< Psaltaren 78 >

1 En undervisning Assaphs. Hör, mitt folk, min lag; böjer edor öron till mins muns tal.
Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
2 Jag vill öppna min mun till ordspråk, och vill förtälja gamla hemligheter;
Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
3 De vi hört hafve och vetom, och våra fäder oss förtäljt hafva;
abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
4 Att vi det icke fördölja skulle deras barnom, som efter komma skulle; utan förkunna Herrans lof, och hans magt och under, som han gjort hafver.
Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
5 Han upprättade ett vittnesbörd i Jacob, och gaf en lag i Israel, den han våra fäder böd, till att lära deras barn;
Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
6 På det att efterkommanderna måtte det lära, och de barn, som ännu skulle födde varda; då de uppkommo, att de ock förkunnade det sinom barnom;
don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
7 Att de skulle sätta sitt hopp till Gud, och icke förgäta Guds verk, och hålla hans bud;
Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
8 Och icke varda, såsom deras fäder, en affällig och ohörsam art; hvilkom deras hjerta icke fast var, och deras ande höll sig icke troliga till Gud;
Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
9 Såsom Ephraims barn, som väpnade voro och förde bågan, föllo af i stridstidenom.
Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
10 De höllo icke Guds förbund, och ville icke vandra i hans lag;
ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
11 Och förgåto hans verk, och hans under, som han dem bevist hade.
Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
12 För deras fäder gjorde han under, i Egypti land, på den markene Zoan.
Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
13 Han åtskiljde hafvet, och lät dem gå derigenom, och satte vattnet såsom en mur.
Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
14 Han ledde dem om dagen med en molnsky, och om nattena med en klar eld.
Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
15 Han lät bergsklippona remna i öknene, och gaf dem dricka vatten tillfyllest;
Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
16 Och lät bäcker flyta utu bergsklippone, att de flöto derut, såsom vattuströmmar.
ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
17 Likväl syndade de ännu emot honom, och förtörnade den Högsta i öknene;
Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
18 Och försökte Gud, i deras hjerta, att de spis beddes till deras själar;
Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
19 Och talade emot Gud, och sade: Ja, skulle väl Gud kunna bereda ett bord i öknene?
Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
20 Si, han hafver väl slagit bergsklippona, att vatten utflöt, och bäcker sig utgåfvo; men huru kan han gifva bröd, och skaffa sino folke kött?
Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
21 Då nu Herren det hörde, vardt han upptänd; och eld gick upp i Jacob, och vrede kom öfver Israel;
Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
22 Att de icke trodde uppå Gud, och hoppades icke uppå hans hjelp.
gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
23 Och han böd skyarna ofvantill, och upplät himmelens dörrar;
Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
24 Och lät regna Man till dem till mats, och gaf dem himmelsbröd.
ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
25 De åto änglabröd; han sände dem mat tillfyllest.
Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
26 Han lät blåsa östanväder under himmelen, och genom sina starkhet upprörde sunnanväder;
Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
27 Och lät kött regna uppå dem såsom stoft, och foglar såsom sanden i hafvet;
Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
28 Och lät dem falla i deras lägre, allestäds der de bodde.
Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
29 Då åto de, och vordo för mätte; han lät dem släcka sin lusta.
Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
30 Då de ännu sin lusta icke släckt hade, och de ännu åto deraf,
Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
31 Så kom Guds vrede öfver dem; och drap de yppersta ibland dem, och nederslog de bästa i Israel.
fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
32 Men öfver allt detta syndade de ännu mer, och trodde intet uppå hans under.
Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
33 Derföre lät han dem dö bort, så att de intet fingo, och måste i deras lifsdagar plågade varda.
Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
34 När han drap dem, sökte de honom, och vände sig bittida till Gud;
A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
35 Och tänkte, att Gud är deras tröst, och Gud den Högste deras förlösare;
Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
36 Och skrymtade för honom med deras mun, och lögo för honom med deras tungo.
Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
37 Men deras hjerta var icke fast intill honom, och höllo sig icke troliga intill hans förbund.
zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
38 Men han var barmhertig, och förlät missgerningarna, och förgjorde dem icke; och afvände ofta sina vrede, och lät icke alla sina vrede gå.
Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
39 Ty han tänkte att de äro kött; ett väder, som bortfar, och kommer intet igen.
Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
40 De förtörnade honom ganska ofta i öknene, och bekymrade honom i ödemarkene.
Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
41 De försökte Gud framgent, och rette den Heliga i Israel.
Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
42 De tänkte intet uppå hans hand, den dagen då han förlöste dem ifrå fienderna;
Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
43 Såsom han sina tecken gjort hade uti Egypten, och sina under i det landet Zoan.
ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
44 Då han deras vatten i blod vände; så att de af deras bäcker icke dricka kunde.
Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
45 Då han ohyro ibland dem sände, som dem åto, och paddor, som dem förderfvade;
Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
46 Och gaf deras frukt gräsmatkom, och deras säd gräshoppom.
Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
47 Då han deras vinträ med hagel förderfvade, och deras mulbärsträ med stort hagel.
Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
48 Då han deras boskap slog med hagel, och deras hjordar med ljungande.
Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
49 Då han i sina grymma vrede sände ibland dem onda änglar, och lät dem härja och förderfva, och skada göra.
Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
50 Då han lät sina vrede gå, och icke skonade deras själom för dödenom, och lät deras boskap dö af pestilentie.
Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
51 Då han i Egypten allt förstfödt slog, de första arfvingar i Hams hyddom;
Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
52 Och lät sitt folk utdraga såsom får, och förde dem såsom en hjord i öknene.
Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
53 Och han ledde dem säkra, så att de intet fruktade sig; men deras fiendar öfvertäckte hafvet;
Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
54 Och lät dem komma i sina helga gränsor, till detta berg, hvilket hans högra hand förvärfvat hafver;
Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
55 Och fördref för dem folk, och lät dem utskifta arfvet, och lät Israels slägter bo i deras hyddom.
Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
56 Men de försökte och förtörnade Gud, den Högsta, och höllo intet hans vittnesbörd;
Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
57 Och föllo tillbaka, och föraktade all ting, såsom deras fäder; och höllo intet, såsom en lös båge;
Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
58 Och förtörnade honom med sina höjder, och rette honom med sina afgudar;
Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
59 Och då Gud det hörde, vardt han upptänd, och förkastade Israel svårliga;
Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
60 Så att han lät fara sina boning i Silo, den hyddo, der han ibland menniskor bodde;
Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
61 Och gaf deras magt uti fängelse, och deras härlighet uti fiendans händer;
Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
62 Och öfvergaf sitt folk för svärd, och var upptänd emot sitt arf.
Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
63 Deras unga män förtärde elden, och deras jungfrur måste ogifta blifva.
Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
64 Deras Prester föllo genom svärd, och inga enkor voro, de der gråta skulle.
aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
65 Och Herren vaknade upp, såsom en sofvande, och såsom en stark glad är, den ifrå vin kommer;
Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
66 Och slog sina fiendar baktill, och hängde en evig skam uppå dem;
Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
67 Och förkastade Josephs hyddo, och utvalde icke Ephraims slägte;
Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
68 Utan utvalde Juda slägte, det berget Zion, som han älskade;
amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
69 Och byggde sin helgedom högt, såsom ett land det evinnerliga fast stå skall;
Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
70 Och utvalde sin tjenare David, och tog honom utu fårahusen.
Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
71 Ifrå de däggande får hemtade han honom, att han hans folk Jacob föda skulle, och hans arf Israel.
daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
72 Och han födde dem också med all trohet, och regerade dem med all flit.
Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.

< Psaltaren 78 >