såsom din tjänare har hört? HERRE, Israels Gud, förkunna det för din tjänare.» HERREN svarade: »Han skall komma hitned.»
Mutanen Keyila za su bashe ni a gare shi? Shawulu zai gangaro nan kamar yadda bawanka ya sami labari? Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, ka gaya wa bawanka.” Ubangiji ya ce, “Zai zo.”
12 David frågade ytterligare: »Skola Kegilas borgare då utlämna mig och mina man åt Saul?» HERREN svarade: »De skola utlämna eder.»
Dawuda ya sāke cewa, “Mutanen Keyila za su bashe ni da mutanena ga Shawulu?” Ubangiji ya ce, “Za su yi.”
13 Då bröt David upp med sitt folk, som utgjorde vid pass sex hundra man, och de drogo ut från Kegila och vandrade vart de kunde. När det då blev berättat för Saul att David hade flytt undan från Kegila avstod han från att draga ut.
Saboda haka Dawuda da mutanensa wajen mutum ɗari shida suka bar Keyila, suka yi ta tafiya daga wannan wuri zuwa wancan. Sa’ad da aka gaya wa Shawulu cewa Dawuda ya tsere daga Keyila, sai ya fasa tafiya can.
14 Så uppehöll sig nu David i öknen på bergfästena; han uppehöll sig bland bergen i öknen Sif. Och Saul sökte alltjämt efter honom, men Gud gav honom icke i hans hand.
Dawuda ya zauna a jeji cikin kogunan duwatsu da kuma tuddan jejin Zif. Kowace rana Shawulu ya yi ta neman Dawuda amma Allah bai bashe Dawuda a hannunsa ba.
15 Och medan David var i Hores i öknen Sif, förnam han att Saul hade dragit ut för att söka döda honom.
A lokacin da Dawuda yana zaune a Horesh cikin jejin Zif, ya sami labari cewa Shawulu ya fito don yă kashe shi.
16 Men Jonatan, Sauls son, stod upp och gick till David i Hores och styrkte hans mod i Gud.
Yonatan ɗan Shawulu kuwa ya tafi wurin Dawuda a Horesh, ya ƙarfafa shi yă dogara ga Allah.
17 Han sade till honom: »Frukta icke; ty min fader Sauls hand skall icke träffa dig, utan du skall bliva konung över Israel, och jag skall då hava andra platsen, näst efter dig. Detta vet ock min fader Saul.»
Ya ce, “Kada ka ji tsoro, mahaifina Shawulu ba zai taɓa sa hannu a kanka ba. Za ka zama sarki a Isra’ila, ni kuma in zama na biyu gare ka. Kai, ko mahaifina Shawulu ma ya san da haka.”
18 Sedan slöto de båda ett förbund inför HERREN. Och David stannade kvar i Hores, men Jonatan gick hem igen.
Su biyunsu kuwa suka ɗaura yarjejjeniya a gaban Ubangiji. Sai Yonatan ya koma gida amma Dawuda ya zauna Horesh.
19 Men några sifiter drogo upp till Saul i Gibea och sade: »David håller sig nu gömd hos oss på bergfästena i Hores, på Hakilahöjden, som ligger söder om ödemarken.
Zifawa suka tafi wurin Shawulu a Gibeya suka ce masa, “Ashe, ba Dawuda ne yake ɓuya a cikinmu a kogwannin duwatsu a Horesh a bisan tudun Hakila, kudu da Yeshimon ba?
20 Så drag nu ditned, o konung, så snart det lyster dig att göra det. Vår sak bliver det då att utlämna honom åt konungen.»
Yanzu, ya sarki, ka gangaro, ka zo a duk lokacin da ka ga ya yi maka, ka zo mu kuma hakkinmu ne mu bashe shi a hannun sarki.”
21 Då sade Saul: »Varen välsignade av HERREN, därför att I haven velat spara mig bekymmer.
Shawulu ya ce, “Ubangiji ya yi muku albarka, gama kun damu da ni.
22 Men gån nu och skaffen eder ytterligare visshet, och tagen reda på och sen efter, på vilket ställe han nu vistas, och vem som har sett honom där; ty man har sagt mig att han är mycket listig.
Ku tafi ku ƙara shiri. Ku san inda yakan tafi, wane ne kuma ya gan shi a can. An gaya mini cewa shi mai wayo ne sosai.
23 Och sen efter och tagen reda på alla gömställen där han kan gömma sig; och kommen så igen till mig, när I haven fått visshet, så vill jag sedan gå med eder. Ty finnes han i landet, skall jag veta att söka upp honom, om jag än måste söka bland alla Juda ätter.»
Ku binciko duk wuraren da yakan ɓuya, sai ku dawo ku gaya mini tabbataccen labari. Sa’an nan zan tafi tare da ku in yana can. Zan nemi shi ko’ina cikin dukan kabilar Yahuda.”
24 Då stodo de upp och gingo till Sif före Saul. Men David och hans män voro i öknen Maon, på hedmarken, söder om ödemarken.
Sai suka tashi suka koma Zif, suka sha gaban Shawulu. Dawuda da mutanensa kuwa suna jejin Mawon cikin Araba, kudu da Yeshimon.
25 När nu Saul drog åstad med sina män för att söka efter David, om talade man det för denne, och han drog då ned till klippan och stannade så i öknen Maon. När Saul hörde detta, satte han efter David in i öknen Maon.
Shawulu da mutanensa suka tafi neman Dawuda. Da Dawuda ya ji labari, sai ya gangara cikin duwatsu ya zauna a cikin jejin Mawon. Sa’ad da Shawulu ya ji haka, sai ya tafi jejin Mawon yana fafaran Dawuda.
26 Och Saul gick på ena sidan om berget, och David med sina män på andra sidan. Men just som David var stadd på flykt för att komma undan Saul, under det att Saul och hans män sökte kringränna David och hans män för att taga dem till fånga
Shawulu yana tafiya a gefe ɗaya na dutsen, Dawuda da mutanensa kuma suna a wancan gefe, suna hanzari su ɓace wa Shawulu. Sa’ad da Shawulu da sojojinsa suka kusa cimma Dawuda da mutanensa don su kama su,
27 kom en budbärare till Saul och sade: »Skynda dig och kom, ty filistéerna hava fallit in i landet.»
sai wani manzo ya zo wurin Shawulu yana cewa, “Ka koma da sauri, Filistiyawa sun kawo wa ƙasar hari.”
28 Då upphörde Saul att förfölja David och drog mot filistéerna. Därav fick det stället namnet Sela-Hammalekot Betydelsen oviss; möjligen skiljeklippan.
Shawulu kuwa ya janye daga fafaran Dawuda, ya tafi yă ƙara da Filistiyawa. Dalilin ke nan da ake kiran wannan wuri Sela Hammalekot, wato, dutsen tserewa.
Dawuda kuwa ya haura daga can ya zauna a kogwannin duwatsun En Gedi.